🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ Godiya🙏 Bismillahir Rahmanir Raheem Alhamdulillah Alhamdulillah Alhamdulillahi Rabbil Alamin. Godiya ta tabbata ga Ubangiji Mai Rahma mai jinƙai. Rabbish rahlee sodree wayassir lee Ameer, wahlul uqdatan min lisanee yafqahu qaulee. Masoyana mutanin aljanna, Allah dai ya bar mu tare. Banida abun faɗa sai dai nace Allah yabar min ku. Ina alfahari da ku sosai sosai🫰. Gargadi🧏 Wannan littafin nawane, Ni na zauna na tsara labarin a yadda raina yaga dama. Banga amfanin wata ko wani ya kasa zama shima yayi amfani da basirar da Allah yayi masa ba, saidai ya zabi ya zauna ya bata lokaci wurin editing littafin wani ya juyashi zuwa nashi. Duk wani ko wata wadda yayi ko tayi mun haka, sakamakonsa yana wurin Allah. Akiyaye Please. Tsarin labari✍️ Wannan littafin banyishi don cin zarafin kowa ba, kwata kwata ma ƙagaggen labari ne ba real life story bane. Don Allah duk wacce taga yayi kamada labarin da toh wannan kuma total coincidence ne, ina mai bada haquri. Labarine wadda ya ƙunshi tsananin jaddada, cin amana, mugunta,dogon buri, abubuwan ban mamaki da nishadi,zazzafan kauna da soyayya😌😌. Nice taku kullum Reemah, marubuciyar MIJIN TACE FARHAAN yanzu kuma RAYUWAR ANEESA.... # BETRAYAL # COMEDY # HOT LOVE # ROMANCE Happy Eid my loves❤️ PG 1_5 "Kan ubancan, ni yarinyar nan zata watsawa ruwan wanke wanke ajiki" Ni dai ina tsaye ko ƙala bance ba, nasan halin Abba sarai, karamin aikinsa ne ya rufeni da dukan tsiya. Cikin rawan murya nace "Abba kayi haquri, wlh bansan kana shigowa bane na watsa ruwa.." maganan danakeyi ne ya maƙale sakamakon wani irin gigitacciyar marin da Abbana ya sakar mun afuska har hakan yasa na zube akasa na kwala kaina da tukunyan tuwon Innati😂. Ko kallona Abba baiyi ba ya wuce cikin gidan abunsa yana zage zage. Da ƙyar na mike na zauna ina mulmula inda kaina ya bugu, abunka da mai arahan hawaye, take suka fara zubowa shaaa. Nidai na shiga uku, inda wani yau zai zo ya faɗamin cewa ba Abbana bane ya haifeni da wlh babu tantama zan yarda, jin kukana yasa Innati fitowa daga ɗan bayinmu dake tsakar gida wadda buhu kawai akasa aka ɗan rufe Kofar shiga, ganina datayi aƙasa caba caba cikin ruwan datti yasata isowa wurina da sauri tana kamani har na tashi akan kafata. Kamo hannuna tayi zuwa kan taburman dake malale a tsakar gida gaba daya ya fice hayyacinsa tsabar tsufa, zan iya cewa tunda aka haifeni har na taso naga wannan taburman da tsufanta, hala yana cikin kayan ɗakin Goggo (mahaifiyar Abba)😂. Cikin sheshsheka nace "Innati nidai Allah na gaji da abinda Abba yake yi mun, saikace ƴar bare bana cikinsa ba, abu kaɗan duka duk jikina babu inda bai bar tabo ba, kalli kigani fa"nafaɗa ina nuna mata duk inda nasan akwai wata alama ta duka da Abba ya bari ajikina. Tsabar tsoron da Abba ya dasawa Innati akansa ya hanata cewa uffam, tasan sarai yana jinta shi yasa bata iya cemun komai ba sai haquri datake bani, ni kuma harga Allah nagaji da wannan haƙurin, aiko sarauniyar haƙuri itama tanada maƙura. Fitowa Abba yayi daga ɗaki dukkanmu dagani har Innati mukaja bakinmu mukayi shiru bamu ce komai ba, watso min kayansa dana ɓata da ruwan datti yayi yayi wucewarsa, ko ba'a faɗa mun ba nasan meyake nufi, to da me zan wanke kayan na shiga uku Ni JAMMA, Ni kaina na mance yaushe nayi wanka da sabulu balle nasan ina zanyi kashinta na wanke wa Abba kaya dashi. Hawayen danake dannewa ne sukayi nasarar gangarowa, Innati babu abinda ke ƙaryata irin taga hawaye a idanuna,nice kawai mai bata ƙarfin guiwa, aduk lokacin da Abba yayiwa Innati duka, ni kaɗai takeda wadda ke iya rarrashinta. Dake saurin kuka nayi gadonsa ne daga wurin Innati, kasa bani haquri tayi itama kawai ta fashe da nata kukan tana rungume dani saman kirjinta. Sheshshekan kukanmu ne ya tasar da Goggo abaccinta. Fitinanniyar tsohuwa kenan, ko Abba albarka. Tun daga daƙi tafara sakin ashar tana zaginmu dagani har Innati. Jin haka yasa muka rarrashi kanmu mukayi shiru amma haka muka yini cikin ƙunan rai da rashin walwala kamar kullum. Washe gari da sassafe na farka nagama duk wata aiki dazanyi danna samu naje islamiyya, shima rashin zuwa alokaci ba ƙaramin hukunci ne atattare dashi ba. Dake nasan babu batun karin kumallo yasa kawai na shirya cikin koɗaddun kayan makaranta na na ɗau jakata wadda akayishi da buhu na zuba littatafai na na fito daga ɗan kwangon ɗakina. Innati kawai na samu a tsakar gida tana wanke kayan Goggo. Sallama nayi mata nasa kai zan fita naji Goggo tayi ihun sunana wadda babu mai kirana da shi sai ita wato "Bahaguwa" bafa wai donni din Bahaguwa bace, ita kaɗai tasan ma'anar wannan sunan. Cikin ɗaure fuska na juya ina addu'a azuciyata Allah yasa ba aiki tsohuwar nan zata sani ba. Aikuwa kamar ta karanta abinda ke raina naga ta dunƙulo mun wata uwar ashar harda daƙuwa. Allah ya sani, badon komai na dage da zuwa islamiyya ba sai don yaƙi da jahilci amma wannan tsohuwar da ɗanta wato Abba makiyana ne akan haka, saidai idan zan saci idonsu na fice a gida zuwa makaranta, Amma muddin suka ganni tofa saidai na fasa zuwa. Kallona Goggo tayi cikin halin ko in kula tace"dama dai kin huta da zuwa wannan makarantar amma nikam tausa zakiyi mun, na kwana da ciwon ƙafa" Allah ya kawo mun ƙarshen wannan tsohuwar, kamar na ƙwala ihu amma babu yadda na iya. Haka na zauna a ƙasa ta ɗora mun kafafunta wadda duk faso yagama cinye shi akan cinyata, inama ƙafan nada laushi dana ji dadin yin tausan amma gaba daya sai keta mun hannu yake. Wlh duk zanuwan gadon Goggo sun ɓaɓɓarke tsabar ƙaushin kafanta, Allah sarki ƙanwata Ameera, da tana nan kenan da itace zata yi daidai da Goggo, ba ƙaramin kwasa sukeyi da ita ba, har shakkar ta tsohuwar take idan tanaso tayi mata wani kulli kuma babu Abba a gida, amma muddin yana nan to sai inda ƙarfinta yaƙare. Wannan dalilin yasa Abba baiwa ƙaninsa Ameera amatsayin yar riko, saboda acewarsa tasa uwarsa agaba( to ya za'ayi bazata sa ta agaba ba, kaima ka takura wa uwarta🙄). Ina nan zaune ina abu ɗaya har kusan awa ɗaya sannan Goggo ta ciro nera dari biyu a gefen zaninta ta jefa min tace " Ke Bahaguwa, maza miƙe kije ki sayo mun ƙosai na koko awurin innan Ladi kafin ɗana yadawo, nasan ya fice da yunwa tunda ba wani abinci uwartaki ta dafa masa ba" Goggo taƙarashe magana tana zabgawa Innati uban harara, ganin idonta baya kaina yasa nima hararanta ƙasa ƙasa ina murguɗa mata baki, kai kaman karas, wai Innati ce bata dafawa ɗanta abinci ba saikace shi ɗannata ya kawo ne aka ƙi dafawa. Ƙwafa nayi ƙasa ƙasa na mike ina cunno karamin bakina gaba, sai wani disco cikina yake kamar anbude gidan kiɗa a cikinta tsabar yunwa. Inama inna kawo kosannan Goggo ta ɗeba mana kaɗan nida Innati na. Saida na shiga na canza kayan jikina zuwana aiki sannan na fito ina ƴar nasheed dina wadda malaminmu malam sabo yake yawan yi mana a islamiyya. Ina isowa na samu ana dambe, ankifarwa Innan Ladi kullun ƙosai gaba ɗaya aƙasa, saiga tsohuwa tasha ɗammara a tsukakken ƙugunta tana cewa lallai sai an biyata kuɗin kosanta😂😂, kasa riƙe dariya na nayi, aikuwa saida na dara. Kallon ikon Allah nake, wannan tsohuwa akwai ƙarfin hali, wadda fa ya kifar mata da kullunnan, naushi ɗaya idan yabata wlh saidai akaita gidanta na gaskiya tuyan ƙosai ya ƙare kenan😂. Nikam wannan batu ba ƙaramin daɗi yayi mun ba, wannan shine kamuwar Allah, nadai san babu wata mai tuyan ƙosai a wannan unguwar sai Innan Ladi, to kuma an kifar mata da kullu kenan yana nufin dagamu harsu Goggo da Abba zamu wuni cikin yunwa💃😂, dama nasan idan nakawo saidai su cinye su barmu da wanke musu kwanuka. Harda ƴar rawata na juya nayi hanyar gida ina waƙa, sai da nazo dab da gida na canza fuskata alamar damuwa, ina shiga na tadda Abba yana zaune shida Goggonsa suna hira, ko da nayi sallama Innati ce kawai ta amsa amma su Goggo sai kallon hannuna sukeyi suna jiran suga ledan ƙosansu. Ganin haka yasa naɗan kara ɓata fuskata na iso gabansu, cikin ladabi na tsuguna na gaida Abba, "ke Ni dallah bani abinda aka aikeki banason munafirci, gaisuwanki zanci dan ubanki"? Fadin Goggo, murmushi nayi araina na miƙa mata dunkulallen ɗari biyunta nace "Goggo babu ƙosai" Abba bai bari na gama explanation ba kawai ya kwaɗa mun Mari, cikin fushi Goggo ta ingiza shi ya ƙara mun, acewarta hala ma ban tafi wurin ƙosan ba tunda taga ban daɗe ba nadawo. Har rana dagamu harsu babu wadda yasa komai abakinsa, nida Innati sai ɗurawa cikinmu ruwa muke wai ko dan ya riƙe mana ciki, daga ƙarshe ma ƙulle mana ciki ruwan yayi. Goggo ta zauna tayita sakin tsaki ita kaɗai, shiko Abba ficewarsa yayi, yasan yadda zai yi dakansa. Yar karamar wayar ta ƙirar Nokia irin mai Black and white dinnan ta fidda tasani na kira mata layin Baba Auwalu ƙanin Abba wadda ƙanwata Ameera ke wurinsa. Cikin zumudi kuwa nayi dialling number din nasa kodan zan samu naji Muryar ƴar ƙanwata. Bugu biyu ya dauka na mikawa Goggo, ko sallama babu tace "Auwalu shikenan kai kuma babu waiwayon uwarka dan kana wani gari, tun jiya rabona da abinci amma kai na tabbata yanzu haka cikinka acike yake dam, kai ko kanason albarka kuwa" cikin tsananin damuwa wadda muryarsa ne ya nuna hakan Baba Auwalu yace "Goggo ki gafarceni, wlh muma ko karin kumallo bamuyi ba, dama Hansatu ta sawa ƴar wurin Husseina tallan piya wata ne gashi kuma tun safe ja'irar yarinyar bata dawo ba balle ayi amfani da cinikin datayi ayi cefane dashi" jin haka yasa ƙirjina dana Innati bugawa muka juya muka kalli juna, tun safe fa, yanzu kusan ƙarfe ukun rana kenan. Allah dai yasa lafiya. Tsaki Goggo taja tace "wannan yaran nikam na rasa wani irin rashin Sa'a suka shigo mana ahali dashi, yanzu haka shegiyar ƙila tana can wurin yan wiwi suna aikata iskanci dasuka saba, dake iskancin ajinin dangin uwarsu take" tafada tana hararan Innati, duƙa kai Innati tayi hawaye na gangarowa daga idanunta, itadai duk ba wannan ba, Allah yasa ƴarta tana cikin koshin lafiya. 🌷🌷🌷🌷🌷 Abu kamar wasa har ƙarfe bakwai na yamma babu Ameera ba labarinta. Tun hankalin Baba Auwalu da matarsa Hansatu bai tashi ba, ganin almuru yayi kowani ɗan talla da ƴar talla sun jima da dawowa gida, basai hankalinsu yatashi ba, to ina yarinyar ta tafi. Bata taɓa kaiwa irin wannan lokacin ba. Bayan sallan isha'i, Baba Auwalu baiga tazama ba, tunda yaji har yanzu yar ɗan uwannasa bata dawo ba. Babban ɗansa isyaku da mabiyinsa Ibrahim ya kira suka bazama neman ta. Ga uban hadari daya haɗu, iska mai ƙarfi yanata kaɗawa. Babu inda basu duba cikin unguwar nan ba, harma da unguwar dake kusa dasu kuma sunyi tambaya babu wadda yagane yarinyar da suke magana akai. Har ƙarfe sha daƴan dare babu labarin Ameera, to mezaicewa ɗan uwansa. Alokacin ne iska yaƙara yin karfi, nan da nan kuwa aka kece da ruwan sama mai bala'in karfi kamar da bakin ƙwarya , fakewa Baba Auwalu yayi shida ƴaƴansa har ruwan yayi sauƙi, wuraren ƙarfe sha biyu da rabi suka dawo gida. Lokacin Hansatu har tayi bacci itada ƴar ta Halima kamar babu wani abinda ya faru. Awannan daren kasa bacci Baba Auwalu yayi, to ina wannan yarinyar tashiga ne. Allah kawai ya kawo mafita. 🌷🌷🌷🌷🌷 Yadda Innati taga rana haka taga dare, haka kawai taji zuciyarta nata bugun uku uku, wuraren ƙarfe ɗayan dare Abba yayi wani irin miƙa jin iska mai daɗi na shigarsa, ahankali ya lalube saman gadonsa ya taɓo Innati wadda ke hawayen zuci tana addu'a Allah yasa komai lafiya wannan irin bugu da zuciyarta keyi. Shikam ko ajikinsa, hannunsa yakai yafara shafa Innati ahankali yana ɗan numfarfashi, anzo wurin. Inhar Abba ya fara laluɓan Innati ahankali to yana cikin halin buqata ne, amma komai nasa zafi yake yi mata. Jin haka yasa Innati fashewa da kukan datake ta kokarin rikewa, kamar Abba ya kwaɗa mata Mari, shi duk atunaninsa Innati na kukan taɓata dayakeyi ne,amma bai san cewa damuwarta daban bane. Cikin kuka Innati tace "Abbansu dan Allah ka taimaka ka kira yaya Auwalu ko anga Ameera, wlh hankalina gaba ɗaya ya karkata wurinta, ji nake zuciyata tana ta bugun uku uku" doguwar tsaki Abba yaja yace "yanzu ke Hussaina tsabar rashin sanin kiman miji, ina nemanki ashimfiɗa na kikeyi mun maganar wata shegiyar yarinya, ke angaya maki shi Auwalun baida matane, kawai sai in fara kiranshi da tsakar darennan dake nima na zama mahaukaci irinki. Dallah ni idan zaki bani haqqina kawai kibani banason doguwar zance" yana gama fadin haka kawai yajawota da karfi yafara yi mata abubuwa wadda ko motsa ta bayayi,toh baiwar Allah hankalinta ba'a jikinta yake ba balle taji daɗin abinda yake yi, dake kuma dama tunda tayi aure da Abba batasan wani daɗin s*x ba saboda shi kansa kawai yasani, idan kuma ya biya nashi to nata kuma ko oho ne. Jin abinda yake mata kawai ta kwanta tabar masa jikinnata amma kwata kwata bata wani tanashi. Ina kwance saman yar katifata wadda yagama jin wahala, ga cizon sauro duk ya addabe ni. Sai tunanin rayuwa nake, inama ace mu masu kuɗi ne kuma Abbanmu da kakanmu suna sonmu da babu abinda zai kai haka daɗi. Nifa a kullum tunanina bai wuce nayi kuɗi ba don gani nake kuɗi shine tushen komai, zai samar maka farin ciki aduk inda yake. Na riga na ayyanawa raina idan nayi kuɗi saina sayowa Innatina wannan haɗaɗɗiyar leshin damuka gani a kasuwa wani rana, sannan zan ƙarasa karatuna na sakandare tunda ayanzu dai na tsaya a haji na biyune aɓangaren sss, zanyi karatu nima inzama wata babba mai faɗa aji a wannan ƙasar tamu. Saina inganta rayuwar ƴan mata da zaurawa wadda ke fama da ƙuncin rayuwa. Ina so idan nayi karatu nazama lauya saboda na ƙwatowa Innatina ƴancinta ahannun Abba, ita kuma Goggo imma Allah yasa zansata agidan dazan gina, to daƙinta zai zamo ƙarami sosai wadda zata takure sosai acikinta kamar ƴar yari😂 Ni kaina danayi tunanin saida nayi dariya. Kullum kafin nayi bacci sainayi irin tunanukannan,shike ɗebe mun kewar ƴar uwarta Ameera, itace muke zama muyi wannan hiran da ita har tsakiyar dare kafin muyi bacci. ALLAH sarki koya take yanzu agidan Baba Auwalu, ko itama tana shan wahala ahannun matarsa Hansatu, dama nasan can ba sonmu take da Innatinmu ba. Ahaka naita tunanin rayuwa har bacci ɓarawo yayi nasaran saceni. Wuraren ƙarfe huɗu na asuba akayi wani irin gigitacciyar tsawa, wadda yasani farkawa kamar acikin kunnena wannan tsawa ta sauka. Take naji wani irin tsoro ya kamani, ance ba'a alaƙanta mafarki da wani ma'ana, to amma yanzu mafarkin ƴar uwarta Ameera nayi, kuma mummunan mafarki ne,inaji tana ihun sunana dana innati tana cewa ataimaka mata zasu kasheta, daidai ina ƙoƙarin kama hannunta akayi wannan tsawar. To me hakan ke nufi, anya Ameera tana lafiya kuwa. Gashi banida waya balle na kira naji. Kasa samun natsuwa nayi, ƙirjina sai dukan tara tara yake yi, ganin zama dai bazai yi mun amfani ba tunda bacci ya washe kawai na mike na fito waje cikin ruwan saman, abakin ɗakina na tsaya ina tarar ruwa nayi alwala, tsorone dani kamar farar kura dan haka sharp sharp nayi alwala na shigo ɗakina. Duk na jiƙe sharƙaf dan haka na tuɓe kayana na ɗaura tsumman zanina na sanya hijabi na tada Sallah. Nafilfili na dinga jerowa, bayan na idar na fidda Qur'an dina nafara karatu cikin zazzaƙar muryata. Nikaina nasan inada zaƙin murya😌, mafi yawancin lokuta Ni akafi sawa a musabaƙah dan nice ɗalibar data fi kowacce ƙoƙari kuma ga daɗin murya. Ban koma bacci ba har saida nayi sallan asuba, dake har yanzu ana ɗan yayyafi yasa banyi tunanin fitowa waje ba. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Karfe takwas na safe yayiwa Baba Auwalu a gidan Radio dan sanarwa akan ɓatar yarinyar wurinsa koda wadda yaganta, yabada lambar wayarsa dana Abba. Koda ya fito bai koma gida ba, kwata kwata hankalinsa yaƙi kwanciya,lallai duk inda Ameera take to bata cikin ƙoshin lafiya. Wani zuciyar yace to ko dai yaje wurin polisawa yasasu a lamarin, wani zuciyan kuma yace masa yaje gida ya sanarwa matarsa tukunna. Haka kuwa yayi, yana sanar wa Hansatu tayi alambaran babu wani polisawan da za'a kira, barin kawai suci musu kuɗi azo kuma ba'a ga yarinyar ba. Gara kawai in akayi sanarwa akayi sanarwa kuma babu wadda yaganta toh hala kwananta ne ya ƙare dan haka sai kowa ya ɗau abinda Annabi ya dauka. Sosai furucinta yabashi mamaki, wannan inda ƴarsa Halima ce abunnan yasameta daya zai yi? Wuraren ƙarfe ɗayan rana wasu yara suka shigo gidan Baba Auwalu suna ƙwala masa kira. Da da farko bai ɗauka kirannasu da gaske ba,dan sun saba kawai suyita ƙwalawa babba kira kamar sa'ansu. Can yaji mutanin angwa suna ihu. Da sauri yaɗora jallabiyarsa saman ɗan guntun wandonsa yafi to harabar gidannasa. Turus ya tsaya ganin jama'a maƙil agidansa kowa shi yake kallo, Hansatu da Halima duk suma sun fito, to meya kawo wannan mutanin kuma. Ɗaya daga cikin matasan dasuka shigo gidan yace "amma Allah saiya tambayeka Auwal,bazai barka haka ba. Wlh kun cutar da ƴar mutane, kun kasa riƙon amana. Yanzu inda ƴarku Halima ce ta shiga wannan halin a hannun wasu yazakuji. Kun muzgunawa rayuwar yarinya, kun sata zuwa talla gashi asanadinku yarinyar tayi rashin abu mafi muhimmanci a matsayinta na ƴa mace, turrrr daku wlh" duk Baba Auwalu bai gane me suke nufiba, to wai anga yarinyar ne ko kuma menene da wannan yake yi masa magana adaƙile. Bai ida cewa komai ba saiga wasu ƴan sanda guda biyu sunyi sallama sun shigo cikin gidan, cikin Hansatu dana Baba Auwalu basai ya ɗure ruwa ba, kamar sunga mala'ikan mutuwa, tsabar rashin gaskiya dason kare kai Hansatu tace "ikon Allah, Ni Hansatu, me kuma wnn shegiyar yarinyar take tajawo mana oho, muna zaman zamanmu cikin rufin asiri, yanzu wani laifi ta aikata da har polisawa suka zo wurinta. Ga..." Magananta ne ya maƙale sakamakon tsawar da wata tsohuwa wacce ake kira da Lantana tace "yi mun shiru Hansatu, duk unguwarnan babu wadda bai san hali irin naki na son kai da ƴaƴanki ba, kin takurawa ƴar wasu kikace taki ƴar ta gwal ce, amma hisabin ki tsakaninki da iyayen yarinyar nan bazai yi kyau ba, muguwa azzaluma kawai mara amana" cikin zallan rashin kunya Hansatu ta yatsina fuska ta bude baki zata yi magana ɗaya daga cikin polisawan yace "Malama kiyi mana shiru, bamuzo nan dan muji muryarki mara daɗinnan ba" cikin zallan rashin iya turanci Hansatu tace "sori Saa"😂. Baba Auwalu daya kasa wani kwakkwaran motsi, zufa ya jiƙa masa riga, yasan kome yasamu yarinyar nan, shi za'a ɗorawa laifi,mutanin nan kowa yafara cewa aiya kamata polisawa su kama Baba Auwalu da matarsa Hansatu, tunda dai ba'a kama wadda keda sa hannu a lamarin Ameera ba. Jin haka yasa Hansatu rantaba wata uwar salati, ina ita ina wani gidan yari, abinda ko angwar da gidan yarin garin nan yake bata sani ba. Da dai polisawan sukaga cecekuce yaƙi karewa suka kori kowa a gidan yarage dagasu sai su Baba Auwalu. Tsuru tsuru sukayi suna jiran jin menene makomarsu, ƴan sandan nan ba ƙaramin takaici ne ya kamasu ba, wannan wani irin rashin imani ne, ankawo muku riƙon yarinya amma haka kuka dinga muzguna mata, yanzu gashi me gaba ɗaya ya sameta. Take dan sandan yafara labarta wa Baba Auwalu abinda yasamu Ameeran kuma a inda suka samota. Wani bawan Allah ne ya zo station da safennan cikin tsananin tashin hankali, dasuka tambayeshi meya faru yace ai can yaga wata yarinya akarkashin main bridge kamar babu rai acikinta, ga roban pure water dinta agefe. Gaba ɗaya jini ya bata skirt dinta, gashinan dai. Yanzu haka ankaita asibitin cikin gari kuma likitoci sunce bazasu taɓa yarinyar ba sai ankawo ƴan sanda shi yasa ya taho wurinsu, sukuma sukayi bincike suka gano inda gidan yarinyar yake shi yasa suka taho. Cikin matsanancin tashin hankali Baba Auwalu yayi hanyar ƙofa baimasan inda zaije ba, kamo shi sukayi ganin irin ruɗanin daya shiga. Hansatu kuwa tsuke fuska tayi taja gefe ta zauna, tabbas tasan abinda yasamu Ameera bai dace ba, lokacin dataso tafara ɗorawa Ameera talla saida ta kai ruwa rana kafin Baba Auwalu ya yarda, to gashi kuma yanzu irin mummunan labarin daya riskesu da rana tsaka. Ahap ai duk yadda zata yi saita saluɓe tabar Baba Auwalu cikin wannan abun shi kaɗai, haka kawai akan yarinyar Hussaina bazata je gidan yari ba🙄 Haka polisawan suka ɗau Baba Auwalu cikin motarsu sukayi hanyan asibitin da aka kai Ameeran. Ɓangaren emergency suka tafi, nan fa sukaga abun tashin hankali. Da ƙyar likitoci ke iya riƙe Ameera tana ihu tana kururuwa su ƙyaleta. Kowa awurin tsananin tausayin ta ne ya kamashi, ba ƙaramin tabo mugayen mutaninnan suka barwa yarinyar ba. Yanzu haka tana cikin halin shock ne, Allah kaɗai yasan su waye wannan azzaluman da kuma ita yarinyar. Saida akayi mata alluran bacci sannan aka samu sauƙi, ahaka ma tana bacci tana firgita. Da aka nunawa likitoci baban yarinyar sosai suka haushi da faɗa kamar zasu dukeshi, har wata nurse mace take cewa "ku dama hausawa inda kuke ƙarewa kenan talla, yaranku bazaku zasu a makaranta suyi ilimi ba, jahilci ya rufe muku ido, kalli yanzu inda rayuwar ƴar karamar yarinyar nan ya shiga. To mene amfani shi dan Allah haba wannan wacce irin masifa ce" Baba Auwalu da jikinsa yayi sanyi klau ya ɗago ya kalli Ameera dake kwance, fuskarta yayi fayau kamar fatalwa. Yau ne rana ta farko dayaji tausayin yarinyar ya kamashi. Bai taɓa kyautata mata a rayuwa ba, wahalar datake sha nayau daban na gobe dabanne. Duk wani maƙo irin nashi saida ya fidda kuɗi akayi mata treatment. Daga nan kuma su polisawan suka sashi yabisu station yaje yayi signing wasu papers kan cewa duk abinda yasamu yarinyar idan ba'a gano inda mutaninnan suke ba shi da matarsa za'a kama dan zasu cigaba da bibiyar yarinyar. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Ni Aneesa na shiga uku da wannan tsohuwar, da sassafe nan Goggo tsabaragen rashin imani, ga sanyi haka wai tasa nazo nayi mata surfen gero na wanke, gaba daya jikina sai rawan sanyi yake, gashi tun jiya bansa komai acikina ba, Innati ma haka, duk wata kuzari dake tattare damu ya ƙare, aikin damukeyi gashinan dai kawai. Muna nan da safennan Abba ya fita da kansa ya siyo masa da kunun gyaɗa isasshe shida mahaifiyarsa, haka suka zauna anan tsakar gida muna aiki muna kallonsu musamman Ni wadda yunwa yagama cinye wa, bakina yawani bushe yayi fari fat. Dake haɗama ce, duk cin abincin su basu iya cinye wa ba, ragowar masa guda biyu da kunun gyaɗa rabin kofi suka bari. Babu yadda suka iya haka suka miƙa mana badon ransu yaso ba. Na ɗauko abincin ina ayyana rashin imani irinna Abba da Goggo, yanzu wannan abincin ko Ni bazai ishe ni ba balle Innati na. Nasan halin Innati sarai, sai tace kawai ita ta haqura ni naci, amma samm bazan yarda, innati na tanada ulcer. Nasan kawai jurewa take amma inta yini haka bataci komai ba toh ba ƙaramin tashin hankali take shiga ba. Haka na zauna nida ita muka ci masa kowa da ɗaya, kuma muka sha kunun muka bishi da ruwa. Mun ɗan ji dama dama duk da bamu ƙoshi ba, amma Hausawa sunce da babu gara ba daɗi. Inada haquri sosai a irin wannan ɓangaren, duk yadda yunwa tayi yunwa bazan taɓa zuwa wani gida roƙon abinci ba, kuma abun hannun wasu bai taɓa tsone mun ido ba. A islamiyyan mu akwai mutane da dama wadda burin su a kullum shine su nuna su sunada wani abu wadda zai sa ka maida kanka bawa awurin su, amma aduk lokacin da sukeyin hakan ba ƙaramin dariya suke bani ba. Har kirana ake da mai girman kai, wai duk da ni talaka ce amma sai girman kan tsiya, ina son abu amma bazanyi tambaya ba. Yoh shi talaucin hauka ne? Kamar jiya yauma banje islamiyya duk saboda Goggo. Ina cikin wanke kaya da ɗan sabulun da Innati tabarmun na wankin kayan Abba datayi jiya, naji ana sanarwa a radion Goggo cewa ana cigiyar wata yarinya mai suna Ameera, dammm naji zuciyata ta buga, banma ƙara shiga tashin hankali ba saida naji ƴan gidan radion suna describing din yadda yarinyar take, harda kuma lambar wayar da aka bayar na gane na Abba aciki don na haddace. Bansan lokacin danayi wuff na miƙe daga inda nake zaune ba nazo na ƙwace radion daga hannun Goggo na ƙara kasawa a kunne da kyau don tabbatarwa. Ƙafafuna dake neman kadani ƙasa nayi saurin zama dirshan aƙasa,Ameerata fa ake cigiya. Kenan mafarkin danayi a kanta da gaske ne. Inna lillahi wa inna ilaihi raji'uun...... React Comment And Share fisabilillah Reemah ✍️ 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 REEMAH ✍️ PG 6_10 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Yanzu mene mafita? Ina Ameera ta shiga? Tana hannun mutanin ƙwarai ko a'a? Wannan shine tambayoyin dasukayita yawo a ƙwaƙwalwata. Jin an ƙwace radion ahannuna yasani dawowa cikin hayyacina, ɗagowa nayi na kalli Innati dake tsaye akaina da radion ahannunta hawaye na gangarowa daga idanunta. Wayan Goggo ne ya fara ƙara ta ɗauka, nida Innati muna jiran muji wanene ya kirata, toh dama wayar Goggo badai ƙara ba, daga ɗayan ɓangaren mukaji muryar Baba Auwalu yana yi mata magana. Sosai muka kasa kunne nida Innati munajin maganar da Baba Auwalu yake yiwa Goggo, gaba ɗaya hankalinmu inyayi dubu to ya tashi,"Goggo, wlh na rasa yadda zanyi in kira yaya in faɗa masa maganar nan, kece kaɗai zaki iya taimako na. Jiya kamar wasa muka nemi yarinyar nan muka rasa, har dare muna nemanta ruwa a jallo. Nashiga tashin hankali matuƙa, yau da sassafe na tafi gidan Radio akan atayani sanarwa, ɗazu kawai ina gida da rana sai yara suka shigo suna ihun sunana. Dana fito ta tadda babban tashin hankali. Goggo wasu marasa imani sun yiwa yarinyar nan fyaɗe, naje asibiti amma in kika ga yadda yarinyar takeyi sai kin tausaya mata. Dan Allah ki tayani sanar masa, ko idan aka sallame ta daga asibiti nadawo da ita gida, sai uwarta tacigaba da jinyarta tunda nasan Hansatu ba iyawa zata yi ba" ashe dai nice kaɗai da Goggo muke jin sauran zancen amma Innati tun da taji kalmar fyaɗe komai nata ya tsaya cak, jikina ne ya fara ɓari kamar mazari har wani jijjiga nake. "Allahumma ajirnaa fee musibatina wakhlifna Khairan minhaa" Shine abinda na fara maimaita wa a labban bakina, tsaki Goggo taja tace "ai dama kowa da tasa ƙaddarar, kila Allah yayi wannan shine nata ƙaddarar babu yadda ta iya saidai ta rungume shi,ke kuma Bahaguwa naji kin je islamiyya basai kin damemu da addu'ar karya ba" wannan maganar ta Goggo ba ƙaramin taɓamu yayi ba, aiko maƙiyinka ne bazakayi addu'a irin wannan abun yasameshi ba balle kuma jikanka. Kamar an tsikara Innati ta miƙe wuff tayi cikin daƙinta da gudu, ina ƙoƙarin sa kai cikin daƙin nima mukaci karo da ita a hanya, hijabi ne ahannunta tana ƙoƙarin sakawa, idanunta yayi wani irin jaa wadda tunda nake ban taɓa ganin irinsa ba, sosai na tsorata da wannan yanayin tata, ko kallona batayiba ta raɓa ta gefena ta wuce. Duk maganar da Goggo ke yiwa Innati baisa ta tsaya ba, lallai kam yau nasan Innati na cikin tashin hankali. Daidai zata fita saiga Abba yasawo kai cikin gidan sukaci karo da ita, wani kallo ta watsa masa kamar ba Innati na dana sani ba wacce ke tsananin tsoron mijinnata. Ganin dai ba tsayawa zata yi ba Abba yasa hannu yajawota cikin gidan ya kulle ƙofa. Kukan da Innati na ke riƙewa tuntuni ne yayi nasaran fitowa, zama tayi dirshan abakin ƙofar gidan tana rusan kukanta. Toh shi Abba bai san meya faru ba ya juya ya kalleni, nima shi ɗin nake kallo da hawaye a idanuna. Goggo ce ta ce"wai kaji fa, wannan shegiyar yarinyar Auwalu ya kirani yanzu cewa an sameta aƙarkashin gada yau da safe, wai fyaɗe akayi mata. Toh ni inba munafirci irinna yaran zamani ba, mekike tunani a matsayinki na ƴa mace, kina Kai kanki inda Allah baikaiki ba, yanzu haka inada tabbacin cewa ita takai kanta, yanzu mai rabo ya tumurmusheta kuma ana cewa wani fyaɗe, nidai alambaran ban yarda ba, mu za'a maida yara"? Cakk kukan Innati ya tsaya, lallai yau Goggo takai maƙura, amma bari taji me Abba zai ce tukunna. Kamar zan buɗe baki nayi magana naji Abba yace "mtcheeew, yanzu wai don haka ne Hussaina ke ƙoƙarin buge ni ahanya zata fice batare da izini na ba? ahhh lallai wuyanta yayi ƙwari" bansan lokacin dana furta Abba da wani irin kausashshiyar murya ba. Yau kawai za'ayi ta ta ƙare. Innati ta mike a sukwane tayo kan Abba kamar mai aljannu, wani irin damƙe masa collar din riga tayi tana jijjigashi kamar zai faɗi kasa tana kuka tace " Zaidu, yau ba matarka keyi maka magana ba, uwa ce ke tsaye agabanka don yarta, yau dinnan za'ayi ta ta ƙare. Kai wani irin uba ne? Kaifa ka haifi wannan yaran, meyasa kake abubuwa kamar mara tunani. Badon komai nake riƙe zuciyata ba sai don ƴaƴana. Ina duk wata kokari dazanyi saboda ganin na faranta maka da mahaifiyarka, bansan me ake kira farin ciki ba tun daga gidan uwar goyona har gidan aurena. Nima fa mutum ce kuma mace, ina zuciya mafi rauni" Goggo data gama ƙamewa azaune tana kallon ikon Allah na kalla, azuciyata ina cewa inama inada iskokai da babu abinda zai hana ban rufe tsohuwar nan da dukan tsiya ba, duk itace SILAH(ASHANTY LOVE) kome Abba yake yi itace mai ingiza shi. Allah ya kawo mana daidai da ita. Wani irin wawan naushi Abba yabawa Innati a kumatu, take bakinta ya fara fidda jini. Igiyan babur dinsa ya cire yafara zabga mata ajiki yana cewa "Hussaina, ni har kin isa ki buɗe baki kina maida mun magana. Yaushe har kikayi wannan ƙwarin kan, kodai kinfara bin maza ne yasa kike ganin ko kin barni yau wani zai kwasheki amatsayin ragowata" ihu na yi kamar mai tashin iskokai. Ni kaina in aka tambayeni ya haka ta faru banida takamammen amsa, nadai san Abba ya na dukan Innati kuma nayi ihu, daganan bansan meya faru ba. Bude ido nayi naga Abba a ƙasa kwance sumamme, Goggo kuma tana ihun neman ceto wai na kashe mata ɗa. To ya akayi hakan tafaru, Innati kuwa tana zaune ko ƙala bata cemun ba. Can saiga makwabtan mu sun fara shigowa gidan. Kan kace me mutani suka cika gidan maƙil, Goggo na maida musu abinda ya faru. Ji nayi tana cewa "ƴarnan iskokai ne da ita, muciya ta ɗauka ta raɗawa ubanta akai haka kawai, so take ta kashe mun Zaidu na, wayyo Allah na shiga uku" Ni kaina abun ya bani mamaki,daga addu'a sai Allah ya amsa alokacin, waifa cewa nayi inama ina dasu danayiwa tsohuwa dukan tsiya saikuma ya juya kan Abba. Amma banji daɗin wannan lamari ba, dama dukkansu biyun na haɗa gaba ɗaya nayi wa dukan. Ko banza aina ramawa Innati na cin zalin da ake yi mata. Yayyafawa Abba ruwa akayi ya mike azabure yana wiƙi wiƙi da ido, gaba daya sai naji kunya ya rufeni, za ayi mun kallon mara kunya wacce ta duke babanta, to amma ai ba laifina bane, dama wai inada iskokai ne ko kuma kawai Allah ne ya kawo su danna ceci mahaifiyata. Saida komai ya lafa sannan aka fara raguwa a gidannamu har yarage dagani sai Innati dasu Abba. Tsit kakeji kamar anyi ruwa an dauke, muna jiran muji me zai faru, Innati da kumatunta gefe guda ya kumbura ta kalleni tace "Aneesa maza shiga ɗaki ki sanya hijabinki ki taho muje wurin ƴar uwarki, yau bazan kwana agidannan sainaga yarinyata" banyi musu ba na miƙe sumi sumi na shige akurkin ɗakina na ɗauko tsumman hijabina daya gama jin wahala. Ina fitowa Innati ta mike ta kamo hannuna, ko inda Abba yake bata kalla ba tasa kai muka fara tafiya, har mun isa bakin ƙofa naji Muryar Abba yana cewa "Hussaina, ki tabbata kina sa kafa a wajen gidannan abakin aurenki ne" kamar na kurma ihu, meke shirin faruwa,anya Abba yasan me yake faɗi kuwa? Abakin aurenta fa, kenan yana nufin kartaje ta dubo ƴarta inkuma tayi hakan to ya sake ta, wai wannan wani irin mutum ne? Ga mamaki na naga Innati taja hannuna muka isa bakin kofa, juyowa tayi ta kalli Goggo tace "Goggo saduwar Alkhairi, Allah ya haɗaku da daidai daku. Idan ba daidai nayi muku ba, Allah zai saka muku, idan kuma kune kuka zaluncemu nida ƴaƴana to insha Allah, nan bada jimawa ba zaku gani. Ma'assalam" tana gama fadin haka muka fice daga gidan. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Mainoma Mansion 🏛️ Gidane babba wadda kowa ya shaida zamansa agarin Kano. Gidan babban General ne na sojoji. Ko ina kewaye yake da sojoji masu tsaurin gaske. Kana kallon yadda suke shawagi a tsakar gidan kasan duk wadda yayi ɓatan hanya ya shigo gidannan to sunansa soriiiii. General Abdulazeez Isa Mainoma,mutum ne mai tsaurin gaske wadda ko ƴaƴansa bai bari ba a tsauri, shi yasa kusan duka ƴaƴannasa suka biyo shi a zafin rai musamman guda ɗaya wadda ake kira Babban Yaya. Matansa biyu, Hajiya Turai da Hajiya Azeeza. Ƴaƴansa kuma su bakwai ne, ƴaƴan Hajiya Turai huɗu, yaran Hajiya Azeeza uku. Mujahid(babban yaya), Ismail, Sultan sai Raihanah sune yaran Hajiya Turai. Amin,Mustapha da Jawad sune yaran Hajiya Azeeza. Zama ake na kwanciya hankali da tarbiyya agidan, dukkansu matan General babu mai banbanta ko ɗaya acikin yaran. Komai ana yinsa ne cike da kiyaye dokokin General watau Abby. Babban yaya(Mujahid), shine babban ɗan General Abdulazeez, kusan zance yamafi babansa tsauri, mugune bana wasa ba. Ƙannensa ba ƙaramin tsoronsa suke jiba, shi mutum ne mai ra'ayi sosai, yafiso duk abinda yafaɗa to kawai ayi shi alokacin koda kuwa kai Kanada abinda kake yi mai muhimmanci. Yanzu haka shine Efcc Boss a birnin tarayya Abuja. Idan aka gansa saika ɗauka sojane shima irin babansa amma kuma sam ba haka bane, kawai nature ɗinsa ne na yadda yake abubuwa gashinan dai. Miskili ne na ƙarshen misali, jarumi, ya ɗauki aikinsa da zuciya ɗaya. A yadda labari yazo, yana shiga office cikin sati ɗaya saida ya sa aka cire CBN governor, sannan kuma duk wasu senators masu satan kuɗi ba ƙaramin rugurguzasu yayi ba. Dake babansa kamar yadda sunansa yazo wato Mainoma, shi ɗin babban manomi ne, shiyasa kuɗin gwamnati bai taɓa damunsa ba. Yanada babban kamfani wadda ake producing kayan gona da dama, irinsu grains(shinkafa, dawa, masara, dss), harsu kayan lambu, ana exporting dinsu zuwa ƙasashen waje. Toh shima haka Mujahid bai zauna a aikinsa na Efcc Boss ba, shi ɗin mayene aɓangaren cyber security, irinsu ake yiwa laƙabi da "TECH BRO", saidai idan ya ƙyaleka ka cuceshi a ɓangaren kwamputa, amma bawai don baisam meyakeyi ba. Da a ƙasan waje yake zama, Us precisely (takamaime), da aka bashi appointment as Efcc Boss shine ya dawo nan kasa Nigeria. Sai na biyunsa mai biye dashi watau Ismail. Manyan maza kenan, shi ma ƙafan babansa yayo, yanzu haka yana matakin Captain ne a Airforce. Shi bai cika tsauri kamar Babban yaya ba, amma dai ba sauƙi. Na ukunsu kuma Sultan aka gentle bro. Shiɗin na kowa ne, baida damuwa kwata kwata. Likita ne shi, yanada babban asibitin kansa anan garin Kano. In yaran gidan sunada damuwa shi kaɗai suke iya zuwa su sama saboda sunsan shine mai sauƙin kai, ga kyauta ba kama hannun yaro. Saikuma auta Raihanah. Shalelen Abby, itace kawai ƴa mace agidan General. Itace sukazo Sa'a da yaron Hajiya Azeeza na biyu wato Mustapha. Ashekara ɗaya aka haife su, sunada shekaru goma sha bakwai su biyun, duk suna haji biyune a sakandare. Babban yaron Hajiya Azeeza Amin aka Black head. Bakomai yasa aka sa masa wannan sunan na saidon rashin jinsa. Yana biyewa abokai marasa jin magana. Shekarunsa twenty three. Yana three hundred level wadda tuni Yakamata ace yagama makaranta, amma tsabar rashin ji yayi spill over sau uku. Yakamata makarantar su koreshi, amma saboda tsoron mahaifinsa yasa suka barshi, kullum saidai yayita gararamba shida abokannasa suna kashewa ƴan mata kuɗi. Sai kuma autan wurin Hajiya Azeeza Jawad, yanzu haka yana jss three ne. Shekarunsa sha huɗu. Yau tun ƙarfe bakwai na safe aketa kai komo ana shirin zuwan Babban Yaya. Hajiya Turai (Mamy) takasa zaune balle tsaye, dakanta take inspecting part din MJ da ake gyarawa, tasan ɗannata badai ƙyanƙyami ba. Abincin dazai ci itada Hajiya Azeeza (Anna) su suka dafa masa. Duk wani abinda suke amfani dashi wurin girkawa ɗannasu abinci ba ƙaramim tsaftacewa akeyi masa ba. Kullum Raihanah kance "matar Babban Yaya tanada aiki agabanta". Ƙarfe ɗayan rana motoci sukayi convoy zuwa Aminu Kano international airport Dan tarban ɗan General Abdulazeez Isa Mainoma. Sojoji sunfi talatin wadda suka yi jeri har cikin airport din. Kowa da ak47 ahannunsa, gashi sunsa irin face mask dinnan nasu na sojoji da hand gloves, jikinsu a mummurtuƙe. Cikin takunsa na ƙasaita yafara taka matakalan jirgin. Namijin fama, the youngest Efcc Boss ever. Sanye yake cikin dakakkiyar three pieces designer suit dark blue. Fuskarsa sanye yake da face mask. Dogayen ƙafafunsa yake jefowa ahankali kamar me koyan tafiya. Duk yadda Babban Yaya yakeda zafi, amma baya abu cikin gaggawa, komai nasa abun burgewa ne, musamman yadda yake tafiya in a hot 🥵 way. Yana ida saukowa yayi gaba sojojin suka mara masa baya, kowa kuma sai hankalinsa ya dawo kansu musamman shi wadda ke gaba. Ba ƙaramin burgewa sukayi ba yadda suke tafiya gaba ɗayansu cikin takun ƙasaita. Bai jira anbuɗe masa kofar mota ba kawai ya bude da kansa ya shiga suka tada mota sai Mainoma Mansion. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Bayero University Kano. Administrative block. Office of the Vice Chancellor Ko sallama babu ya banƙade kofa ya shigo. VC dake attending wa mutane wadda baƙine daga wani University, ɗagowa sukayi gaba ɗayansu suka kalli wadda ya shigo babu ko neman permission. Wani dogon tsaki VC yayi ƙasa ƙasa yadda babu wadda yajishi, Amin masifa ne agaresu wlh. Har Allah Allah yake tenure dinshi ya ƙare saboda wannan yaron kaɗai, yasa rayuwarsa agaba. Kullum threatening dinsa yake kan cewa idan ya bari mahaifinsa yasan cewa yanada spill over sai yasa sojojin babansa sunyi masa azaba mai tsanani. To wakeso ya haɗa hanya da soja, balle kuma sojojin gidan General kamar special species ne na sojoji, ƙirar jikinsu daban yake. Ɗaya daga cikin baƙin VC wadda baisan Amin ba ya miƙe a fusace yace "Kai how dare you enter this office without permission, kana haukane?" Amin dake tsaye abakin ƙofa cikin wani irin shiga na bad boys, kyakkyawa ne sosai gashi dogo da ƙiran maji ƙarfi, ba fari bane kuma ba baƙi ba, za'a iya kiransa da wankan tarwaɗa. Hala kyawunsa ne ke ruɗansa yake ganin kamar babu wani sai shi. Askin dake kansa punk ne,irin askinnan da ake aske gefe da gefen kai sai abar gashi atsakiya. Wani kallon "who the hell is this one"yayiwa wannan mutumin da yayi magana. Shock da embarrassment ya kwanta luff akan fuskar VC, me wannan yaron yake nufi da kansa ne wai. Jiki asanyaye ya mike yana so yayi magana, amma yana tsoron batawa Amin rai, gashi kuma idan baiyi magana ba baƙinsa zasuyi tunanin ai tsoronsa yakeji. Cikin takun ƙasaita Amin ya shigo office din ya zauna saman sofa dake gefen table din VC ya zauna ya ɗora kafa daya kan daya. Prof. Ahmad Al kafawiy da ransa yagama ɓaci kuma dama shine baiyi magana ba, yanzu yace "Amin, lallai wannan ba tarbiyyan gidan General bane. Kuma i promise you daganan ina fita a office dinnan babu inda zan tsaya sai wurin mahaifinka" tsananin shock ya bayyana afuskar Amin, ya akayi wannan mutumin yasan mahaifinsa. Miƙewa yayi da sauri ya ƙaraso wurin Prof.Ahmad yace "ya akayi ka Sanni"? Murmushi irinna manya Prof. Ahmad yayi yace "Dama ba lallai ka ganeni ba, nikuwa nasan kowa ma gidanku. Kuma ka jira consequences dinka awurin babanku" yana gama fadin haka ya kalli VC ya girgiza kai irin I'm really disappointed in you, ya fice. Amin daya daskare atsaye ya kasa koda ƙwaƙƙwaran motsi, ai idan maganannan yakai kunnen Abby kashinsa ya bushe. Kai dole ne ma ya tsaida wannan mutumin. Da sauri shima ya fice yabi bayan mutumin. Amma me, kamar Flash har wannan mutumin ya isa first floor, Yana ficewa daga building din. Kara gudu yayi danya cim masa amma ina, lokacin daya sauko first floor yasamu mutumin har ya shige motarsa ya tafi. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Wai ina labarin Aneesa da Innati? Tafiya kawai muke nida Innati babu maiyiwa wani magana. To yanzu ina zamu? Wannan shine tambayar dake yawo a raina, muda ko sisi bamudashi. Kallon Innati nayi naga tana sharar hawaye da gefen hijabinta. Muna isowa bakin titi ta tsaida adaidaita sahu tace masa gareji zai kaimu. Ganin ina ƙin shiga yasa Innati fusata tace "Jammah ki maida hankalinki dani, inata kula da ke tun ɗazu nayi shirune kawai, kar kisa na sauke fushina akanki. Maza ki shigo mutafi" kamar zanyi kuka na shiga, to dame Innati zata biya kuɗin wannan keke napep din, nifa arayuwata banason wulaƙanci, nasan tabbas idan mukace wa mai adaidaitannan bamuda kuɗi ba ƙaramin wulaƙanci zamu sha ba. Mun iso babban garejin Adamawa muka sauko daga adaidaitan. Ga mamaki na naga Innati ta kunce ƙunzugunta dake daure a ƙugunta ta fidda kuɗi tabawa mai adaidaitan. Kallonta nayi itama ta kalleni, maka bakina nayi tsit ina tsoron ɓata mata rai. Mun iso wurin mota, muka tadda saura mutum biyu motar Kano ya cika. Ban ƙara shiga shock ba saida naga Innati ta ciro yan dubu har guda biyar ta biya mana kuɗin mota. To wai kodai anbawa Innati Zakka ne banida labari. Da muka fara tafiya sainaji duk na ƙagu mu isa, na ƙosa naga yar ƙanwata. Take baki hawaye masu zafi sun zubo mun, Allah ya isa duk wadda yayiwa ƙanwata wannan abun. Allah ma bazai barshi ba. Sai naji na maza gab dayansu, gani nake duk halinsu ɗaya. Ganin dai tafiya akwai dan nisa yasa na kulle ido nafara karatun Qur'an a zuciyata har bacci ya ɗaukeni. Ban farka ba saida naji Innati tana magana da driver kan cewa nan zai ajemu. Buɗe ido nayi naga ai har mun iso Kanon Dabo. Saukowa mukayi daga motar, Innati ta tare taxi, wani inyamuri ne acikin motar. Kuma da alama baya jin Hausa. Kallon mu yayi tunda ga sama har inda idonsa ya tsaya, ganin irin kayan dake jikinmu sai yake gani kamar bamuda wani kuɗi dan haka yaja motarsa ya tafi. Murmushi kawai Innati tayi, nikuma naja tsaki nace "duk halinku ɗaya, babu abinda kuka iya sai wulaƙanta mata". Da ƙyar muka samu wani taxi ɗin har ya yarda zai kaimu inda zamu. Kwatance Innati tayi masa na gidan Baba Auwalu. Tunda muka fara tafiya sainaji kuma gaba ɗaya zuciyata ta sauya, kamar na koma Adamawa dan tunawa nayi fa yanzu auren Innatina ya ƙare. Allah dai yabamu ikon cin jarabawa koda wacce irice. Dake Ni ban taɓa zuwa gidan Baba Auwalu ba, Innati ce kawai tasani dan haka tayi wa mutumin kwatance har muka iso. Bayan ta biyashi muka fito. Abakin ƙofa muka tadda babban ɗansa Ibrahim, abun mamaki shikam baida damuwa. Yana ganin Innati ya ganeta, har ƙasa ya tsuguna ya gaidata nikuma na gaida shi dan ya girmeni. Da sallama muka shiga cikin gidan, saidai abinda muka gani shiyasamu daskarewa atsaye. Ameera ce akasa tayi kneel down cikin wannan zafin ranan, aka ɗora mata dutse ahannu, matar Baba Auwalu Hansatu tana rikeda dorina ta wani haƙimce saman kujera tana cika tana batsewa. Tana ganinmu matsanancin tashin hankali ya bayyana afuskar ta. Batayi tunanin zataganmu awannan lokacin ba. Ameera na ganin mu ta yarda dutsen hannunta ta mike, da sauri tayi kanmu tana ɗingisawa alamar akwai rauni a tsakanin ƙafafunta, sosai take kuka harta iso wurin mu. Rungume ta Innati tayi, nima na haɗasu wuri ɗaya muka rungume juna muna kuka abun ban tausayi🥹🥹..... Like Comment Share fisabilillah 🙏 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 11_15 "knowledge is a virtue not everybody is destined with. Learn to use your tongue and your instinct will guide you through. Good morning great minds 🌞" 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Mun ɗau lokaci mai tsawo muna kuka kafin muka rarrashi kanmu tunda bamu maiyi mana sai Allah. Kallon Ameera nayi, fuskarta duk akumbure alamar yarinyar ba ƙaramin wahala tasha ba. Kallon Hansatu innati tayi da wani irin cold expression, uban ameeran ma ya wulakantata balle kuma itada take matsayin matar ƙanin mahaifinnata,amma ai ance ciwon ƴa mace na ƴa mace ne, shin wannan maganar gaskiya ce? Babu alama gsky. Shigowar Baba Auwalu kenan. Da mamaki yake kallon Innati dake tsaye ta kafe Hansatu da ido. Dake Abba yariga ya sanar dashi abinda ya faru yasa yasamu ƙarfin guiwa dazaiyi mana wulaƙanci. Ameera na manne da jikina ta kankameni sosai sai rawar jiki take. Kallon Baba Auwalu nake ina mamakin yadda Allah yasa gaba ɗaya ƴaƴan Goggo babu mai kirki a cikinsu daga mazan har matan, ai inna ce rashin kirki ma nayi sauki, rashin imani da sanin muhimmancin dan Adam duk Allah ya hada musu. Tunda muka taso bamusan gidansu Innati ba, kullum in muka tambayeta sai tace ahalinta sunada nisa. Kuma daganan shikenan bataso ta ƙara jin maganar. Hawaye Innati ta share a gefen idanunta ta kamo hannuna dana Ameera sannan ta kalli Baba Auwalu tace" na rabu da ɗan uwanka dan haka banida hurumin dazan zauna agidannan, duk wata alaƙa dake tsakaninmu ya ƙare saboda aurena dashi ya ƙare wadda inada tabbacin kasani" gyada kai Baba Auwalu yayi yace"hakane ya sanar dani, dama kuma ina jirane Allah ya kawoki kixo ki tafi da ƴartaki tunda babu wani alaƙa tsakaninmu kuma. Abinda yasameta kuma dan Allah karki ce laifinmu ne nida matata, kema kinsani tun ba yanzu ba Ameera akwai rawan kan tsiya, dan haka itace silan abinda yasameta" babu wani mamakin da zamuji dan Baba Auwalu yayi wannan maganar,yo Abba ma ya faɗa balle kuma wani daban. Bamu ɓata lokaci wurin wani dogon zance ba, amma alƙawari na ɗaukar wa kaina, Allah bazai taɓa haɗani da mutaninnan ba sai mun basu kunya. Abunnan da basuso Allah yamana inshallah muna fita agidannan kofofin Alkhairi zasu buɗu. Tafa hannu Hansatu tayi tace "ayyiyiri nanaye, yau Allah ya rabamu da ƙaya. Dama ba wani abinda take karamu dashi saima rage mana datakeyi, to aje can umma tagaida A'isha". Duk wannan maganar datake babu wadda ya tanka mata dagani har Innati. Kafin muka sanya kafanmu awajen ƙofa saida muka karanta addu'o'in neman tsari da nasara a sabuwar rayuwar da zamu shiga. New chapter new beginning👏 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 "Yanzu Dan Allah ɗannan har in mutu bazan ƙara ganin ƴata ba? Kullum innayi maka magana saikace kuna kan bincike, yau shekaru dai dai har talatin da uku amma binciken yaƙi karewa. Dan Allah in mutuwa tayi bakaso ka faɗamin ka taimaka ka sanar dani na cire rai nayiwa ƴata addu'a" wata tsohuwar dattijuwa ce wadda akalla zata kai shekaru saba'in da biyar aduniya,zaune a ƙasan kafanta kuma wani magidanci ne wadda shi kuma zai iya kaiwa shekaru hamsin da ƙari. General Abdulazeez kenan da mahaifiyarsa Hajiya Aneesa Sulaim wadda kowa ke kira da Hajja. Tsabar firgici ne ke kwance akan fuskar Abby akan wannan magana ta yarinyar Hajja watau ƙanwarsa. Yau shekaru talatin da uku kenan da bacewarta amma Hajja ta kasa mancewa da ita. Tun kafin yafara aikin soja yake aikin neman ƙanwar tasa ruwa ajallo, to ta ina zai fara bayan baisan su wanene suka ɗauketa ba shima lokacin yana yaro. Kallonsa Hajja tayi tace "ɗan Isa, ƴata bata raye ko?, Meyasa kullum idan nayi maka wannan tambayar kake kin fadamin gaskiya, kullum ni ina ji ajikina wata rana ƴata zata dawo gareni. Wlh ko shekara ɗari tayi inhar naganta ni dinnan zan iya ganeta" jikin Abby yayi sanyi, kullum idan rikicin Hajja ya tashi tofa babu mai iya kwantar mata da hankali sai mutum ɗaya. Kiran da akayiwa Abby awaya shine abinda ya kubutar dashi ahannun Hajja har ta bari ya fice afalon. Zama tayi ta kafe makeken TV dake gabanta ido amma sam hankalinta ba'a nan yake ba, ina ƴarta take, shin tana raye ko kuma mutuwa tayi? ************* Mamy ta kasa zaune ta kasa tsaye, tuntuni akaje ɗauko Mujahid to meyasa har yanzu basu iso ba. Kodai sun tsaya a wani wurinne. Ta duba part dinsa yafiso akirga duk dan kawai ta tabbatar cewa gyaran da akayi masa komai yayi. Raihanah da Mustapha na zaune saman carpet suna buga game ɗin Chess, sunyi nisa awasansu har basuji lokacin da aka buɗe kofa aka shigo ba. Saiji kawai sukayi anyi sama da tray din wasansu sama. Tashin hankali, kallon juna sukayi suna wiki wiki da ido. Mutum ɗaya ne zai yi wannan abun, shikenan nasu ya ƙare. Yana tsaye akansu fuskarsa a murtuƙe wadda hakan ba ƙaramin fidda kyawunsa yayi ba. Duk da ba murmushi ko magana yake ba, hakan bai hana two side dimples dinsa bayyana ba. Dogone amma ba sosai ba, fatarsa nada haske sosai kamar ba ɗan Nigeria ba. Yanada wani irin murdadden jiki mai ban sha'awa. Hannunsa biyu saman ƙugunsa yana binsu da wani irin kallo irinna zaku gane kuranku dinnan. Cikin wani irin angelic cool voice kamar wadda aka sa dole yayi magana yace "ban hanaku buga game ɗin Chess ba"? Muƙut suka hadiye yawu babu wadda ya tanka masa. Wannan abun shi yafi bata masa rai, ya tsani yayi magana ashareshi don shi bai yarda da principle din repeating magana ba. Yanzu kam tsananin bacin raine ya bayyana afuskar tasa, tsawa ya daka musu yace "You guys are very stupid, ba daku nake magana ba. Oya ku miƙe zaku serving punishment" Raihanah harta fara ruwan hawaye, Allah dai ya kawo Babban Yaya sai yadda akayi dasu. Frog jump yasasu sunayi to and fro a falon Mamy wadda keda girma da faɗi bana wasa ba. Kan kace me sun hada zufa suna ruwan hawaye. Mamy na saukowa daga upstairs taci karo da Babban Yaya na aiki. Girgiza kai tayi tace "Allah yayi". Ƙarasa saukowa tayi ta nufosu, yana zaune saman sofa guda, ya cire suit din jikinsa yarage dagashi sai rigan ciki ya naɗe hannayen rigar kamar mai shirin yin dambe, hakan yabawa murdadden dantsen hannunsa bayyana farare tas masu ɗauke da gargasa wadda ke kwance luff. Mustapha na ganin Mamy ya ƙara sautin kukansa yadda za'a ji tausayinsu akyalesu. Wannan ba ƙaramin tunzura babban Yaya yayi ba, miƙewa yayi ya nufosu gadan gadan, haba mezai faru. Miƙewa sukayi a sukwane suka wuce wurin Mamy suka boye abayanta tunda dai sunsan bai isa ya tabasu ba suna manne ajikinta. Ganin Mamy yasa yadan saki fuskarsa ya shafa keyarsa, "har an dawo anfara samun ƴan autana agaba ba"? Hararan su yayi da brown eyes dinsa dake glowing kamar na mage bai ce komai ba. Zasu sani ne, yanzu sun samu ancecesu amma su kiyaye haduwarsu dashi. Kamar wadda zai yi kuka yace "Mamyyyy na" wani irin jan sunan yayi cikin sigar shagwaba wadda kamar hakan nature ɗinsa ne idan yana tare da mamyntasa. Rungume ta yayi yasa hannunsa ta bayanta ya kamo kunnin kannen nasa yaja kamar zai balla har saida suka saki ƙara alokaci daya sukace"Babban Yaya dan Allah kayi haquri". Yana sakesu kowa yayi hanyarsa. Mannewa yayi da mahaifiyartasa yana shaƙar kamashinta ɗaya daɗe baijiba. Gaskiya ne da bahaushe yace duk wadda yabar gida, gida ya barshi. Wani irin farin ciki ne da annashuwa suka ziyarceshi duk da hakan bai nuna a kyakkyawar fuskarsa ba. Jan kunninsa Mamy tayi tace "wannan ɗan Allah ya shirya mun kai, kaki yin aure kullum saidai cin zalin yara da shagwaba ka iya"kamar wani karamin yaro haka yayita shigewa Mamy har suka iso bakin ɗakinsa inda anan tajuya tasauko shikuma ya shige ɗakinnnasa. Wani irin kanshi ne mai sanyaya jiki ya buge shi,komai kalkal kamar sabobbi. Bawani tarkace afalon. Dan madaidaicin farko ne wadda yaji hadaddun Italian cushions white color, ga makeken TV asaƙale abango. Sai center table Dan madaidaici. Miƙela yayi tsabar gajiya dake fuskarsa ya kwanta saman dogon sofa, kallon ceiling din falon yake hannunsa ɗaya bisa goshinsa ya kurawa chandelier ido, can kuma ya miƙe wuff kamar ya tuna da wani abu, wani ƙofa magani mai kyan gaske na gold ya nufa. Babban yatsansa yasa kofar yayi scanning sannan kiii ta buɗu. Masha Allah, wani hadadden bedroom ne kona sarki albarka. Komai yaji zamzam yamafi na falo. Can cikin dakin naga katon frame wadda aka manna abango amma anrufeta da farin kyalle. Cikin takun sa mai cikeda natsuwa ya isa har wurin hoton, ya ɗau kusan minti ɗaya kafin ahankali kamar maijin tsoro yasa hannu ya buɗe kyallen. Wata matashiyar mace ce kyakkyawan gaske wadda akalla zata yi shekaru ashirin da shida hannunta na rikeda wani jariri fari sol mai bala'in kamada ita. Ahankali yasa hannu ya shafahoton yanajin wani irin radadi azuciyasa. To mene ma amfanin rataya wannan hoton tunda bata tareda shi kuma? He misses her so much it hurts, ta zama wani bangare ajikinsa wadda duk yadda zai yi ya cireta yakasa. Labbansa na rawa ahankali yafurta "Hayaaty". Ganin zai ƙara shiga halin dayake shiga aduk lokacin daya kalli hotonta kuma abinda ya faru abaya yana dawo masa ƙwaƙwalwa kawai yasa ya rufe hoton ya juya zuwa king-sized bed dinsa. Kwanciyar rufda ciki yayi ya kulle idanunsa kamar mai bacci amma kuma ba bacci yake ba, wani siririn hawaye ne ya fara gangarowa daga kurmin idanunnasa. Toh fa Babban Yaya da kuka kuma?🤔 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Tafiya muke acikin unguwa bamusan inda muka dosa ba tunda wannan ba garinmu bane. Da ƙyar Ameera ke iya takawa hakan yasa Innati tsugunawa tace ta haye bayanta. Duk inda muka ɓullo idon mutane na kanmu, kamar dai kowa yasan abinda yasami Ameeran, wasu har nunata suke da yatsa. Ikon Allah, mutane ba tausayi. Har muka fito titi inda motoci suke wucewa. Can dai naji ina, wani irin juyi cikina keyi alamun yunwa, rabona da abinci mai kyau na mance. Wani wuri muka samu inda ake saida abinci na ƴan talakoki, anan Innati tace muje muci abinci. Nikam har yanzu Innati bata daina kasheni da mamaki ba,a ina tasamo wannan kuɗin. Shinkafa fara da miya sai pure water, yadda muke cin abincin dagani har Ameera har saidai mutane suka juya suna kallon mu. Ameera ce ta ƙware tsabar rusan abinci. Tana shan ruwa taci gaba daga inda ta tsaya har kerma jikinta keyi, sosai tabani tausayi. Muna zaune mukaji gunjin motoci sun faso kai cikin harabar wurin, bamu gama tunani ba sai ga wasu jiga jigen sojoji sun sauko daga cikin motocin, da kaɗan ban saki fitsari ba, wani irin tsoro ne ya rufeni lokaci guda. To mekuma ya kawo wannan mutaninnan, Allah dai yasa ba laifi mukayi ba. Abun bai kara bani tsoro ba saida naga wasu sojojin sun shigo da gudun gaske kowanne rikeda bindiga ahannunsu sunyi layi su goma, biyar a gefen dama biyar a gefen hagu suka daga bindigarsu sai paaaa kakeji. Ameera dake gefenmu take ta saki fitsari a wandonta,Ni kaina riƙe kaina nake. Ba ƙaramin tsoron sojoji nake ba, musamman tunda ba ganinsu nake ba agarinmu. Wai nikam me zai kaini inda sojoji suke ko a mafarki inaa. Wani dankareren mota ne ya sawo kai cikin wurin, bansan sunan motar ba amma dai nasan duk yadda akayi motar akwai kuɗi sosai. Soja daya ne ya buɗe motar, kusan minti biyu kafin wani kafa mai sanye da kakin sojoji ya fito, har mutumin ya ƙarasa fitowa bamu daina kallon wurin ba. Wani hadadden magidanci ne fari amma kuma ya manyan ta. Kakin sojoji ne ajikinsa wadda ba ƙaramin amsarsa yayi ba, sojojin nan sukayi masa salute 🫡 kamar dai yadda sukeyi idan wani babba ya iso wuri.. Gefenmu naji wasu matasa suna cewa "Jenar Abdulazeez Isa Mainoma kenan, mazan fama. Gsky duk wadda sukazo wurin nan yau kamar dai mu mun taki Sa'a, Allah ya kawo mana karshen wahala da yardarsa" juyowa nayi na kalli wadda aka kira da Jenar din, gaskiya kuɗi yayi arayuwa, kalli yadda jikinsa ke wani sheki kamar ba tsoho ba, akanme nima bazanso nayi kuɗinan ba. Gaba ɗaya mutanin suka miƙe ganin haka yasa muma muka mike, kowa yafara sara masa, muma ɗin haka mukayi. Ahankali yafara takowa inda muke tsaye, Innati ta kalleni nima na kalleta, mekuma yasa yake zuwa wurin mu. Bamu gama tunani ba har mutumin ya iso wurin mu, makwat na hadiye yawu ina zaro ido waje. Abby da ya kafe su Innati da ido musamman ita innatin, meyasa zuciyarsa ke fuzgarsa zuwa garesu, kodai saboda shirin dayagani ajikinsu ne wadda ya nuna su ɗin mabukata ne sosai. Da murmushi afuskarsa ya kalli Aneesa wacce aƙalla zatayi shekarar ƴar autarsa Raihanah, inba idonsa ne ke ƙaryatasa ba zai iya cewa gaba ɗayan su su ukun Innati, Aneesa da Ameera suna Kamada Hajja.... 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Gogho abun duniya ya ishe ta sai faman sakin tsaki takeyi akai akai. Abba dake ɓare mata lemu yakalleta yace "Goggo menene lafiya kuwa"? Ajiyar zuciya tayi tace "haka kawai naji gidan ba daɗi tunda Hussaina ta tafi. Yanzu wazaina mana bauta, kadaisan babu abinda zan iya yi da kaina." Yatsina fuska Abba yayi yace "ahap Goggo karki damu kanki, Ni dinnan akwai wasu kudaden dana adana gobe gobe nan zan kai gidansu Abu zan biya sadaki, dama mahaifinta yace ni kaɗai suke jira ayi a ɗaura auren" hamdala Goggo tayi tace "ashe dai abun ya matso Allah, to haka akeso". Miƙewa Abba yayi yace "bari indauko kudaden mu kirga tare mu tabbata sun cika" da sauri Abba ya shiga ɗakinnnasa ya lalube jakan kudinsa daga kasan gado. Har wani zakadi yakeyi ya buɗe jakan, yana budewa yaga abinda idanunsa suka kafe wuri ɗaya ya kasa koda motsi ne🤣🤣🤣🤣🤣....... Like Comment Share fisabilillah 🙏 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 16_20 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Har wani zakadi yakeyi ya buɗe jakan, yana budewa yaga abinda idanunsa suka kafe wuri ɗaya ya kasa koda motsi ne. Wani iska mai sanyi ne yaji ya buge shi, lokaci guda yaji kamar an dauke duk wani kuzari ajikinsa. Suuu ya tafi kamar zai faɗi, adaddafe ya zauna saman gadonsa ya shafe fuskarsa. Goggo dake zaune awaje taji shiru kamar anyi ruwa an dauke tafara kiran sunansa, jin shiru bai amsa ba yasa ta mike ta buɗe labulen ɗakinnnasa, Abba na zaune akan gado ya kafe wuri ɗaya da ido babu ko kyaftawa, yama rasa ko ihu zai kurma ko kuma salati zai yi ko kuka. Hussaina ta cuce rayuwarsa tagama dashi. Goggo tayi masa kiran duniyannan amma ko ajikinsa. Kamar me tsoro tasa hannu tadan taɓashi, afurgice ya ɗago ya kalleta, bakinsa na rawa yace "Goggo Hussaina ta gama dani, ta gama da rayuwata itada ƴarta sun gudu da kuɗaɗena, na shiga uku" kamar Goggo bata ji meyace ba sanadiyyar wani tsuuuu dataji cikinta yabada, mene? Mene? Mene? Hussaina ta sace kuɗi ta gudu, shikenan nasu ya ƙare, ta ina zasu fara yanzu. Bata iya cewa komai ba kawai ta mike asukwane tayi waje ta ɗau buta da gudu tayi bayi sakamakon ruɗewar da cikinta yayi lokaci ɗaya sai gudawa kawai takeyi ba kakkautawa🤣🤣🤣🤣. Toh yanzu ina ma zasu fara nemanta bayan ta kai kusan awa uku da barin gidannan. Amma ta cuce rayuwarsu. Ance kamuwar Allah yafi na mutum, wannan kuɗin da Innati ta ɗauke nata ne halak malak, sai dai ma ace Abba ne ya hanata haqqinta. Uban goyonta wadda shine ya aurar da ita ya bata ɗan gona madaidaici, amma Abba ya saida gonan harma yafara cin kuɗin, duk tunaninsa duk abinda yakeyi Innati batada wayau ne shiyasa batace komai ba amma baisan tarashi kawai take ba. Gashi yau Allah ya ɗorata akansa har ta samu ta damƙi haqqinta bata bar gidan hannu wofi ba. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Abby dake kallonsu Aneesa kamar akwai inda ya sansu kawai yaji tausayin bayin Allahn ya kamashi lokaci guda, musamman yadda yaga fuskar Ameera duk akumbure kamar anyi mata duka. Innati ma jitayi kamar akwai inda ta sanshi, amma tamance a ina ne. Cikin muryan tausayi yace "bayin Allah, daga ina kuke, me kukeyi anan" kowa kuma sai mamaki ya kamashi, meyasa duk cikin dunbin mutanin dake wurin bai iya yiwa kowa magana ba sai wannan almajiran. Innati ce tayi magana tace "daga Adamawa yallaɓai" gyada kai yayi yace "kunada zama ananne ko kuma akwai inda zaku daganan"? Yaƙara jefo musu tambayan, kamar me jira da sauri nace "wlh babu inda muka sani agarinnan, kuma bamuda kowa. Bamusan ko ina agarinnan ba, gash..." Ban gama magana ba naji Innati ta buge bakina tana hararana alamar inyi shiru,, cunno baki nayi gaba kamar zanyi kuka. Murmushi Abby yayi, yadda tayi ɗin sak yadda Raihanarsa takeyi idan tana shagwaba. Juyowa yayi ya kalli wani soja acikin sojojinsa yace" ina so akai mutaninnan sabon estate dina dana ginawa marasa ƙarfi, abasu apartment guda su zauna aciki, abasu duk wani abinda suke buqata. I'll get back to them in the meantime inshallah". Da sauri Innati tace "a'a yallaɓai, wlh daka bari. Bazamu rasa wurin kwana ba da izinin Allah" kamar nayi ihu, meyasa Innati takeyin hakane wai don Allah, yanzu Allah ya kawo mana mataimaki amma tana cewa a'a, tsakani da Allah ita kanta tasan karya takewa kanta, babu inda zasu zauna agarinnan saidai in a gindin gada zasu na kwana. Abby daya gane cewa mutanin atsorace suke dashi yace "i insist, kar ku damu. Sojojina suke gadin wurin. Babu abinda zai sameku, dan Allah ku kwantar da hankalinku", badon Innati taso ba ta yarda. Harta Bill dinku damukaci abinci shine ya biya mana. Mutanin wurin kowa ya fara kuskus, wasu suna cewa kullum suna Zarya awannan wurin amma Jenar bai musu Alkhairi ba sai mu damuka zo yau yau. Ya ɗau lokaci sosai awurin yana ta rabawa mutane kuɗi, wasu kuma matasa ne wadda sukeda takardun karatu duk sun haɗo sun kawo masa. Ɗaya daga cikin motan sojojin akasa muka shiga, duk mun Kame kanmu wuri ɗaya inda Innati ta kankamemu ajikinta kamar za'a rabamu. Munyi tafiya mai ɗan nesa kafin muka iso bakin wani gate mai girman gaske inda sojoji ne masu gadin dana gani suna zaune ga bindigarsu agefensu. Suna ganin motan mu suka tashi suka wangale mana gate ɗin gidan, wurine mai girman gaske sashe sashe sunfi aƙirga yan madaidata masu kyau daidai misali. Gaban wani sashe sojojin suka tsaida motarsu sannan sukasa muka fito. Muna fitowa suka miƙawa Innati makullen gidan sannan suka ce mana anjima za'a kawo mana kayan amfani. Bakina kin rufuwa yayi, Allah kenan. Mun fito batareda tunanin yau yau dinnan Allah zai kawo mana mafita ba amma gashi. Anbamu gida kyauta halak malak batareda munsha wahala ba. Godiya Innati tayi musu. Saida mukaga tafiyarsu sannan tasa makullin tabude ƙofan gidan. Da sallama abakinmu muka shiga, ɗan ƙaramin falo ne wadda babu komai acikinsa sai ɗan ƙaramin carpet wadda ke malale aƙasa. Can gefen falon kuma kofofi ne guda biyu, saida muka shiga ko ina muka bubbude muka duba, Alhamdulillah gidane wadda mu awurin mu kamar aljanna aka bamu in za'a hadashi da inda muka baro. Dake akwai ruwa a ko ina babu ruwanmu da wani fita debo ruwa akai. Da ruwan sanyi muka yi wanka gaba ɗayanmu. Saida muka biya sallolin da ake binmu kafin muka zauna muna fuskantar Ameera nida Innati. Sai yanzu muka samu daman kebancewa dagamu sai mu, kafin Innati tayi wani magana kawai Ameera tafashe da kuka tana faɗin "Innati sun cuceni, sun gama da rayuwata. Wlh har duniya ta naɗe bazan taba yafe musu ba" yadda take sambatu kamar wacce ke ƙoƙarin zarewa saitabamu tausayi. Wani sabon shafin kukan muka buɗe muna rerawa gaba ɗayanmu. Mun jima sannan Innati tayi ƙoƙarin rarrashinmu, saida ta tabbata hankalinmu ya kwanta sannan tacewa Ameera"kin sansu ne? Kin san inda sukeda zama? Kin shaida fuskokinsu?" Da sauri ta girgiza kai alamar a'a tace "bansansu ba Innati, amma yaran masu kuɗi ne dan acikin wani mota suka zo mai girman gaske su uku. Ɗayan cikinsu dogone kuma yanada jiki kuma ba fari bane. Cikin su ukun ma Innati shine kawai yayi mun fyaɗe, sauran sun tayashi rike Ni ne saboda kokuwan ceton raina danayi" share hawaye nayi nace "ɗaukan ki sukayi amota"? Gyaɗa kai tayi tace "sun shaƙa mun wani abune mai ƙarfin gaske ahanci na , daganan ban sake sanin inda nake ba. Sai farkawa nayi naganin a wani hadadden daki, shi wannan mutumin shina fara gani dagashi sai gajeren wando. Innati har duka saida sukayi mun kalli" tafada tana nuna mana shatin bulalai ajikinta wadda ya nuna kamar da igiyan madauri wandon maza akayi(belt). Wannan rashin imani har ina. Dan kawai yarinya ta fito neman kuɗi sai wasu yan iska su ɗauketa su keta mata haddi, wlh Allah ya isa. Munci kuka mun godewa Allah, kuma mun barsu da Allah tunda bazamu iya dasu ba, amma aisu basufi ƙarfin wadda ya halicce su ba. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Yana tsaye gaban makeken bathroom mirror dinsa, ƙugunsa daureda towel iya guiwa. Abs dinsa sun wani fito radau radau saman lafaffen cikinsa sun haɗe da vline dinsa, gashin kansa dake da bala'in yawa kamar mace ya kwanta saman ƙafaɗarsa yana digan ruwa, golden brown sharp eyes ɗinsa na dauke da wani cold expression wadda bazaka iya tantace halin dayake ciki ba. Hannunsa hands akimbo yana ƙarewa ƙirar jikinnasa kallo. He looked so sexy🙈🙈. Yau shekarunsa uku kenan babu Neehal ɗinsa ataredashi, it feels like a dream. Yarasa meyasa yakasa cireta aransa,kodan saboda itace first love ɗinsa? Lallai Neehal ɗinsa tadabance, sai an tara mata ɗari za'a samo guda daya wacce ta yi kusa da ita a kyau. Itace kawai jarumar macen data iya ɗaukan nauyinsa harna tsawon lokaci. Babu mace, he repeats babu macen dazata iya da buqatunsa har yau baiganta ba. Shiyasa kawai he prefers to overwork himself dan ya cire wannan tunanin azuciyarsa, gara yayita zama ahaka har Allah ya ɗau ransa. Bazai taɓa iya trusting wata mace aduniyar nan ba, the heartbreak he has undergone is enough for him. Women are cheaters🤔inji Mujahid fa bani na faɗa ba. Hand dryer ya ɗauka yafara busar da gashin kannasa wadda ke fidda wani irin ƙamshi mai daɗin gaske na oils. Bayan ya gama ya wuce makeken closet dinsa,gefen kayan bacci dake shaƙe da different brands din kayan bacci masu tsadan gaske. Komai nasa cikin miskilanci yake yinshi, wani riga da wando na cotton yard honey colour ya fitar da takalmin su irinna yawon ɗaki mai laushinnan ya dauko sannan yadawo cikin dakin. Bayan ya gama sawa ya tsaya gaban mirror din ya ɗau turarensa na Oud Al-layl na maza ya feshe jikinsa gaba ɗaya. Gashin kansa kuma ya tufke wuri ɗaya da ɗan ƙaramin rubber band, ba ƙaramin fidda masa zallan kyawunsa style dinnan yayi ba. Shi kansa saida ya gyaɗa kai irin "this is it" dinnan kafin ya juya ya koma wurin study table dinsa. Wayarsa ƙirar Samsung Z flip ya ɗauka yafara duba emails da aka turo masa. System dinsa da shima same Company ne da wayarsa ya buɗe, yana danna power button hoton matannan ta ɗazu ya ƙara bayyana. Amma wannan karon ita kadaice, tana sanye da Arabian gown babu dankwali akanta, kannata yasha kitso ƙanana tana murmushi hannunta daukeda jan fure aka ɗauketa hoton, ba ƙaramin kyau tayi ba. Saida yadauki lokaci yana kallonta sannan yacigaba da abinda yake. Wayarsa ne yafara ƙara, sunan "Abby" ya bayyana akan screen ɗin. Daukawa yayi ya amsa da sallama cikin ladabi, Abby aɗayan gefen yace " haba Babana, kazo tunda rana amma bamu haɗu ba. Abincin ka ma duk adaki kaci. Kana lafiya daiko"? Yatsina fuska yayi murya ƙasa ƙasa yace "Yes Dad, ina Lafiya" badon Abby ya yarda ba kawai ya ce "shikenan, yanzu dai tunda dare yayi mubari sai gobe mu haɗu ko"? Gyaɗa kai yayi kamar mahaifinnasa na ganinsa,kit ya kashe wayar bai jira ance komai ba. Wani irin murɗawa yaji cikinsa yayi daidai maransa, saiga mutuminku na matse ƙafa wuri ɗaya, can kuma ya mirgina ya faɗa saman guiwowinsa yana dafe da cikinsa, nan da nan ya haɗa zufa. Da ƙyar ya iya rarrafawa da guiwa zuwa inda fridge yake ya ciro goran ruwa, ya koma wurin side drawer din gadonsa ya ciro magani ya haɗiye yana maida numfashi. Guiwansa na ƙasa rabin jikinsa na kan gado ya kwanta saman hannunsa guda, dayan kuma still yana cikinsa. Rufe ido yayi kusan two minutes can kuma kawai saiya fashe da wani irin kuka kaman ƙaramin yaro. Sosai yake kukannan kamar ba Mujahid ɗan Jenar Abdulazeez ba. Har wani sheshsheka yakeyi,bakinsa na rawa yafara furta "Neehal why, why did you do this to me. Why would you go away from me when I needed you the most, why"? Saikuma ya ƙara fashewa da sabon kukan. Atake wani irin zazzaɓi ya rufeshi, jikinsa yahau kakkarwa yana rawan sanyi. Da ƙyar ya haura gadonsa ya jawo lallausan duvet ya rufe jikinsa ya kashe wutan dakin gaba ɗaya. Sorry Babban Yaya 🥹🥹 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Karfe goma daidai ya dinga buga horn abakin gate ɗin gidannasu. Sojojin dake gate suka wangale masa ita ya danno hancin motarsa da wani irin gudu kiiii. Sports car ne mai kyan gaske yellow color. Fitowa yayi ya ƙulle motar yana cigaba da rera waƙansa yana kaɗa kai kamar ƙadangare. An gama yawon dare kenan sai yanzu aka ga daman dawowa gida. Amin ba ƙaramin mayen mata bane, shidai abarsa da wannan, bai taɓa koda ɗandana wani abu wai shi giya ba. Tafiya yake cikin izza har ya iso bakin apartment ɗinsu, baima lura da motan MJ dake pake a tsakar gidan ba sai yanzu. Kansa yayi wani irin sarawa lokaci guda. Dama Babban Yaya na gari shine yakai wannan time ɗin bai dawo gida, shikenan kashinsa ya bushe. Gobe sai ya yabawa aya zakinta. Kamar wadda aka zarewa laƙa ajiki ya buɗe ƙofan falon Ammi ya shiga. Babu kowa an kashe komai na falon. Hasken wayarsa ya kunna cikin sanɗa yafara haurawa stairs, bai ankara ba kawai yaji yaci karo da mutum. Har zai kurma ihu Abby yayi saurin mauje masa bakin da bayan hannunsa, collar din rigarsa yakama yajawoshi har ƙasan Babban falon sannan ya kunna wuta. Amin na ganin Abby yafara salati, wai meke faruwa ne yau. Dama Abby ma yadawo gari, inna lillahi. Zama Abby yayi kan sofa yace "yau dinnan ni da kaine agidannan Amin. Dama bakasan ya ake bawa sojoji horo ba yau zan koya maka, oya kneel down and raise your hands up" kamar zaiyi kuka haka babu musu ya tsuguna yayi abinda aka umurce shi. Wani ƙaton stool Abby ya dauka ya ɗora masa saman hannunsa dake sama sannan yace "karka kuskura ka sake abunnan ya fado ƙasa idan ba haka ba nida kaine" hannunsa na rawa haka ya riƙe stool dinnan bai bari ya fado ba. Abunka da tsohon jinin army, zama Abby yayi ya ɗora ƙafarsa ɗaya kan ɗaya yana kallon ɗannasa. Amin na ganin wasa mahaifinsa keyi, saidai yaga ya shafe awa ɗaya curr Abby bai motsa ba kuma idanunsa ƙyam akansa. Wani irin zufa ya haɗa ga fitsari daya matseshi kamar zai fasa masa mara. Duk wani motsi da Abby na lura dashi amma bai ce komai ba, yau yanaso ne idan jikinsa ya faɗa masa gobe babu inda zashi. Saida ya ɗau awa biyu da rabi, by this time Amin kuka yake harda majina yana roƙon Abby yayi haquri, hannunsa rawa yake gashi Abby na rikeda dorina yaƙi barinsa ya aje stool ɗin. Jin kukansa yasa Ammi fitowa daga ɗakinta, ko damunta abun baiyi ba dan wai ana hukunta Amin, dama kullum addu'ar ta kenan Allah ya hadashi da Mahaifinsa. Amin na ganin Ammi ya saki wani kukan yace "Ammi kibawa Abby haquri, wlh bazan ƙara ba. Na tuba" bai ƙarasa ba Abby yace "nabi tuba da gudu ba wando, ko kayi shiru ko ka kwana awurinnan ahaka kuma kasan zan aika, nonsense kawai" tsit yayi baice komai ba. Stool ɗin Abby ya cire yace masa ya miƙe ya bashi wuri. Kasa sauke hannunsa yayi saboda wani irin tsami dayayi ya ƙame wuri ɗaya, yana kuka yana haurawa sama har ya kai bakin ɗakinsa ya shige. Kallon ƙofan dakin Abby yayi ya girgiza kai yace "Allah ya shirya". 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Muna kwance saman katifa dake malale aƙasan dakin, nida Ameera muna kwance saman kirjin innati tana shafa kanmu, can na ɗago kaina na kalli Innati nace "Innati yanzu bazamu koma Adamawa ba"? Ajiyar zuciya Innati tayi" toh Aneesa yau ko mun koma garinnan wa mukedashi, gara muzauna anan mu gina rayuwarmu daga tushe inda babu wadda ya shaida mu. Addu'a nake ma kada Allah ya ƙara nuna mun koda mai kamada wannan ahalin" bakina bai iya shiru ba saida na ƙara cewa "toh Innati wai ina ahalinki suke, kullum idan muka tambayeki sai ki share maganar" wannan karon kam Innati kasa cewa komai tayi, ita ma ai batasan inda ahalinnata suke ba. Baba Mariya uwar goyonta dai tace mata itadin ƴar tsuntuwa ce kuma su kansu basusan inda ahalinta suke ba. Idan Allah yayi zasu haɗu toh idan kuma ba haka ba Allah ya zaba musu mafi alkhairi arayuwarsu itada ƴaƴanta. Suna cikin tunaninnan Ameera tace "Ya Aneesa ranan da ina dawowa gida da yamma naga wasu motoci masu kyau sun jero akan titi, wai naji wasu mutane suna cewa ai shine shugaban inda ake kama manya manyan ɓarayin ƙasa, bakiganshi ba wlh, kamar Balarabe fari sosai kuma kyakkyawa, kinsan gashinsa ma tsayi dashi har saida ya tufke shi. Amma fa baya dariya idanunsa karr akan titi ko kallon gefensa bayayi. Da alama baida fara'a ko kaɗan" tsaki Aneesa taja tace "Innati dan Allah ki cewa yarinyar nan tayi shiru, kina wani bani labari saikace nace miki ina so naji. Toh ni bari kiji farin namiji kwata kwata bashi a lissafina, kuma banason namijin daya cika kyau, duk da bansan shi ba kuma bansan ko zan taba haduwa dashi ba amma haka kawai naji banayinshi tunda ya cika kyau.....🙆🙆 Like Comment And share fisabilillah 🙏 🙏🙏 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 21_25 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Mainoma Mansion Ƙarfe ukun dare yadda MJ yaga rana haka yaga dare, zazzabine bana wasa ba ya rufeshi, gashi ya haɗa uban zufa amma kuma yana cikin bargo sai rawan sanyi yake. Kamar cikin hallucination (zafin ciwo) yake kiran "Neehal, Neehal, Neehal", can kuma sai jikinsa ya sake, kansa kuma ya sara lokaci guda. Cikeda son karfafa kansa ya mike ya jingina bayansa da headboard din gadonsa, pillow ɗinsa ya ɗauka ya runguma akirjinsa yana sakin ajiyar zuciya kamar wadda yayi tseren gudu da wani. This is his greatest nightmare that nobody knows up until today. Shi kaɗai yasan meke damunsa, amma Allah kaɗai yasan mafuta. Kunna side lamp din gadon yayi ya mike yana tangarda adaddafe yakai ƙofan bathroom dinsa ya shiga. Tubewa yayi dagashi sai wandonsa na Bacci three quarter ya kunna wa kansa shower ɗin ruwan sanyi, hannunsa bibbiyu adafe da bango. Ruwan na dukan fatar jikinsa yana jinshi har cikin ƙashinsa, yakai ten minutes ahaka sannan ya kashe showern ya tuɓe wandon yaɗora towel. Alwala yayi ya sanya jallabiya milk colour ya fito. Still ba ƙaramin ciwo kannasa keyi masa ba, sallaya ya shimfida ya fara sallan nafila duk azaune saboda jikinsa ba ƙwari. Bai yi ƙasa aguiwa ba, bayan ya idar yafara tilawan Al Kur'ani har yaji anfara kiran Sallan asuba. Ganin dai har yanzu jikinsa bawani ƙwari ne sosai dashi ba kawai ya yi sallan anan ɗakinnnasa. Yana idarwa bacci ya fara fuzgarsa, miƙewa yayi ya koma kan gadonsa ya kashe wutan daƙin. Minti kaɗan bacci yayi awon gaba dashi. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Karfe takwas na safe Hajja tafito falo ta zauna saman cushion dinta na alfarma, taci kwalliyan leshi maroon colour wadda ya ƙara fitar da zallan hasken fatarta na buzaye, an kafa wannan dankwalin one side ita adole ta dage tayi ɗauri me kyau kenan. Falon ƙal ƙal dashi ko ina sai tashin ƙamshin turaren wuta yake. Mai aikinta ne ta fito daga kitchen da tray ahannunta wadda yaji kayan alfarma na karin kumallo, tun daga nesa take zabgawa Hajja wani uban harara kamar zata balle idon waje. Tana ajewa saman center table ta juya zata tafi taji Hajja ta kira sunanta tace "ke ladidi, wa kika aje dazai serving ɗina" kamar wata sa'arta wacce aka kira da Ladidi tajuya tana cunno katon bakinta gaba,cikin zallan rashin ɗa'a tace "to ke Hajja bakida hannune da kullum saina zuba miki abinci, ku masu kuɗinnan..." Bata rufe baki ba sakamakon wani irin mari dataji an ɗauketa dashi wadda yasata zubewa aƙasa warwas gefen bakinta na fidda jini. Yana tsaye yasha wankan ƙananan kaya riga da wando three quarter farare masu kyau sai tashin ƙamshi yake, fuskarnan amurtuƙe babu ko annuri, amma da kallonsa kasan yaɗanyi rama saboda zazzabin dayayi jiya da daddare. Tun kafin Ladidi ta miƙe yaƙara sa ƙafa ya mauje bakin yarinya. Sandan da Hajja ke dogara wa ya dauka ya dinga ƙwala mata aduk wani gefen ɗaya samu ajikinta sai ji kake ƙwal ƙwal yana dukan ƙashin kafarta dana hannu. Hajja dake zaune sai dariya take tiƙawa kamar anyi mata bushara da aljanna. Sosai ransa ya ɓaci da attitude din da mai aikin tanunawa kakarsa. Dan ganin kansa ya ƙyaleta sannan yasa sojoji sukayi waje da ita bayan yabata saƙon sallama daga aiki. Zama yayi kusada Hajja ya kama kansa hannu bibbiyu yanaji kamar zai tsage gida biyu. Kannasa Hajja takama tace "Babana lafiya kuwa. Tun jiya ban ganka ba, yau kuwa kazo kamar baka da lafiya. Menene" girgiza kai yayi alamun babu komai. Kwanciya yayi ya mike kansa akan cinyarta, voice dinsa so low yace "Hajja kisa Abby ya canza miki mai aiki, kuma ban yarda aƙara kawo miki wata mara kunya ba" murmushi Hajja tayi, shiyasa duk cikin jikokin ta suka fi shaƙuwa da Mujahid, yafi su nuna mata kulawa kodan itace ta raineshi. Abincin dake gabanta ta ɗeba a plate sannan ta miƙar dashi tace lallai sai yaci, duk da baida wani appetite amma tunda yasamu kakartasa tana shagwaba shi yasa ya zauna tana bashi abaki, bayan yayi sosai ta ɗauko maganin ciwon kai taɓashi yasha. Wunin ranan a part din Goggo yayi, sallah kawai ke fitar dashi. Da yamma da Abby yazo wurinta ta sanar dashi ta kori mai aikinta acanzo mata wata. Bai yi mamakin haka ba tunda ɗan gaban goshinta nagari sai duk abinda yafaɗa. To yanzu a ina zai samowa Hajja mai aiki, wani tunani ne ya faɗo masa shikaɗai yayi murmushi. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Washe gari da karfe goma,mun gama ƴan ayyukan da baza'a rasa ba, Innati ta girka mana yar jalop din taliyar Hausa ƴar murji mukaci, muna cikin hira mukaji siren din sojoji alamar babbansu ya shigo. Da sauri na miƙe zuwa window na leƙa, aikuwa irin motar mutumin nan ne daya taimaka mana, da sauri na dawo na zauna nace "Innati shine wlh, Allah yasa mu haɗu dashi sai nayi masa godiyan taimakon mu dayayi. Ashe dai har yanzu akwai na Allah a duniya. Ban gama rufe baki ba naji kwankwasa aƙofar part din namu. Cikeda mamaki muke kallon juna, hijabi na na sanya na mike naje wurin kofar na bude. Yana tsaye sai sakin murmushi yake fuskarsa kamar gonar auduga. Yau kam babu kakin sojoji ajikinsa manyan kaya ne kaftan riga da wando. Dattakonsa ya kara bayyana sai wani haske da kyalli yake. Daga bayana naji Innati na cewa "Jamma wanene"? To wa zance mata, ban gama rufe baki ba naji mutumin yace "wani bawan Allah ne" wuff Innati ta miƙe jin muryan mutumin daya taimaki rayuwarsu. Ameera na kwance bisa carpet itama tayi saurin mikewa ta zauna. Abby kuwa jiyake kamar yazo gidan wani nasa, jin muryan Innati ba ƙaramin daɗi yayi masa ba. Itada ƴaƴanta sunyi matuƙar burgesa. Ina tsaye kamar me jiran umurni naji Innati tace "Jamma basu hanya su shigo mana, kin tsaya abakin kofa saikace matar soja" Abby yayi murmushi yace "a'a wannan matar Babban mutum ce ba soja ba" cikin rashin fahimtar abinda ya faɗa na matsa gefe ina sosa kaina kamar mai ƙwarƙwata. Zama Abby yayi kan carpet ya tankwashe ƙafarsa kamar wadda zaici tuwo. Innati duk ta rasa dame zata tarbesu dan babu komai agidan. Kallon mutumin yayi yace "ƴata zoki zauna akwai maganar danake so muyi daku ne", bayan na zauna ya kallemubɗaya bayan ɗaya yacewa Innati "dan Allah idan bazaku damu ba ina so naji labarin ku. Bazai yi kyau na aje mutane agida haka kawai bayan kuma bansan daga ina kuke ba" gyaɗa kai Innati tayi, saida ta ɗau kusan mintina biyu sannan tafara magana kamar mai shirin yin kuka. Gaba daya labarinmu tabawa wannan bawan Allahn,harda rashin imanin da aka aikatawa Ameera. Jikinsa ne yayi sanyi sosai har kwalla ya zubar, irin rashin imaninnan a wannan zamanin, saikace wasu bayi. Tun yaushe aka daina irin rashin imanin nan na gidan miji, shi a tunaninsa yanzu mata idonsu ya beɗe da zasu iya ɗaukan mataki akan tauye musu hakki da mazajensu keyi. Take yaji wani irin tausayinsu ya mamaye zuciyarsa. Duk yadda zaiyi saiya inganta rayuwar wannan bayin Allahn, saiya sanya su farin cikin dahar su mutu bazasuu mance ba. Kallon Aneesa yayi yace "ƴata zaki yarda kibini gidana ki zauna tareda mahaifiyata amatsayin abokiyar fira"? Wani irin dammm naji zuciyata ta bada, zama agidan sojoji cab din janjan, ba'a haife kamata koba, bazan bari inje nafara shan horo hannun wannan marasa imanin ba kaiii. Kamar kuwa yasan abinda nake tunani yace "kar ki damu indai sojojina ne, bazasuu shiga hurumin ki ba matsayin kema baki shiga tasu ba" kallon Innati yayi yace "baiwar Allah ina neman alfarmar kibani ƴarki na kaita gidana, mahaifiyata tana buqatar wacce zatana taimaka mata da wasu abubuwan saboda halin tsufa. Kamar Innati bazatayi magana ba, har addu'a nake Allah yasa tace bata amince ba. Itako Innati gani take idan taki barayi masa adalci ba, ai wadda ya taimake ka shima yaci kayi masa wani Alkhairi matsayin bai fi ƙarfinka ba. Abby ma addu'a yake Allah yasa ta yarda, ajiyar zuciya Innati tayi tace "badamuwa Alhaji, na amince. Allah yasa hakan shi yafi Alkhairi" hamdala Abby yayi yace "Nagode sosai sosai ƙanwata" wani irin dammm zuciyar Innati yayi, ƙanwata kuma, saikuma ta tuna kila yafaɗa ne kawai batareda wata ma'ana ba. Nikam na cika fammm kamar wacce aka activating da yeast, tsakani da Allah ni banaso naje ko ina, yanzu duk daddaɗan labaran da Innati ke bamu kullum zauna wuce ni saidai suyi hira itada Ameera, gaskiya ƙwararta za'ayi. Haɗa ido mukayi da Innati ta harareni alamar ko na sake fuska ko in gamu da fushinta. Kallon agogon Abby yayi,akwai inda zai tafi karya makara yacewa innati ahado mun kayana saimu tafi tare. Kamani Innati tayi muka shiga ɗaki Ameera ma tabi bayanmu, muna shigowa na fashe da kuka ina bubbuga ƙafata aƙasa ni alambaram babu inda zani, rungumeni innati tayi tana rarrashina harna samu nayi shiru, sosai tayi mun nasiha saikace wacce za'akai gidan miji. Bamu ɓata lokaci ba muka fito hannuna cikinna Ameera dake matso kwalla itama. Bayan nayi sallama dasu, bawan Allahn yace wa Innati gobe da yardar Allah zai aiko aje ayiwa Ameera registration na makaranta saita fara zuwa. Kuma ya bata maƙudan kudade masu tsoka yace asiya kayan abinci da na sawa. Atake naji ɓacin raina ya kau, farin ciki ya mamaye ni. Gaskiya wannan mutumin saƙo ne daga Allah. Muna fitowa, mota ɗaya muka shiga dashi. Mutanin wurin sunata leƙowa, to wai su wannan wasu mutanene da Jenar ya kawo gidan ya aje sai wani tarairaya akeyi musu. Wasu dasukayi shekara a estate dinnan koda bakin ƙofarsu Jenar bai taɓa zuwa ba amma su wannan mutanin jiya jiya kawai gashi dakansa ya tako har inda suke. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Muna tafiya amota sai kallon hanya nake, gaskiya Kano ta haɗu, irin wannan titin kamar ba'a Nigeria ba, wanan ka bace agarin saidai ayi wanin ka kuma. Wani dogon titi naga mun ɓullo, bamu jima ba naga anyi parking gaban wani tangamemem gate mai uban tsayi bama a ganin gidan dake ciki daga waje. Sojoji guda uku ne suka buɗe gate ɗin tsabar girmansa. Baki awangale nake kallon fulawowin dasukayi mana sannu da zuwa kaloli daban daban sai tashin ƙamshi sukeyi gwanin sha'awa. Ga wani wuri da aka zagaye da bangon ragaraga, su agwagi suna shawagi acikin wani kwamin ruwa mai hasken gaske, agwaginma ban taɓa ganin irinsu ba, ko tabon datti babu ajikinsu farare tas tas dasu, ga wasu ɗawisu guda uku suna kwance masu kyan gaske,guda ɗaya kuma yana tsaye ya buɗe fukafukinsa masu kaloli dayawa. Abubuwa dayawa nagani wasu ma bansan sunayensu ba. Muna wuce wurin naƙara ganin wani wuri kuma shikuma an mamayeshi da glass ne, ashe lambu ne na kayan itatuwa masu kyau wayyo Allah. Tsakiyan wurin naga wani abu kamar tulu amma a tsaye ne ruwa na zubowa, ga wasu kujeru anjera agefe da gefen wurin na shan iska. Harma hangoni awurin na zauna inacin ayaba da lemu kai kuɗi yayi arayuwa jama'a. Toni wai har yanzu tafiyan bai isa bane, kodai nan gidan gona ne, banga gidaje ba har yanzu. Ina juyowa ɗayan gefen kawai naga abinda yasani kasa rufe bakina. Ginine ƙaton gaske atsakiya mai hawa biyu wadda gaba ɗayansa glass ne gaban gidan. Wannan tulun da nace nagani ɗazu abaya ashe ma karami ne, wannan wani baban tulunne shima atsaye yake sai kwararo ruwa yake shaaa. Gefe da gefen ginin kuma suma part part ne na gidan sama suma amma basu kai na tsakiyan girma ba. Wannan kodai tafiyan damukayi bacci nayi bansani ba har muka ƙetare zuwa kasan waje, dan bazan taɓa yarda cewa wannan aƙasa Najeriya take ba. To idan kasa Najeriya take, mu da a ina muka zauna, kenan adaji muke rayuwa da ashe. Masu aiki ne keta shawagi a tsakar gidan, duk suna sanye da uniform, ga sojoji suma sai kai kawo suke da manya manyan bindigogi ahannunsu. Makwat na haɗiye wani yawu ɗaya tsaya abakina yaƙi wucewa,ai ina ganin yau dana shiga gidannan to bana ƙara fitowa dan karma nahada hanya da samudawannan. Agaban wannan tangamemen gini motocin suka faka lokaci guda. Bude mana kofa akayi, na fito ta ɗayan gefen inata kalle lalle sai juya wuya nake kamar zan ɓallata. Hatta kasan danake tsaye akai ba ciminti bane, wani irin tile ne mai hasken gaske ƙal ƙal kamar ba'a takawa. Nayi nisa akalle kalle naji ankirani, juyawa nayi naga bawan Allahn ne yayi magana, murmushi nayi nabi bayansa muka fara tafiya. Da sallama abakina muka shigo wani ƙaton falo dayaji kayan duniya na alfarma, ko ina sai tashin ƙamshin turaren wuta yake, ga kuma sanyin wani na'ura na turawa (Ac). Babu kowa a falon sai TV dake aiki, tangamemen TVn nake kallo wadda kusan ya cinye rabin bangon. Zama nayi kasan tiles din dan tsoro nake kada na zauna saman carpet ace nayi datti dashi. Kunsan masu kuɗinnan da kyankyamin talakawa. Abby ne ya haura sama ɗakin Hajja dan sanar da ita cewa ya samo mata mai aiki. Tsohuwar tana zaune bakin gadonta tana ninke kayanta da aka kawo daga wurin wanki tunda babu maiyi mata. Ganin ɗannata yasa ta aje kayan, zama Abby yayi kusada ita yace "Hajjata na samo miki abokiyar fira" cikeda murna Hajja tace "dan Allah, har ansamo wata kenan. Allah dai yasa ba halinta ɗaya da wannan hegiya mai zubin sandan raken ba"😂. Miƙewa tayi ta ɗau sandarta Abby ya kamo hannunta suka fito tare. Ina nan zaune aƙasa, duk mutanin dasuka fito sai sun kalleni sun ƙara, da har tunani nake kodai kashine ajikina aketa kallona, duk sainaji na tsargu na fara kame kame. Wani irin sanyi nake ji kamar ina cikin ƙanƙara, abunka da bansansaba ba. Har su Hajja suka sauko idanunta nakan yarinyar dake zaune, sotake tag fuskarta amma yarinyar ta duƙe kanta aƙasa. Zama tayi kan cushion tace " baiwar Allah ke kam meyasa zaki zauna aƙasa, hala dai daga ƙauye kika fito, idan ba haka ba ga carpet kika gwammace ki zauna aƙasa"? Ɗagowa nayi na kalli inda matar ke zaune, daram daram daram naji azuciyata, nafara ambaton sunan Allah ina yi ina ƙarawa. Wlhi babu abinda matar ta rage Innatina dashi saidai kawai ta nuna mata tsufa. Komai na su iri ɗaya sak, hasken fatar duk da wannan kam kuɗi sun zaunu dan haka ta fi innati haske shima ɗin ba sosai ba. Yanayin fuskarsu iri ɗaya, yalwan gashin kan innati sak irinna matar saboda ya fito ta ƙasan danƙwalinta kuma yanada tsawo har gadon bayanta. Hancinsu, kai komai ma kawai iri ɗaya ne. Meke faruwa? Na tambayi kaina acikin azuciyata. Hajja itama ta ƙurawa Aneesa ido kamar taga cele, sai ƙarewa yarinyar kallo take tun daga kai har ƙafa. Hannunta ta kalla, yatsunta zara zara irinna Nadeen ɗinta data ɓace shekaru aro aro, saidai wannan tagirme mata sosai ma. Haka kawai taji yarinyar ta kwanta mata arai. Abby dake zaune yaga anshareshi sai kallon kallo aketayiwa juna kamar da can sun san juna. Gyaran murya yayi yace "Hajja kinga ta, tayi miki"? Kallon Abby Hajja tayi tace "a ina ka samo yarnan ɗan Isa"? Murmushi yayi yace "can cikin garin Kano Hajja, kin tuna jiya nabaki labarin wasu bayin Allah dana taimakawa na basu gida a estate ɗina, to wannan ƴar matar ce" gyada kai Hajja tayi tace "aiko badamuwa, tayi mun. Allah yasa mu kyautatawa juna" kallon Aneesa tayi da ta sunkuyar dakai yanzu tana ayyana wasu abubuwa aranta tace "ke zo nan " kamar wacce aka zarewa laƙa ajiki ta taso ahankali tazo inda Hajja ke zaune ta zauna daidai ƙafafunta " ya sunanki" Hajja ta tambayeta, kai aƙasa tace "sunana Jamma Hajiya" cikin rashin fahimta tace "Jamma kuma? Ainihin sunan ki kenan? Girgiza kai tayi tace "a'a sunana Aneesa" wani irin fara'a ne yazowa Hajja, yau akaron farko taji mai sunanta, hannunta ta ɗora saman kan Aneesa tace "Masha Allah, ashe ma dai takwarata ce, aiko zan riƙa kiranki takwara", murmushi nayi inajin wani daɗi na ratsa ni. Allah sarki rayuwa, ga wata tsohuwa wacce ta isa ta zama kakata tana nunamun kula, amma wacce nakeda ita ta tsaneni kamar yadda ta tsani mutuwarta. Mikewa Abby yayi ya sallamesu dan akwai inda zai tafi mai muhimmanci. Wata daga cikin ƴan aiki Hajja takira tace da ita "ina so abawa taƙwarata ɗaki mai kyau anan cikin sashi na ba staff quarters ba. Ita ɗin taƙwarata ce dan haka komai nata dabanne. Kuma baza'a bata uniform ba, dan ita bamai aikina bace. Ankawo mun itane don ta tayani kauda kaɗaici" gyada kai matar tayi tace mun "ƴata biyoni kizo muje na nuna miki ɗakinki", har suka tafi Hajja na kallon Aneesa, tana ayyana irin kyawun yarinyar. Wani ɗaki matar ta kaini. Duk na kasa rufe baki saboda girman ɗakin da kuma haɗuwarsa. Kai nidai inata ƙara maimaitawa kuɗi yayi ne kawai arayuwa. Saida ta nuna mun komai da kuma yadda ake amfani da abubuwa a bayin sannan tafito. Zama nayi akan lallausan madaidaicin gadon ina ƙara godewa Allah araina. Inama su Innati sunanan tareda ni, take naji hawaye yazo mun. Ban taɓa nisa da mahaifiyata ba sai yau, Allah ya kareni daga sharrin duk mai nufina agidannan da sharri. Wannan addu'ar sunayi, na miƙe na shige bayi nayi alwala sannan na fito, banga sallaya ba dan haka na shimfida ɗankwali na nafara sallan nafila ina godewa Allah daya amshi addu'an mu kuma ya karemu daga ƙasƙanci da wulaƙanci. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Yau tun safe ko ruwa basusa abakinsu ba. Goggo duk abun duniya ya isheta, gashi babu mai ɗebo musu ruwa balle suyi wanka har ayi wani abun. Abba ma ko fita baiyi ba, suna zaune su biyun a tsakar gida dagashi har mahaifiyar tasa babu mai cewa juna uffam. Abba yaje gidansu Abu jiya da safe yayiwa mahaifinta bayani akan jarabawar data sameshi, sai dai me. Mahaifin Abu yace idan bai kawo kuɗin nan da kwana biyu ba , zai bawa wani dama tunda Abu tanada manema dayawa. Duk abun duniya sun haɗe masa wuri guda. Sai Allah ya isa mara amfani yakewa Hussaina. Ya kira Baba Auwalu waiko yaji cewa Innati tana gidansa danyasashi ya turke masa ita har sai yazo Kano tabashi kuɗinsa amma mummunan labarin da Baba Auwalu yabashi shi ya sanya shi ji kamar ya sa hannu akai yayita ihu. Shikenan reshe ta juya da mujiya. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Har bayan sallan isha'i ba'a nemeni ba, matar nan data nuna mun dakina itace ta kuma kawo mun hadadden abinci naci na ƙoshi. Har nayi Sallah naji gaba ɗaya zaman ɗakin ya isheni. Hijabi na sanya na fito inata ƙara kallon falon. Yanzu tunda darene ankunna kowani fitila mai haske kaloli dayawa. Bayan mutum na hango yana zaune akan cushion kamar abu yakeyi. Abun daya bani mamaki shine, gashi dai alamu sun nuna cewa namiji ne azaune amma kuma sainaga wani tulun gashi daya tara tsakiyar kai ya kamashi da rubber ring, abun daya bani sha'awa da gashin shine gashi baki sidik sai wani sheƙi yake yi. Fatar wuyansa danake hangowa fari sol, da alama dai mutumin farine sosai. Cikin sanɗa nake tafiya wai don kar yaji takun ƙafata, har na iso ta bayansa ina leƙowa ahankali, da sajensa na fara cin karo mai kyan gaske, yana kwance luff Kan farar fatarsa, gashin idonsa zara zara kamar na mata. Laɓɓan bakinsa jaa zur kamar ya shafa jambaki. Duk da gargaɗi na da zuciyata keyi bai hanani karasowa ba, laptop ne kan cinyarsa sai typing yake cikin kwarewa. Tun fitowar ta yaji ƙaran kofa amma bai damu daya juya koya ɗago ba tunda yasan ba Hajja bace, ɗakin Hajja na sama ne. Kwata kwata hankalinsa bai bashi ba har ta iso wurin, tsaye take a kan carpet tanata leƙo fuskarsa kamar an aikota. Cikin ladabi tafara gaidashi tana daɗa leƙo fuskartasa. Sarai yaji gaisuwannata amma ya share, yasan mai aiki ce. Kuma insuka gaidashi ba amsawa yakeyi ba shiyasa baima kalleta ba. Har baki uku tana gaidashi amma bai amsa ba, ganin hakan tayi kamar wulaƙanci, batasan lokacin data saki wani dogon tsaki da har ya sanya shi ɗagowa dan yaga wacce mara kunyar ce that dares to hiss at him. Dammmmm taji kirjinta ya buga a lokacin dasuka haɗa ido dashi. Sharp golden brown sexy eyes ɗinsa directly acikin nata...... Tofa Star da Star sun haɗu, babban magana. Muje zuwa💃💃 Like Comment And share fisabilillah 🙏🙏 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 26_30 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Dammmmm taji kirjinta ya buga a lokacin dasuka haɗa ido dashi. Sharp golden brown sexy eyes ɗinsa directly acikin nata. Tun daga sama har ƙasa yake kallonta kamar yaga kashi, ko minti ɗaya baiyi ba da kallonnata ya maida kansa kan system ɗinsa yacigaba da aiki. Ganin haka yasa Aneesa tayi tunanin baiji abinda tayi ba. Ƙara kallonsa tayi ta taɓe baki tace "yanzu waifa hala zai ce ƙyansa ne ke ruɗarsa, to ina wani kyau anan. Mutum sai fari kamar wani aljani, ana gaidaka kana matse fuska. Kanka akeji". Wannan karon kam tsantsan bacin raine afuskarsa, wace wannan daga ina ta fito da har rashin kunyarta yakai ta tsaya tayi maganan banza agabansa abinda ko ƙannensa basu isa suyi ba. Juyawa nayi zan tafi naji an ɗamko dantsen hannuna, suuuu naji zuciya ta tsinke. A hankali na juya ina tsoron karr naji saukan abu afuskata dan haka nayi saurin kareta. Iya kirjinsa kawai nake kallo tsaban tsayin dayake dashi. Yadda ya matse hannuna kamar zai karya yasa na saki ƙara ina ƙoƙarin kwace kaina amma ina saima ƙara damƙe hannun nawa dayayi. Wannan kuma wani mugu ne daga ina ya fito. Tsabar mugunta dake cinsa aciki yasa ya murɗa hannunta sai ji kake kas karan Kashi ya goce, wani irin razanannen ƙara ta saki hawaye yafara Zarya a idanunta. Har wani ciza jan labbansa yake yi yana ƙara kaimi a abinda yake. Juya hannun nata yayi zuwa bayanta ya murɗa da kyau,sannan ya kama gemunta ya ɗago fuskarta tana kallonsa face to face, ga matse mata baki dayayi ga hannunta datakeji kamar zai balla. Idonsa abin tsorone, ga tsarin jikinsa ma kaman na mutanin da. Take taji wani irin kafirin tsoronsa ya ɗarsu a zuciyarta. Gani nake kamar kasheni zaiyi dan babu alaman tausayi a fuskar tasa. Bakina na rawa cikin hannunsa daya damƙe nafara furta "dan Allah kayi haquri, wlh bazan sake yima tsaki ba" kafafuna dake rawa inaji kamar fitsari yanaso ya fito. Muryar Hajja naji tana magana daga bene tana cewa "Babana banda wannan, wlh babu abinda tayi mun. Sake mun takwarata ban yarda da wannan cin zalin ba" rufe ido nayi ƙyam ina godewa Allah daya kawo Hajja dabansan inda zan kwana yau ba, a duniya ko a kabari na. Badon yaso ba ya hurgata kasan kafet ta fadi,wani irin kallon "don't try to mess with me next time yayi mata" sannan ya ɗau laptop ɗinsa yana mai barin part din gaba daya. Kuka na na cigaba dashi ina kiran Innati. Hajja dake tsaye akaina tace "tashi takwara kukan ya isa. Ince dai bai targaɗa ki ba. Kai wannan yaro da wiyan sha'ani yake, yau yau akawo minke yazo ya hallaƙa ki, tashi abunki yi shiru ki daina kuka. Zona duba miki hannun, Allah yasa ba targaɗe. Irin wannan kamun ai sai hannun mutum ya ƙarye ma gaba ɗaya" mikewa nayi da ƙyar ina jan majina ahancina tsabar kuka. Hannuna Hajja takama tana dubawa, saida ta tabbata babu komai sannan tace inje in kwanta tayi mun saida safe. Ina shiga ɗakina na kwanta saman gado, wani sabon kukan na fara ina kiran Innati kuma ina yiwa wannan mutumin Allah ya isa, kawai zai zo ya rage mun farashi rana tsaka. Duk da kukan danakeyi bai hana nace "Allah ya isa, shiyasa na tsani mutumin daya cika kyau ai, kalleshi kamar farin rago", ahaka na kwana ina jinyan hannuna har bacci ya ɗaukeni. Washe gari ƙarfe bakwai na farka na gyara ɗakina kuma nayi wanka. Baba Larai wannan matar data nuna mun dakina ta kawo mun kaya tace na sa Hajja ce tace akawomin. Kayan kuwa das ya zauna mun saikace dama domin ni akayishi. Dogon gashina wadda yake har ƙasan duwawu na na kama na tufke, gashin duk ya isheni da tsami saboda rashin wanki da baya samu akai akai. Ni a kullum mamakin gashina nakeyi, tsawonsa yafina Innati gashi dark brown ne bakamar na innati ba wadda yake baƙi sosai. Kallon kaina nake agaban mirror ina ayyana yadda zanyi jiki idan nayi kuɗi, gaba ɗaya ƙashin wuyana awaje yake kamar azuba ruwa kuma ya zauna. Ni ɗin siririya ce kuma inada tsayi ɗan daidai bamai yawa ba, to wai Ni danake da tsayi amma saida na raina kaina gaban wancan mugun mutumin, tsawo ne dashi kamar fal waya. Ƙirjina na kalla, aduk lokacin danake wanka ni kaina kunyar kaina nake ji saboda yadda abubuwan suke acike babu rama ko kaɗan aciki, lafaffen cikina nabida kallo, zanso na ga yadda zan zama idan nayi ciki. A hankali na juya na kalli duwawu na wadda gashina ya rufe, ɗan ja nayi da gashin na kalli tudun sa, wayyo Allah na furta ina rufe fuskata. Da ƙirjina da duwawu na dukkansu babu alamun rama a cikinsu, ga wani bajajjen ƙuguna wadda yakeda faɗi Masha Allah. Wani lokacin a gida idan ina tafiya sai Goggo tariƙa cewa ina juya su ne da niyya dan naga inada wadatar su. Knocking naji aƙofar dakin dan haka nayi sauri nasa hijabina. Baba Larai ce atsaye abakin Kofar tace mun Hajja ce ke nemana. Ina riƙeda hannun targaɗena na fito ina biyeda Baba Larai abaya. Muna zuwa falon na samu Hajja na karyawa. Zama nayi kusada ƙafarta na gaida ita cikeda ladabi, inajin son matar sosai cikin raina. Kallon ta Hajja tayi fuskarta daukeda murmushi tace "takwara har kin farka abaccin, in ce dai babu abinda keyi miki ciwo kuma ko"? Gyaɗa kai nayi, abincin dake gabanta na mike na fara zuba mata a plate, sannan na miƙa mata, zama nayi nafara yi mata tausa a ƙafa. Munyi hira sosai, Hajja badai iya bada labari ba, niko sai dariya nake tiƙawa kamar zararriya. Da gudu Raihanah da Mustapha suka shigo ko sallama babu suna kiran sunan Hajja, kaman motoci haka suka ja birki suka tsaya suna kallon yadda Hajja da wata baƙuwa suka zauna sai dariya sukeyi harda tafa hannu. Kallon Raihanah Mustapha yayi yace " sis, idona suna gane mun gaskiya ne kuwa. Yau Hajja ce ke hira harda dariya da mai aikinta, lallai wannan kam tazo da Sa'a" Raihanah tace "Musty kalli yarinyar, mai kyau da ita wlh kamar ba mai aiki ba. Hancinta ma yafi nawa tsayi, a ina Hajja tasamo ta" "excuse me" sukaji anyi magana daga bayansu, da sauri suka matsa sun san wanene yayi maganan. Sanye yake cikin dakakkiyar suit ox blood, jacket din suit din na hannunsa ya riƙe, ga wani spec daya kafa a idanunsa fuskarnan gumm kamar anyi masa bushara da mutuwarsa. Wani irin sihirtaccen kamshine ke fita daga kowani sassa na jikinsa. He's so damn hot 🥵 Shi kansa mamaki yake yadda Hajja bata masan da shigowarsa ba, wannan insolent gurl ɗin duk ta dauke mata hankali. Zama yayi acushion din dake facing ɗinsu ko uffam baice ba, ga kuma time ɗin tafiyarsa nata matsowa. Kallon agogonsa yayi, guntun tsaki yaja cikin zallan shagwabar da Hajja da Mamy kawai yakeyiwa yace "Hajja yunwaa" Sai yanzu na lura da mutum dake zaune ya fuskancemu. Wani irin bugawa naji zuciyata tayi, har hannuna yayi mun zummm kamar yasan wadda ke falon. Shikam ko kallo ban ishe shi ba ya maida hankali kan wayarsa yana latsawa. Hajja ta miƙe tace "bari na haɗo ma abun karinka da kaina" sannan ta wuce kitchen. Raihanah ce ta ƙaraso cikin falon ta gefensa tazo wucewa yasa mata ƙafa, sai timmm kakeji ta faɗi aƙasa, kai Babban Yaya mugune wlh. Bata fuska tayi kamar zatayi kuka tace "Babban Yaya good morning" kamar baijiba ya share ta, Mustapha ma ya shigo shima ya gaida shi, gyaɗa kai kawai yayi masa. Niko ganin ƴan gidan sun gaidashi bai kamata naƙi yi ba, zuciyata cikeda tsoronsa nace "ina kwana" kallon nan ban samu arziƙinsa a wurinsa ba, banyi ƙasa aguiwa ba naƙara maimaitawa. Ɗagowa yayi ya kalleni da sauri na dukar da kaina ƙasa ina kallon yatsuna. Wani dogon tsaki naji yaja, ba zato naji ya daka mun tsawa yace "my friend tashi kibar falonnan before I descend on you, mara galihu kawai" "mara galihu " wannan kalmar ba ƙaramin taɓani yayi ba. Ehh gaskiya ne, wannan mutumin yana ɗaya daga cikin mutanen daya kamata na fara taka tsantsan dasu matsayin inaso na zauna agidannan lafiya. Miƙewa nayi jiki asanyaye nayi hanyan ɗakina, har zan shiga naji ankamo hannuna. Juyawa nayi da sauri ina tunanin Allah yasa badai shi bane, ganin wannan yarinyar daya sawa ƙafa tafaɗi ɗazu afalon Hajja yasa na saki raina. Kamanni su ɗaya, sai dai shi ya ɗan fita haske, kuma kalar idonsu ba ɗaya bane. Murmushi ta sakar mun nima na maida mata martani. Kama hannuna tayi tace "ya sunanki, naji Hajja tace takwara, kema sunanki Aneesa ne"? Gyaɗa kai nayi. Murmushi yarinyar tayi tace "aiko nasamu ƙawa, kin burgeni wlh. Gashi kuma kamar zamuyi Sa'a tunda naga yanayin girmanmu kusan ɗaya ne" bance mata komai ba taja hannuna muka shigo ɗakina tare. Haka taita jana da hira, tun ban sake ba harna fara bata labari nima. Cikin lokaci ƙalilan muka saba da juna kamar yan uwa. 🌷🌷🌷🌷🌷 Yau jikinsa da sauƙi ba tsami kamar jiua. Tunda Abby yabashi wannan horon shekaran jiya sai yau ya samu ya fito daga part dinsu, ko sallah aɗakinsu yake yi. Amin kenan, har wani ɗan rama yayi tsabar wahala abunka da ajebo. Duk cikin yaran Abby shine mai raini gashi kuma bayaso araina shi, son girma ne dashi kamar gyambo. Yanzu haka ma Ammi ce ta tursasashi ya fito yaje ya gaida Hajja sai wani turo baki yake kamar ance yaje ya gaida kashi. Yana shiga daidai MJ Yana fitowa. Haɗuwarsa dashi ba ƙaramin tada masa hankali yayi ba, dama Babban Yaya na gida har yanzu, ohh God another palava. Yadda MJ ya zuba masa wannan shanyayyun idanun nasa kaɗai ya isa yasashi tsarguwa, duƙar dakai Amin yayi yace "Babban Yaya ina kwana" ko arziƙin kallo bai samu a wurinsa ba yace " ka shiga hankalinka Amin, duk abinda kakeyi I'm fully awared, abinda Abby yayi maka kadanne idan ka shiga hannuna, nonsense kawai " sorry kawai Amin ya ce masa ko ƙwaƙƙwaran motsi yakasayi, ko Abba baya tada masa hankali yadda MJ keyi shiyasa bama yaso ya shiga hanyarsa. Da sallama abakinsa ya shiga falon Hajja, babu kowa ko ina tsit dai tashin ƙamshi da kuma sanyin Ac. Har ya juya zai fita yaji anbuɗe ƙofar dake gefen falon. Raihanah ce agaba, sai Aneesa dake bayanta sunata dariya, galala ya tsaya yana kallon wacce ke bayar ƙanwartasa. Daga ina wannan beauty din tazo. Har wani gyara tsayuwa yayi da kyau yana ƙare mata kallo tun daga sama har ƙasa. Her way of laughing, her one sided dimple, her composure, her everything yaji sunyi mai. Duk matan dayake alaƙa dasu bai taɓa ganin macen data kwanta masa ba irin wannan. Me hakan ke nufi. Love at first sight? Ya tambayi kansa yana sakin wani shu'umin murmushi. Raihanah ce tafara ganinsa, take annurin fuskarta ya ɗauke ta gimtse fuska tamau, ko ya damu da hakan datayi tunda hankalinsa ba'a kanta yake ba. Aneesa ma ganin mutum kawai tayi atsaye yana ƙare mata kallo da wani irin excitement kwance afuskarsa. Shima yana da kyau amma bai kai waccan arrogant man ɗin ba, sunan datasa mai kenan. Cikin ɗaure fuska Raihanah tace "Ya Amin ina kwana" gyaɗa kai kawai yayi mata yana sakin murmushi, itama Aneesa gaidashi tayi batareda ta kawo komai aranta na irin kallon dayakeyi mata ba, Yoh tunda ta shigo gidannan kowa sai kallon ta yake kamar sabuwar halitta amma banda mutum ɗaya wadda kallonma bata ishe shi ba. "Morning beauty, kin kwana lafiya"? Amin ya tambayi Aneesa, sheƙeƙe Raihanah ta tsaya kallon ɗan uwannata gsky ya kamata tajawa Aneesa kunne tunda wuri, tarayya da Amin ba Alkhairi bane awurin kowacce mace illa matarsa kokuma ƴar uwarsa. Itako Aneesa maimaita sunan beauty tayi aranta, Yoh ina kyan, mutum duk yana cikin dauɗa ace masa wani beauty. Kamo hannun Aneesa Raihanah tayi suka fice daga part ɗin Hajja zata kaita wurin Mamy su gaisa. Da kallo Amin yabi bayan Aneesa, wani irin yawu ya haɗiye makwat yana kallon yadda ass ɗinta ke juyi acikin hijabi kamar dama don shi take juyasu, murmushi yayi wadda ya bayyana zallan kyawunsa yace "ohhh God, I think I've fallen for her". Cabb ɗin janjan🙄 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Convoy ne na motoci guda biyar, huɗu na sojoji ɗayan dake tsakiya kuma na shugaban EFCC ne watau Boss Mujahid Abdulazeez Mainoma. System na hannunsa yana aiki cikin kwanciyar hankali, dake idan ya koma aiki ba wani jimawa zaiyi ba saboda leave dinsa is due, Dan haka zai dawo gida cikin satinnan kuma hutunsa na tsawon wata biyu ne. Vice ɗinsa zai takeover duk wani aiki dake office ɗinsa. Dayayi aiki kaɗan sai ya runtse ido na ƴan mintina kafin ya buɗe ya cigaba. Karfe sha ɗaya suka iso birnin tarayya Abuja saboda yau ba jirgi yabi ba. Direct wurin aikinsa suka wuce. Wurine babba mai hawa goma sha biyu, fentin wurin ja ne da fari. Motoci ne birjik kota ina, ga sojoji dake kai kawo acikin harabar wurin. Ƴan jarida suna ganin motocinsa sun danno kai cikin harabar EFCC suka taso da camerorinsu, sojojin suka zagaye su suna baiwa Ogansu hanya. Fuskarsa dake cikin Black face mask yanuna cewa akwai seriousness atattare dashi. Golden eyes ɗinsa were so damn cute, ga Bluetooth din ɗaya saƙala a kunninsa ɗaya alamar waya yake yi, kwata kwata ma ba'a jin abinda yake faɗa. Agogonsa ya kalla yaga time ɗin su na board meeting saura kaɗan ga ƴan jaridannan sai matsa musu sukeyi. Ganin dai bazasuu haƙura ba saiyayi magana yasanyashi zame face mask ɗin afuskarsa yayi nuni da yatsa alamar sunada one minute suyi masa duk wata tambayar da suke so. Wata ƴar jarida mai suna yusrah tace "ƴallaɓai dan Allah Kanada mata" wani wawan kallo ya jefa mata dayasata saurin komawa baya da microphone ɗinta ahannu. Wannan irin question ɗin dama suke so su tambayeshi. Fuskarsa dake a murtuƙe kamar kullum yace "do you wish to be my wife's slave"? Shiru wurin ya dauka. Lallai Mujahid baida daɗi, irinma Ansar dazai bata kenan. Wannan yar jaridar ji tayi kamar ƙasa ta tsage ta shige cikinsa. Tasan yau kuwa zata rasa aikinta, dan wannan tambayar datayi masa kwata kwata babu shi acikin jerin tambayoyin da aka basu umurnin suyi masa, kawai anxiousness ɗinta ne yasata yin wannan tambayar. Ganin they're not serious kawai yasashi maida face mask dinsa ya juya ya barsu adaskare awurin, kalma ɗaya dayayiwa yusrah yasata jin ta tsani aikinma gaba ɗaya. Kuma they're live, kenan kowa da kowa zai gani. Board room ɗin wani ɗakine mai girman gaske dake ɗauke da round table mai cin mutane ashirin da biyar. Ga babban kujeran chairman agaba akwai wani tag inda aka rubuta sunansa "MUJAHID ABDULAZEEZ MAINOMA. EFCC CHAIRMAN" , kowa ya hallara adakin taron shi kaɗai ake jira. Yana shigowa batareda bata lokaci ba aka fara gabatar da meeting ɗin. Yawancin tattaunawansu akan yadda za'ayi faɗa da masu cin hanci da rashawa ne cikin al umma, da kuma yadda za'a kama gwamnoni da sanatoci masu sata kuɗin gwamnati suna gina gidaje a Turai, suna kashewa iyalansu bayan ga talakawa masu neman taimako, sai kuma yan yahoo masu kashewa mutane kuɗade ta hanyar da bai kamata ba. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Aɓangaren Mamy, ta karɓi Aneesa hannu bibbiyu, kwata kwata basu ɗauketa kamar mai aiki ba. Yadda Mamy taga yarinyar bata da damuwa saitaji ta burgeta matuƙa. Yanzu duk tunanin Aneesa ya su Innati, gashi batada waya balle takirasu taji ya suke. Ko ya jikin Ameera, Allah yasa babu wani damuwa. Tana wannan tunanin taji Mamy tace "ƴata yanaga kamar kina cikin damuwa, menene" ajiyar zuciya tayi tace "Hajiya ina kewar mahaifiyata ne"ɓata fuska Mamy tayi tace "Hajiya kuma, bayan keba mai aiki bace, takwarar Hajja cefa, daga yau Mamy zakina cemun yadda ƴaƴana suke kirana kinji" gyaɗa kai Aneesa tayi cikin tsantsan farin ciki. Jana Raihanah tayi zuwa ɗakinta tace muje muyi fira, baiwar Allah taƙi bari na koma wurin tsohuwa. Dake ma Hajja yanzu haka nabari tana bacci, kar kuma ta farka ne ta nemeni. Muna shiga ɗakin na tsaya baki ahangame ina kallon irin dukiyar da aka kashewa ɗakin. Komai na ɗakin pink colour ne tsarin barbie. Gawani ƙaton ƴar baby akan gadon shima pink. Zama mukayi abakin gadon Raihanah tace "ke wai ko Ustaz zaki aura ne. Tunda muke baki cire hijabi ba, sai wani noƙewa kike acikin hijabin. Dan Allah nidai cire, ai mu biyune kawai aɗakinnan" tafaɗa tana zare mun hijabi daga kaina. Gashina dana tufke ta haɗa da rubber ring ɗin ta ciresu gaba ɗaya. Salati ta saki tana kallon uban gashin dake kaina wadda ya rufemun fuskata. Hannu tasa tun daga saman kaina tana bin dogon gashin har in daya tsaya, tace "takwarar Hajja gashin ki kenan, nashiga uku. Wlh duk da inada gashi amma naki karshe ne. Dan Allah ke daga wani kasa ne" murmushi nayi nace "daga Adamawa nake. Ni ɗin Fulani ce" wani harara ta mun tace "Fulani, wlh ban yarda ba. Kalli fa, saidai gashin kawai yana buqatar gyara ne. Amma ba damuwa. Gobe zanje wurin gyaran kai, zanyiwa Hajja magana sai ku tafi tare" wani irin daɗi najiya mamayeni, alhamdulillah kaina zai samu yasha iskan ƴanci shima. Ahaka mukayita hira tana nuna mun hotuna a wayarta da videos munata dariya cikeda nishaɗi. Nayi ƙawa agidan Jenar 💃. Sai bayan sallan zuhr nakoma part ɗin Hajja, ko kaɗan bata nuna ɓacin ranta akan jimawan danayi agefen Mamy ba. Haurawa nayi zuwa ɗakinta na gyara ko ina tsaf tsaf sannan na turara ko ina. Ina saukowa ƙasa, Hajja tasa nakawo kaskon turaren wuta na turara mata gashinta. Gashinta ga tsayi ga laushi sak irinna Innati na, kodai matar nan tanada wata alaƙa da Innati ne bansani ba. Komai nasu iri ɗaya, harta muryan Hajja idan takirani sainaji kamar Innati ce ke kirana. Shaƙuwar mu da ƴan gidan yayi ƙarfi sosai cikin kwana biyu. Saidai wannan Amin ɗin, tunda Raihanah ta ja mun kunne akansa nafara taka tsantsan dashi. Yawanci idan ina falon Hajja sai yazo yayita jana da hira, duk da bawani amsa nakeyi ba. Kuma yawancin hiran tambayata yake ko inada saurayi ko kuma in akwai wadda ya taɓa cewa yana sona. To shi ina ruwansa da shiga hurumin daba masa ba. Har wani ɗan kumatu naga nayi cikin kwana biyun nan, kuma godiyata da Allah ban ƙara ganin wannan arrogant man ɗin ba. Allah yasa ma karna kara haɗuwa dashi, halinsa sam baiyi ba. Mutum yayita tamƙe fuska kamar wani sa. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Innati da Ameera ba'a cewa komai sai hamdala. Gidansu an wadata shi da komai najin daɗin rayuwa daidai gwargwaɗo. Ga Ameera harta fara zuwa makaranta inda take SS one a wani private school. Innati kuma ta kama sana'a na saƙa, dama Allah yabata basira a wannan fannin. Tana saƙan kayan sanyi masu kyau na yara jarirai kuma ba laifi ana siya saboda yanzu lokacin sanyi ne. Sunyi wani fes dasu kamar basu taɓa shan wahalar rayuwa ba. Ɗan ƙaramin wayar itel Innati ta siya da niyyar duk lokacin da Jenar yaƙara zuwa gidan, zata amshi numbern uwar ɗakin Aneesa su riƙa gaisawa da yartata. Ba ƙaramin kewarta sukeyi ba. Ko tana wani hali agidan Allah kaɗai yasani, itadai addu'ar ta a kullum shine Allah ya kare mata ƴaƴanta daga sharrin maza. Ɗaya ta riga ta faɗa, Allah ya tsare mata ɗayan. Ameera kam jiki ya warke sosai. Tana shan magunguna masu kyau da inganci wadda asibitin da Abby yasa akaita suka ɗorata akai. Saidai tana ta tsammanin ganin baƙon watarta yau sati ɗaya kenan da wucewar lokacin daya kamata yazo. Bata kawo komai ranta ba yacigaba da ɗaukan rayuwa yadda yazo mata, kuma a kullum addu'a take Allah ya tona asirin wannan miyagun mutanin dasuka keta mata haddi, Allah ma bazai barsu ba musamman wannan wadda shine ya aikata komai da komai. Hmmm 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Yau su Raihanah sun tafi makaranta babu kowa agida, Hajja ma taje asibiti dan yau batayi Bacci ba sakamakon zazzaɓin daya sata agaba. Duk sainaji gidan babu daɗi, tunawa nayi da wannan wurin shan iskan dana gani aranan danazo gidan. Sanye nake cikin wata doguwar riga abaya wadda Raihanah tabani, gashin kaina ɗaya sha gyara sai tashin ƙamshi yake na tufke shi da ribbon wadda shima Raihanah ce ta siyo mun bandir ɗinsa masu kyau. Ɗankwalin abayar na ɗauka na yafa akaina sannan na fito. Iska mai daɗi ga daddaɗan ƙamshin fure daya mamaye ko ina na gidan. Sojojin dana gani suna shawagi a tsakar gidan yasa naɗan tsorata, to amma ai Abby yace idan ban shiga hanyarsu ba suma bazasu shiga tawa ba. Da wannan naji ƙwarin guiwa yazo mun. Tafiya nake ina kama ɗankwalina da iska ke ƙadawa gashin kaina sai tashi yake, har na iso bakin rumfar naga ai ƙofar ma abuɗe take. Murmushi nayi na shiga da sallama kamar akwai wadda zai amsa mun. Babu kowa acikin wurin, sai ƴan tsuntsaye dake zaune saman bishiyoyin kayan marmari. Kusan babu abinda babu anan na kayan marmari masu kyau sunyi ɓulɓul dasu. Ga wannan tulun ruwan dake kwarara sharr dashi babu datti aciki. Bishiya apple na gani, ga apples sunyi yawa akai sunyi manya manya gwanin ban sha'awa, guda biyu na cire na wanke a ruwan dake kwarara a Tulun sannan na zauna a ɗaya daga cikin kujerun da aka tanada saboda zama. Banji motsin mutum ba sai kawai ji nayi an warce Apple din dake hannuna. Miƙewa nayi ɗan ganin wanene wanann,wani irin bugawa naji zuciyata tayi. Wayyo Allah, Ni dake addu'a kar Allah ya ƙara haɗani da wannan mutumin mekuma ya kawo shi nan. Ai babu laifin danayi masa, kallon Apple dina dake hannunsa nayi inajin zafin kwacemun ita dayayi, wani irin wulaƙanci ne da rashin sanin darajar dan adam ne haka. Kallon ta yake with deer anger on his face. Waya bata daman shigowa private garden ɗinsa. Who is she, how dare she? Bakina na rawa nace "me nayi maka ka ƙwacemun Apple dina ahannu" na ƙarasa maganar hawaye na taruwa a idanuna. What??? She even dares to question him akan abunsa, ehhh lallai gaskiya anyi sake wa wannan mai aikin har aka bata daman ta tsaya ta bawa shi the mighty MUJAHID amsa. Yanzu ɓacin raine kwai kwance afuskata, ina ƙoƙarin na buɗe baki naƙarayin wani magana naji ya ɗaukeni da wata makauniya wadda zafinta har tsakiyar brain ɗina najishi. Ban ankare ba ya ƙara ɗaukeni da wata aɗayan kumatu na, ya matse mun baki yace "how dare you ina magana kina magana. Waya baki daman ki shigo mun garden ɗina, waya baki daman ki tsinka mun fruits ɗina kikai filthy mouth ɗinki. Nayi miki kamada wadda zaki kalla har na fada ki faɗa, You insolent gurl ". Tureni yayi na faɗi akan artificial carpet grass da aka malale gaba ɗaya wurin. Kama ƙuncina nayi da hannu biyu ina jin yadda hawaye masu zafi suke gangarowa. Yana tsaye bai tafi ba, ina ƙoƙarin miƙewa naji ya kamo hannuna ya miƙar dani tsaye, jana yake kamar dabba har yakai kofar shigowa cikin garden ɗin ya jefar dani awaje ya ƙulle Kofar. Miƙewa nayi da gudu nayi cikin gida ina kuka kamar an aiko mun sakon mutuwar Innati, Allah ya isa ban yafewa ...... Like And comment🙏🙏🙏 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 31_35 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Ina shiga part din Hajja na wuce ɗakina direct. Kwanciya nayi saman gado ina sharara kukana yadda ya kamata. Menayiwa wannan mutumin yasani agaba haka ne. Idan ma wurin nasa ne ba saiyayi mun magana da baki ba, wato shiga jaka yasamu dole yayita jibgata, kuma ban yafe ba sai Allah ya sakamun. Da haka nayi bacci inajin yadda kumatuna ya tasa yayi suntum, har ciwon kai nakeji sosai sosai. Hajja tadawo daga asibiti ta nemi Aneesa akace ai tayi bacci. Itama haurawa sama tayi zuwa ɗakinta taɗan kwanta dan har yanzu jikin bai gama sakinta ba. Ina cikin bacci naji an diro akaina,ko ban farka ba nasan babu wadda zaiyi hakan sai Raihanah. Itama kanta haushinta nakeji tunda ɗan uwanta yasani agaba baya sona ko kaɗan. Duk yadda tayi na farka naƙi tashiwa, inaji tayita sakin tsaki daga ƙarshe ma fushi tayi ta fice a ɗakin. Araina nace kanku akeji keda ɗan uwanki. Har bayan sallan maghrib Hajja bata ga Aneesa ba, yaci ace tafito ko kuma ta farka abaccin haka ai, to ko dai batada lafiya ne. Har ta miƙe zataje dubata aɗakinnata dakanta sai gata ta fito. Fuskarnan tamau, har yanzu kuma akwai shatin yatsu a kumatunta. Ganin haka yasa Hajja tasan ba lafiya ba. Ina ƙarasowa falon na zauna kusada ƙafar Hajja na gaida ita. Cikin damuwa tace "takwara lafiya, me ya samu fuskarki naga kamar alamun yatsu" zan buɗe baki kenan sai gashi ya shigo da sallama abakinsa. Raina baƙi ƙirin nake kallonsa, yana tafiya cikeda isa kamar bazai taka ƙasa ba. Hajja tace "takwara meyasameki. Faɗa mun mana" ƙasa ƙasa nace "Hajja wannan mutuminne ya mareni ɗazu babu abinda nayi masa" "kaiiii" Hajja ta furta da tsananin ɓacin rai afuskarta, "Mujahid dinne ya mare ki? Mekikeyi masa"? Hajja ta ƙara jefomin amsar, wannan karon kam idonsa akaina karr yana jira yaji mezance, kauda kai nayi nace "Hajja wai don kawai ma shiga garden ɗin cikin gida na cire Apple ina ci, shine ya shigo ya warce Apple din ahannuna ya wanke mun mari harda jefani awaje" salati Hajja ta buga kamar zata cire bakin tajuya wurin Mujahid tace "yanzu Babana ka kyauta kenan, an kawo mun yarinya sai tiƙarta kakeyi kamar sakwara. Dan kawai na fita naje asibiti shine kasamu ka ci zalinta ko? To maza yanzu nan kabata haquri tun muna mu biyu" "WHAT"? Mujahid ya furta, Hajja tace "ƙwarai da gaske, ka bata haquri yanzunnan ko nayi fushi dakai, banson cin zali" Kamar na tashi nayi tsalle haka naji, muga girman kan nasa a ina ya tsaya, ai komai walh saiya bani haquri. Kamar yayi bomb haka ya tsaya yana kallona, yanzu akan mai aiki Hajja take tozarta shi salon kawai tasa yarinyar nan ta raina shi. Laɓɓan bakinsa dabe ko motsa ba yace "sorry" Hajja tace "banji ba, kafaɗa da kyau", idonsa har ya juya kala yace "I'm sorry", ɗagowa nayi na kalli ƙwayar idanunsa, they spell danger, kallon dayayi mun irinna "zaki san dani kikayi dinnan ne" juyawa yayi ya fice yanajin zuciyarsa na wani irin ƙuna da tuƙuƙi. Shafa kaina Hajja tayi tace "Allah ya miki albarka. Dan Allah ki riƙa kiyaye duk wani abun dazaisa ki shiga hanyar Mujahid, bayason raini. Kuma wannan garden ɗin da kika shiga nasa ne, ban faɗa miki bane agabansa saboda kar kiji kunya amma ki kiyaye kinji" gyada kai nayi, abincin dare na serving ɗinta, nima na sa nawa dan yanzu tare muke cin abinci, munaci muna hira wayar Hajja ya ɗau ƙara. Wata baƙuwar lamba ce ke kiranta, da har bazamu ɗauka ba sai na ɗauka nasa a loud speaker. Jin muryan Innati yasa na daka tsalle nayi wani ihun murna nace "Innatina kece" dariya Innati tayi tace "Allah daiya shiryeki Jamma" Hajja dai tana zaune sai murmushi takeyi batasan meyasa dataji muryan Innati kawai taji wani daɗi aranta ba. Gaisawa sukayi, harda Ameera sannan ta miƙawa Hajja akan su gaisa da mahaifiyarta. Jira Innati take taji muryan matar, haka kawai ta tsinci kanta da faɗuwar gaba. Sallama Hajja tayi tace "Assalamu alaikum, ina wuni innatin takwara" gbasssss Innati taji zuciyarta tayi wani irin mummunar bugawa, tabbas tasan muryannan kuma kamar tasan mai muryan amma a ina ta mance. Zuciyarta nacigaba da bugu ta amsa gaisuwan Hajja, ɗan magana sukayi na lokaci kaɗan sannan ta miƙawa Aneesa wayar. Cikeda shagwaba tace "Innati yaushe zakuzo dan Allah keda Ameera. Ina kewarku sosai sosai" rau rau da ido nayi, gaskiya komai wahalar rayuwa gara ace kana tareda naka. Ahaka dai mukayi sallama da Innati. Hajja tace "muryan mamanki kamar tawa, tana magana sainaji kamar nike magana da kaina" murmushi nayi nace "Hajja wlh dan ma baki ganta bane. Kamanninku ɗaya, harta yanayin fuskarku da yanayin jikinku" da mamaki Hajja tace "kai takwara banason ƙarya, dan kawai nace muryarta irin nawa shine zaki ce kamanninmu ma ɗaya"? Noƙe kafaɗa nayi nace "toh shikenan tunda baki yarda ba, Allah ya haɗaku zaki gani ai" ahaka mukayita fira har ƙarfe tara da rabi sannan kowa ya tafi ɗakinsa. Tun ranan da abun yafaru ban ƙara sashi a idona ba. Yau wankan atamfa naci riga da skirt. Dake niba gwana bace a ɓangaren ɗauri yasa na yafa ɗankwalin akaina kawai na fito. Raihanah har yau fushi take dani, bata ƙara zuwa gefen Hajja ba yasa nace yau ni da kaina zanje na ɗaukota muzo muyi hira ni kaina na gaji da zaman kaɗaici. Ina cikin tafiya naji abu ya kamamun kasan skirt ɗina. Juyawan dazanyi nayi tozali da wani irin katon ƙare wadda tunda Innati ta haifeni ban taɓa ganin irinsa ba, ƙatone bana wasa ba kamar ba abinci kawai ake bashi ba. Ga bakin shi wani iri ba kyau, labbansa na sama maga maga sun rufe bakinsa gaba ɗaya, wani ihu nayi na ƙwace skirt ɗina abakinsa nafara gudu ba kakkautawa. Karen ko kamar ance yabini ina gudu yana bina yana haushi, kuka na fashe dashi ina ihun ataimaka mun. Hatta sojojin dake gadin gidan sun kasaa tsaida shi, gudu muke ina jin yadda yake kamamun kasan skirt ɗin, ai ba shiri na tattara shi sama na riƙe ahannu ina ihun neman ceto. Munyi gudu mun zagaya gidan duk da faɗinsa sau biyu, daidai munzo part din Mami naga wani ya buɗe ƙofa alaman fitowa za'ayi. Wani irin super nayi koma waye aƙofar nasan bai ankare dani ba sai jina kawai nayi akan mutum na fado saman ruwan cikinsa na bugo ƙofar. A mugun tsorace nake dan haka na ƙanƙame mutumin ina kuka kamar raina zai fita. Shiko karennan yana ganin ta tsere masa yasa ya koma can bayan wani gini da akayi kamar boys quarter yana wangale tail ɗinsa. Mamaki ne ya kamani ganin Mujahid tsaye awurin sai tiƙar dariya yake kamar hanjinsa zai fita, shiko karen sai rawa yake yana tsalle. Da alama dai shi dinne ya tura mata bull dog dinnan. Kai amma Mujahid dinnan professor ne a ɓangaren mugunta🙄🙄 Kusan minti biyu banji mutumin ya motsa ba, har na karashi kuka na banji yace na tashi ba. Ahankali na ɗaga kaina na zuba masa ido kamar wani naga sabon halitta. Lallai wannan gidan ƴan kyau ne. Shima sanye yake cikin kakin sojoji, kuma yana kamada Abby. Kamar yadda nake kallonsa shima haka yake kallona. Tamau naga ya haɗe fuskarsa ya fara kokarin mikewa. Da sauri na tashi daga jikinsa ina jan hanci nace "dan Allah kayi haquri,wani karene yabini" gyaɗa kai kawai yayi yace "ki kula" sannan ya fice a falon yana gyara kakinsa wadda ya matuqar amsar jikinsa. Murmushi nayi, wannan bawan Allahn ya haɗu. Gashi ba baƙi ba kuma ba fari ba, ƙirar jikinsa ya nuna cewa shi ɗin yana ɗaga karfe kamar dai wancan arrogant man ɗin. Sai yanzu ma nafara tuno wani abu, karennan saikace an aikoshi. To idan aikoshi akayi wanene wannan mugun da baya ƙaunata, wani zuciyar yace "mugun nanne mana" haba aiko ba'a faɗa mun ba nasan babu mai nufina da Sharhi sai shi. Yanzu inda karennan ya illata ni fa🥹 Muryan Mami naji abayana tace " takwarar Innati fatan dai babu abinda yasameki ko"? Juyowa nayi ina kallon ta, zaune take a cushion ga takarda ahannunta tana dubawa. Wani irin kunya naji ya kamani, yanzu haka ta kamani ina kalle mata yaro daga sama har ƙasa. Ban iya cewa uffam ba na juya da sauri na buɗe ƙofan nafito, cin karo nayi da faffaɗan ƙirjinsa yana tsaye agabana ya cusa hannayensa a cikin wandonsa. A mugun hankali na ɗaga ido na zuba masa kamar yadda shima ya zuba mun tasa. Ni kallon tsoro nakeyi masa shi kuma yana kallon a da tsantsar tsana wadda hakan ya gaza ɓoyuwa afuskarsa. Hannu yasa ya hanmaɗeni gefe yayi wucewarsa. Bayansa nabi da kallo kawai na girgiza kai, Allah dai yaso mutum babu abinda yasameni dana kai ƙara wurin Hajja. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 "Innati na shiga uku, yau sati biyu kenan banga period ɗina ba. Dan Allah babu komai ko"? Ameera ta tambayi Innati tanaji zuciyarta na tsinkewa. Kwana biyun nan ko Innati ta lura da yawan baccinta, kuma ga yawan kasala datake fama dashi, take zuciyar Innati yayi wani irin wawan bugu. Ya Allah yasa ba abinda take tunani bane. Ta ina zata fara inna lillahi wa inna ilaihi raji'uun wannan shine abinda taketa furta wa. Ƙoƙarin kwantar da hankalinta tayi dan itama Ameeran ta kwantar da nata, amma tabbas sai tayi da gaske kar abinda take zargi ya zamo gasky. Idan ko hakan ya tabbata ba ƙaramin cutar su wannan mutanin sukayi ba. Ameera dai har yanzu ƙirjinta sai bugawa yake, ɓakonta bai taɓa tsallake kwanakinsa ba sai wannan karon. Mutaninnan sun bar mata tabon da harta koma ga Allah bazai taɓa gogewa ba, kullum saita kai ƙaransu wurin Allah, idan Innati tayi bacci kullum kwana take cikin kuka da mafarke mafarke. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Haka rayuwa ta cigaba da gudana agidan Goggo. Yau suci gobe kuma sai yadda hali yayi. Abun Abba kuwa tuni mahaifinta yabawa wani dama ya kawo sadaki. Ran Abba ba daɗi haka yake kallo budurwarsa zata auri wani duk asanadiyyar Hussaina. Ko ina na gidan duku duku babu arzikin gyara. Ga kwanuka dake birjik atsakar gida wadda sukayi amfani dashi babu mai gyara musu gidan. Haka Goggo wani rana zata zauna tayita tunanin Innati tace Allah sarki da Hussaina na nan data gyara gidannan fes fes. Ai bakiga komai ba. Abba ko ba ƙaramin kewar ta yake ba, kullum fama yake da sha'awaratarsa amma kuma batanan. Duk saiyaji inama ace zata dawo, daya gyara tsakaninsu sunyi rayuwarsu cikin soyayya, dan wani irin soyayyar ta ne ya bijiro masa yanaji kamar zai fasa masa zuciya. Pls like And comment 🙏🙏 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 REEMAH ✍️ PG 36_40 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Kullum addu'a nake Allah ya haɗani da wannan kyakkyawan yaron Mamin. Ko hira muke da Raihanah sai nayita tambayarta ko yana nan, tun bata gane ba har tazo ta gane tana mun tsiya. Niko wani irin yanayi nakeji, wannan ake kira da soyayya? Daga ganin mutum shikenan sai na faɗa masa. Har sunansa saida ta faɗa mun, Ya Ismail. Kullum ina hanyan zuwa part ɗin Mami wai ko dan zan ganshi, amma abun haushin saidai nahaɗu da mutumin dabaya ƙaunata arayuwan nan. To wai shi baya aiki ne, kullum yana gida saikace namace. Kuma har yanzu idan na ganshi saina gaidashi amma baya amsawa,niko saikace mara zuciya bana fasa gaidashi aduk lokacin dana haɗu dashi. Yau ina taya Baba Larai aiki a kitchen ɗin Hajja tasa naje babban lambun kayan miya a bayan part ɗin Hajja na tsinko mata ganyen ugu da alayyaho. Ina tafiya ina waka na shigo lambun. Har na fara tsinkawa naji mutum na waƙa abayana. "As I dey look your eyes, Shining like brightened star Baby girl I don't mind You go be my wife When you down you can call on me I'll be at your feet Even if you slump I will draw you up Cos when I see you bumbum I no dey hear caution You sweet like Panadol You dey cure my boredom I say when I see your bumbum Bumbumbum....." Da sauri na juya dan ganin wanene wannan, ƙirjina ne ya buga ganin Amin tsaye abayana sai ƙare mun kallo yake yana lashe labbansa. Sosai naji raina ya ɓaci take zuciyata tayi baƙi ƙirin. Wannan iskancin nasa har kan masu aiki? Ehh lallai Raihanah tayi gasky da tace nayi taka tsantsan dashi. Shiko Amin wani shu'umin murmushi yayi yace "haba baby gurl, why do you look scared. Nifa masoyinki ne. Zan baki duk wani jin daɗi na rayuwa dakike buqata, zan kashe miki kuɗi, zan kaiki ƙasashen waje" yacigaba da jero mata karyayyaki yana ƙara kusantota. Sosai raina ya ɓaci, gashi lambun yayi nisa da cikin gida balle ko nayi ihu ajiyoni. Kwandon dake hannuna na ɗaga na nuna masa nace "wlh ko ka barni kona ƙwala maka wannan kwandon agoshi" ganin dai ba fasawa zaiyi ba nafara kiran sunayen Allah azuciyata. Sosai yake matsoni ina komawa baya harya kaini jikin bango, fuskata har wani ja ja yayi saboda irin haushin da nakeji. Hannu nasa na tunƙudeshi gefe da gudu nabar wurin hatta kwandon ma awurin na barshi. Sosai nake gudu bana kallon bayana saiji nake kamar yana bina. Baiso ta tsere masa ba, wannan cute lips dinnata yaso ya ɗanɗana. Da alama dai yarinyar akwai wiyan sha'ani. Wani smirk yayi yace "you've escaped honey, not another day cos ain't giving you a chance to do that" hannunsa yasa saman wandonsa, tsabar jaraba har tayi wani ƙal🙈. Kwandon data bari ya ɗauko yayi part ɗin Hajja dashi. Ina shigowa kitchen na ƙulle Kofar gam, Baba Larai daketa zaman jirana ta kalleni tace takwarar Hajja ina ganyen"? Saida na saita numfashina sannan na dago na kalleta, itama ni take kallo. To me zance mata, su yaran manya iyayensu na bala'in ji dasu, idan nace ga abinda Amin yayi mun anya baza'a hukunta niba. Wani ƙarya na ƙaƙaro nace "Baba, wani ƙaton maciji nagani rataye a ganyen ugun, shine naji tsoro na gudu, harta kwandon ma awurin nabarshi" da mamaki Baba Larai ke kallona alamar dai bata yarda ba, nace "Allah Baba, in baki yarda muje kigani"ganin na dage yasa Baba Larai cewa "toh ai shikenan, bari na kira ɗaya daga cikin mazajennan suje su tsinko mun" ajiyar zuciya nayi. Knocking mukaji aƙofar kitchen ɗin. Baba Larai ce ta buɗe ina leƙawa naga ko wanene idona ya sauka kan Amin dake riƙe da basket dana bari a lambu yana wani cin magani wa Baba Larai. Kulululu naji cikina yabada ƙara, wlh tsoron wannan mutumin nake dashi da sharrin dake tattare dashi. Shigowa Amin yayi kitchen ɗin ya ajiye kwandon saman canta, har ya juya zai tafi saikuma ya juyo ya kalleni ya kashe mun ido ɗaya, tas akan idon Baba Larai daketsaye tana mamaki wai yau Amin ne a kitchen dakansa. Cabb. Bayan ya fice ta kalleni taga duk a tsorace nake, tace "takwarar Hajja meya haɗaki da Amin" bassss naji zuciyata ta buga, me zanyi da Amin inba Baba Larai ba. Bakina na rawa har idona ya fara tara hawaye nace "ba komai fa. Wlh babu komai Baba" gyaɗa kai tayi dan yadda taga tsoro a idanuna tasan tabbas gaskiya nake fadi, takowa tayi gabana takama kafaɗuna tace " karki damu. Kawai dai banson naga abinda zai cutar dake ne kuma naki faɗa miki, karki kuskura wani abu ya haɗaki da Amin, ko hanya karki bari ya haɗaku. Daso samu ne ma nace karki bari ko gaisuwa ya shiga tsakaninku, amma nasan bazaki iya ba dan haka ki lura kinji"? Gyaɗa kai nayi jiki asanyaye na fice daga kitchen ɗin. Tabbas yazama dole na ja layi tsakanina da wannan bawan Allahn. Hajja na samu a falo tana zaune, shiko wannan basamuden yana kwance kan cushion din da Hajja take ya kwantar da kansa saman cinyarta tanayi masa tausa. Ko kallonsu banyi ba dan banida da wani sauran ƙwari ajikina nazo wucewa naji Hajja tace "takwara naji Larai tace wai kinga macici a lambu. Fatan dai babu abinda yasameki ko"? Shaf ma na mance cewa nayi wannan ƙaryar, idona na kan tulin gashinsa da Hajja ke masa tausa na gyaɗa kai kawai na wuce nawa ɗakin. "Allah dai ya kyauta, toko menene ke damunta ta wani ɓata rai. Kodai bata jin daɗi ne" Hajja ta faɗa tana ƙoƙarin kama masa gashin da rubber ring. Juyowa yayi ya kalleta yace "wai meyasa kika damu da mara kunyar nan ne Hajja, saikace ba mai aiki ba, duk kinbi kin wani sake mata har hakan yasa take rainani" fasa ɗaura masa gashin Hajja tayi tace "waya faɗa maka itaɗin me aiki nane, Babana ka fita a idona na kulle. Naga kwata kwata kaki jinin yarinyar nan kamar kana ganin hanjin cikinta. Akanta fa sai mu bata da kai tammm" kasa cewa komai yayi yace "Allah ya huci zuciyar ki Hajja ta" Ameen tafaɗa tacigaba da ɗaura masa gashinnasa. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Ameera na assignment aɗaki Innati ta kirata akan tazo ta duba mata miyan dake wuta akitchen. Fitowa Ameera tayi daga ɗakin daga ita sai yar rigar kanti daidai guiwarta. Ido Innati ta zubawa ƴartata tana kallon ta, wani irin haske ta ƙara gashi idanunta sun wani cicciko kamar na babban mace. Harta nonuwanta sun ƙara tasawa fiyeda da yadda tasanta. Wai meke faruwa ne anya bazata kai yarinyar nan adubata a asibiti ba kuwa? Ameera na shiga kitchen ɗin tabude tukunyan miyan dake wuta, wani irin haura mata kai ƙamshin miyan yayi take taji amai yazo mata, da gudu tafito daga kitchen ɗin tana rike baki tayi cikin daki. Innati harta fara Sallah aita yanke shi ta biyo Ameeran ciki, a bayi tasameta sai faman kwarara amai take kamar hanjin cikinta zasu fito. Habawa ai Innati take ta tabbatar da abinda take zargi. Mekuwa zatayi inba fashewa da kuka ba, tana kuka tana kiran Allah kusa. Shikenan mutaninnan sun cuceta sun cuci rayuwar ƴarta. Ameera na ganin Innati ta fashe da kuka ta wanke bakinta da sauri tataho wurin Innati ta rungumeta itama ta fashe da kukan duk da batasan menene ba. Rungumeta Innati tayi tana cewa "Allah saiya saka miki Ameera, Allah bazai bar mutanin dasukayi miki abunnan ba saiya tona asirinsu. Allah saiya hukuntasu da mafi tsananin azaba" cikin kuka Ameera tace "Ameen Innati, wlh nima addu'ar danakeyi musu kenan" kamo fuskarta Innati tayi tace "bazamu zubar da cikin nan ba zaki haifoshi kuma zamu bashi tarbiyya yadda Allah da Manzonsa suka umurta" Ameera najin Innati ta ambato kalmar ciki taji komai nata ya tsaya cak, ci me? Ciki? Ajikinta. Kai inaaa hakan bamai yiwuwa bane, kallon Innati tayi tace "Innati ciki fa kikace" bata kuma sanin metake ciki ba bayan wannan tambayar datayiwa Innati sakamakon zubewa aƙasa datayi sumammiya. Cikin kiɗima Innati tafara ƙoƙarin tashin Ameera tana kuka kamar anyi mata mutuwa. Tsoronta shine kar ƴarta ta faɗa cikin wani hali saboda wannan jarabawar da rayuwarta ta afka ciki. Ruwa ta samu ta ɗan yayyafa mata, wani irin dogon numfashi taja kafin ta sauke saikuma ta fashe da kuka tana duke duke kamar mahaukaciya tana cewa lallai saidai azubda wannan cikin dake jikinta ita bazata riƙe ba. Abun tausayi 🥹 🥹 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Yau ina shigowa part ɗin Mami na tadda itada Raihanah Ya Sultan Mustapha da Ya Isma'il crush ɗina. Wani irin daɗi naji ya mamayeni a lokacin dana ƙyallara idona akansa. Kamar an yaga mun ruwan sanyi azuciyata haka naji. Shiko ko yasan da zuwana hankalinsa na kan wayarsa yana latsawa. Mamy ce tace "a'a takwarar Hajja shigo mana" sai asannan na lura da idon kowa kaina yake, kunya ne ya rufeni ankamani ina kalle mutumin dako yasan da zamata. Gaidasu nayi na nemi wuri na zauna kusada Raihanah wacce ke tsokanata ƙasa ƙasa nikuma ina share ta. Satan kallon inda Ya Isma'il yake kwance nayi, direct naga shima ni ɗin yake kallo, da sauri na kauda ido inajin yadda zuciyarsa ke bugun tara tara. Can na ƙara ɗagowa na saci kallonsa, kamar ɗazu yanzu ma haka kallona yake. Ban iya sauke idona ba, sai shagala mukayi da kallon juna, wani irin killer smile ya sakar mun wadda yasani jin gaɓoɓina duk sun mutu, kunya ne ya kamani nayi saurin sauke idanuna ƙasa. Lallai wannan mutumin na musamman ne, komai nasa abun burgewa ne. Ashe duk wannan nufin da akeyi akan idon Mamy, murmushi kawai tayi ta girgiza kai. Allah ya shirya yaran zamani watau ko kunya basuji har wani turawa juna signal suke. Uhmmm, su Isma'il Allah yayi, dama shine kawai duk cikin yaranta basu damu da soyayya ba, shi Mujahid yayi soyayya harda aure, shikuma Sultan wannan ba'a magana tunda budurwarsa ma sananniya ce agidan. Shine dai Isma'il wadda aiki kawai yasa agaba bai damu da komai ba. Kallon Aneesa tayi, sai wani duƙe kai takeyi ita adole kunya takeji. Kasa zama nayi, duk najini atakure, idonsa ƙyar akaina yake. Duk wani motsin danayi a idanunsa yake, kamo hannun Raihanah nayi nace mata muje ɗaki akwai maganar dazamuyi, har mun tashi zamu tafi saiga Baba Larai tayi sallama akan Hajja na nemana. Muna isowa part ɗin masani Hajja da wayarta ahannu sai kai komo take yi, ga samuwa kwance afuskarta. Tana ganina ta mika mun wayar tace " gashi nan mahaifiyarki ce ke so tayi magana dake, duk sainabi na damu yadda naji muryarta kamar ba lafiya ba" inajin haka babu zuciya ta tsinke, menene yasamesu. Allah yasa lafiya. Karɓan wayar nayi na kira Innati, bugu biyu ta dauka, a bayan wayar naji kamar muryar Ameera tana kuka, take hankalina ya ƙara tashi na tabbata cewa ba lafiya ba. Muryar Innati na rawa kamar itama tana shirin yin kukan tace "Jamma bazan iya ni kaɗai ba, zan iya karaya, muna buqatarki ataredamu. Allah ya jarabcemu babban jarabawa. Dan Allah kizo" ban iya cewa komai ba sakamakon hannuna daya fara rawa har bansan lokacin da wayar ta subuɗo daga hannuna zuwa ƙasa ba. Hajja dake tsaye tayi saurin ƙarasowa wurina tana tambayata menene. Hawaye kawai ke gangarowa daga idanuna,ganin haka yasa hankalin Hajja tashi. Da ƙyar na iya buɗe baki nace "Hajja Innati na nemana. Gidanmu ba klau ba, inaji ajikina akwai abinda ya faru" itama Hajja cikin tashin tace "to ai baza'ayi haka ba. Yanzu bari in kira kamalu driver ya kaimu gidannaku tare" tana gama faɗin haka tasa Baba Larai ta kira drivern, sukuma suka shirya. Har lokacin da suka shiga mota zuwa gidannasu kirjin Aneesa keta bugun uku uku. To meya faru ne wai agidan, ko dai Abba yazo inda su Innati suke ne yayi musu barazana. Ita kwata kwata ma bata kawowa Ameera batun ciki ba. Suna isowa gaban estate ɗin aka yi saurin buɗe musu ƙofa dan sojojin dake gadin wurin sun shaidasu. Tun kafin driver yagama faka motar Aneesa tayi sairin buɗe kofar motan ta fice da gudu har Hajja na kiranta amma batajiba. Ina ƙarasowa gaban part ɗinmu na bude kofar falon na shiga nama mace wani abu wai shi sallama. Abinda nagani shine ya ƙara tada mun hankali har yasa nakasa motsa wa. Innati na ƙoƙarin kama Ameera amma sai buge buge takeyi kamar tababbiya. Me ke faruwa ne wai. Ameera na ganina ta mike da gudu tazo ta rungumeni tana ƙara rushewa da sabon kuka. Nima rungumeta nayi na fashe da kukan duk da bansan kukanta na menene ba. Sallama Hajja tayi ta shigo falon, dake Innati tabawa falon baya shiyasa bataga wanene ya shigo ba. Har Hajja ta ƙarasa shigowa falon sannan Aneesa ta rabu da Ameera tace "Innati ga Hajja tare mukazo"Hajja ta kafawa bayan Innati ido sai jira take matar ta juyo taganta. Innati ma take taji bugun zuciyarta ya canza tun kafin ma tajuyo, a wani irin slow ta juyo dan ganin wacece Hajja dinnan da Aneesa ke yawan maganarta. Idon Innati na faɗawa cikinna Hajja taji komai ya tsaya mata cak. Hakan ma takasance agefen Hajja. Ameera ma takafe Hajja da ido tana kallon matar, wannan ai carbon copy ɗin Innati ce. Hajja data kasa motsawa, laɓɓan bakinta na rawa ta fara ambaton sunan Allah tanayi tana ƙarawa. A hankali tafara takowa inda Innati ke tsaye, tana zuwa tasa hannu ta ɗan karkata wuyan Innati gefe, taja da tulin gashin kanta,ta duba wani birthmark wadda Nadeen ɗinta data ɓace takeda shi. Wani wawan bugu zuciyar Hajja yayi a lokacin da yayi tozali da tabon wuyan Innati wadda sak irinna Nadeen ɗinta ne. Atake ta fashe da kuka tafara kiran Nadeen ahankali, tace "wlh Nadeen dina ce. Ke ce Nadeen? Ina kika shiga wannan shekarun naketa nemanki, dama da rabon zan ganki kafin nabar duniya. Alhamdulillah alhamdulillah Alhamdulillah lallai Allah kaine abun godiya. Yau naga ɗiyata dana yi shekaru da shekaru ina nema. Allah na gode na gode Nagode ya Allah". Innati kam kasa cewa komai tayi, tabbas babu makawa wannnan mahaifiyarta ce wadda taɗade tana addu'ar Allah yanuna mata ita tunda tasan ahannun marasa imani ta girma. Kuma kullum ana faɗa mata cewa itaɗin ƴar tsuntuwa ce. Hawayen farinciki ne ya fara gangarowa daga idanunsu gaba ɗaya, cikin begen juna Hajja da Innati suka rungume juna suna cigaba da kukansu. Na da Ameera duk muka tsaya muna kallon wani babban iko wadda Allah kaɗai keda ita. Kenan mu ɗin jikokin gidan Isa Mainoma. Hannu Hajja ta miko mana mu biyun tayi mana alama da muzo wurinsu, da murmushi mai kamada kuka mukazo tahaɗa damu ta rungume akirjinta. Hajja baki ya kasa rufuwa sai furta kalmar godiya take abakinta. Bayan komai ya lafa duk suka zauna saman carpet dake malale a falon Hajja sai kallon Innati take tana murmushi. Turawa sunce blood is thicker than water, gashi dai banda kama tun kafin suga junansu amma zuciyoyinsu yariga ya basu cewa sunsan juna. Wayarta ta ciro ajaka ta dialling numbern Abby. Bugu biyu Abby ya ɗauka tun kafin yayi sallama Hajja ta tari numfashinsa tace "Ɗan Isa ka kasa nemo mun ƴata, to gashi ni da kaina na samota. Allah ya nuna min ita da kaina. Sai anjima" bata bari Abby yayi magana ba kittt ta kashe wayar. Kallon Aneesa tayi ta ce "takwara ashe dai keɗin jikata ce, Allah sarki shi yasa najiki daban azuciyata na ɗaukeki a matsayi ɗaya dasu Raihanah. Taho nan mai kamada Nadeen " taƙarashe maganar tana mikowa Ameera hannu alaman tazo. Cikin sanyin jiki taƙaraso wurin Hajjar, sai kuma takara fashewa da kuka. Sai asannan kuma hankalinsu Hajja da Aneesa yadawo kan cewa ai akwai abinda yafaru dayasa su zuwa gidan. Kallon Innati tayi tace "Nadeen mai ya sameta. Ɗan Isa yabani labarinki da komai. Kuma inshallah ƙarshen wahalarku kenan arayuwa. Saina tabbata kun samu jin daɗi wadda baku taɓa tsammani ba. Yanzu dai zaku shirya dan tareda ku zamu koma gida bazan barku anan ba" cikin kuka Ameera tace "Hajja babu inda zani. Bazan iya fita na kalli mutane ba. Gani zanyi kamar kowa zaina kallona da abun kunyar dake jikina. Bazan iya ba" Kallon Innati nayi naga kanta aƙasa, to me suke boye mana ne. Hajja tace "Nadeen menene yake damunta, ku faɗa mana mana, duk kunbi kunsa hankalina ya tashi haba dan Allah " ɗagowa Innati tayi naga idanunta sun juya kala zuwa jaa tace "Hajja Ameera na ɗauke da juna biyu ne" salallami Hajja tafara tana maimaitawa. Nikam daskarewa nayi naji gumi duk ya rufeni na kasa koda ɗaga yatsana ne. La haula waka quwwata illa billah. Allahumma ajirnee fee musibaty wa akhlifnee Khairan minha. Hasbunallahu wa ni'mal wakeel. Ciki? Ameera nada ciki? Babu babban jarabawar daya kai wannan girma a rayuwar budurwa. Shikenan an gama da rayuwarta. Ganin hankalin kowa atashe yake yasa Hajja danna nata tashin hankalin sanya kwantar musu da nasu. Kamo hannun Ameera tayi cikeda kulawa tace " karki damu. In every disappointment there's surely a blessing. Wannan cikin tabbas disappointment ne amatsayinki na budurwa, amma kuma ɗan dake cikinki bi'znillah alkhairi ne dashi mai ɗunbin yawa. Bazaki depressing kanki akan abinda bakida laifi akai ba, tabbas maganan mutane zaiyi yawa amma inaso kiyi kokari ki tsohe kunninki kar ki taɓa yarda maganan mutane yayi tasiri akanki. Ai Allah ba azzalumin bawa bane, kuma yana sane dake. We shall overcome this together" wannan nasihar ta Hajja ba ƙaramin kwantar musu da hankali yayi ba. Haka sukayi ta ɗan taba hira wadda kusan gaba ɗaya akan rayuwarsu tabaya ne. Watau duniyannan,komai kudinka baka isa ne ka hana wani abu yasami wani naka ba. Idan ba haka ba, duk da kuɗi da kuma dukiya da Allah yabawa su Hajja hakan bai hana ƴarta ta sha gwagwarmayar rayuwa ba. 🥹🥹🥹 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 "Yes Please do check that out and keep me updated about all that's ongoing at the headquarters. Kitt ya kashe wayar sannan ya maida hankalinsa kan abinda yake yi a system dinsa. Ɗan gajeren wando ne abokinsa da riga armless irin mai tsayi dinnan. Isma'il ne ya fito shima sanye yake da kananan kaya kamar na danuwansa. Yau fuskar cike take da annuri ba kamar kullum dayake cin magani ba. Kallonsu Mujahid yayi yace "soja ƙanin mutuwa. Ana ganinku jiki ke rawa" ƴar dariya Isma'il yayi wadda ya bayyana zallan kamarsa d Mujahid saidai Mujahid yafi shi haske sosai. Ɗan jimmmm Isma'il yayi kamar da magana abakinsa saikuma yace " bros, how do you see wannan yarinyar ta wurin Hajja" kallonsu Mujahid yayi yace bangane ba wacce yarinya kake magana akai, murmushi Isma'il yayi yace "that beautiful girl dake zama da Hajja" kwata kwata MJ yamance da wacce yarinya Ismail ke magana akai saida yayi masa kwatancen ta, wani irin dariya ya fashe dashi harda kyalkyalwa ya tafa hannu yace "lallai Isma'il, badai so kake kace mun yarinya mara kunyar nan kake crushing akanta ba. Cabb, dama dai ka cire wannan filthy tunanin akanka. Yarinyar nan samm batayi deserving soyayyarka ba, she's a maid fa for crying out loud. Mai aikin Hajja ce. Mezakayi da ita bayan ga mata dayawa a waje masu qualification sai wacce ka zaɓa, come on Man" sosai wannan maganar ta MJ ya taɓa Isma'il amma ya dake yace "bros kenan. Ai baka saniba, ni cikin spec ɗina na macen danakeso na aura, banason wacce idonta ya buɗe ba. Nafison na auri wacce ni da kaina zan koya mata abubuwa da kaina. Zan ɗorata a tafarkin danakeso tacigaba. So all that you mentioned is just a world of fantasy" wannan karon ma dariya MJ yayi yace "lallai yaro ashe da bazaka taɓa sanin menene soyayya arayuwarka ba. Jeka ka auri ƴar ƙauye wacce zatazo ta hura wutan icce akitchen ɗin da akwai gas. Kai baka ga rayuwata da Neehal ba, she was the perfect one for me. Babu abinda na koya mata saima wanda ni ta ɗorani akai. I missed those days, ban taɓa tunanin rabuwa tsakaninmu ba amma gashi" sai kuma yanayin fuskarsa ya canza. Girgiza kai Isma'il yayi, yasan idan Mujahid yafara hira akan Neehal to ba'a ƙarewa ta daɗi. Gara kawai ya canza salon hirannasu dan shi kansa ya tsani labarin Neehal dama komai daya danganceta, asanadiyyarta ɗan uwansa ya kamu da cutar hypertension harya jefa kansa cikin depression wadda ya haddasa masa tsanan mata da kuma trusting ɗinsu ma gaba ɗaya. Shikam MJ tunda yayi shiru ya faɗa duniyan tunani. Ganin haka yasa Isma'il canza hiran zuwana politics da kuma abubuwan daya shafi wuraren aikinsu. Wayar Mujahid ne yayi ƙara, ɗagawa yayi da sallama abakinsa. Abby a ɗayan bangaren da bakinsa ya kasa rufuwa yace " Babana Alhamdulillah, Hajja ta haɗu da Aunt dinka. Allah ya bayyana mun ƙanwata Mujahid. Yanzu dai dan Allah kayi ƙoƙari a tracking ɗin wayar Hajja Dan taƙi ta faɗa mun inda suke". Cikin ladabi MJ ya amsa wa babansa sannan ya kashe wayar. Fuskarsa ɗauke da tsadadden murmushi ya faɗawa Isma'il abinda yafaru. Hamadala shima yayi sannan suka fara tracking wayar Hajja a system ɗin MUJAHID. Bayan sun gano inda take suka kira Abby suka sanar dashi. Sosai Abby yayi mamaki dan wannan ai estate dinsa ne, dama ƴar uwarsa na zama a estate dinsa all this while shine bai sani ba. Batareda ɓata lokaci ba ya tara sojojinsa mota uku suka tafi estate dinnasa dake can GRA Nassarawa, Kano. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Wani kwalin exotic ne ahannunsa ga kuma allura aɗayan hannunsa dayake injecting zuwa kwalin exotic din da murmushin mugunta a fuskarsa. Bayan ya gama ya jijjiga kwalin sosai ya maida shi fridge ɗin kitchen ɗin Hajja ya rufe. So much excitement on his face 😈. Akwai abinda Amin ke shirya wa amma Allah yafi shi. Cikin takunsa na ƙasaita ya fito daga kitchen ɗin yana gyara hannun rigarsa. Bayan ya fice Baba Larai ta fito daga wani lungu na falon tana sakin ajiyar zuciya. Da alama dai taga abinda yayi a kitchen ɗin, hankali tashe ta wuce kitchen ta buɗe fridge. Ba lallai sai wadda ya shirya wa plan dinnan abun zai sama ba, hala ma aje kuma Hajja tasha ko kuma wani daban. Da sauri ta ciro kwalin exotic din ta buɗe ta zazzage shi tass a cikin sink area sannan ta dauko wani kwali daban a store ta maida shi fridge ta rufe. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Mamy na ninke kaya Abby ya kirata akan tafaɗawa kowa ya hallara afalon Hajja gasunan zuwa za'ayi taro na musamman ne. Mamy bata kawowa ranta komai ba duk da ba kasafai haka Hajja ke tarasu gaba dayansu ba saimun wani abu na musamman ne ya faru. Kiran Ammi tayi awaya ta sanar da ita abinda Abby ya faɗa. Batareda ɓata lokaci ba matan da ƴaƴansu gaba ɗaya aka hadu gaba ɗaya kowa na tunanin to kome yafaru da Hajja ta nemi su haɗu? Cikeda farinciki Hajja tafito daga mota hannunta cikin na jikokinnata. Abby Kuma ya riƙe hannun Innati suna tafiya cikeda walwala. Da sallama abakinsu suka shigo falon, Abby da Innati ne agaba sai Hajja dasu Aneesa suna biye dasu. Amin dake zaune shida Sultan akan two seater yana latsa wayarsa baima lura da shigowarsu Abby ba. Su Mamy dasu MJ kowa ya kafa idonsa kan Innati ana kallon ta. Sosai suka zuba mata ido farinciki ƙall afuskokinsu. Sallama Hajja tayi itama ta shigo da ƴan matanta. MJ daya ƙyallara idanunsa kan Aneesa lokaci guda yaji gabansa ya faɗi, me hakan ke nufi. Nooo its not possible. Babu yadda za'ayi mai aiki tazama cousin sister ɗinsa. Impossible. Ameera gaba ɗaya sai taji wani irin tsoro ya shige ta at once. Musamman dataga kusan rabin falon kattin maza ne masu jida jini ajika. Wannan fargaban saitaji yadawo mata sabo dal. Hannun Hajja ta ƙara riƙewa kam har hakan yasa Hajja juyowa ta kalleta. Sosai taga yanayin fuskarta ya canza zuwa tsoro. Ƙarasa shigowa falon sukayi gaba ɗayansu. Ahankali Ameera Kebin kowannensu da ido har idonta yakai kan Amin wadda alokacin shima ya ɗago ya kalleta idanunsu ya sarƙe cikin na juna. Rugugugugugugub. Cikin kiɗima Amin ya miƙe tsaye yama mance cewa bashi kaɗai bane a falon, "kkkkkkeeee, Ke?? Mekikeyi anan?..... Kakara kakakakak 🙆🙆🙆 ana bala'i agidan Jenar. Pls manage🙏 Like Comment And share🙏🙏🙏 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 41_45 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Ganin yadda Amin yabi ya rikice upon ganin Ameera yasa hankalin kowa dawowa kansa. Sai wani sambatu yake kamar mara gaskiya. Ameera kam kasa riƙe firgicin datake ciki tayi ta fara nunashi da hannu bakinta na rawa hawaye na gangarowa daga idanunta tace "SHINE, WLH SHINE,INNATI SHINE YAYI MUN FYADE" kuuuuuuu cikin Amin ya ɗauwani sauti wadda Sultan dake gefensa kansa saida yaji. Cikin tsananin ɓacin rai MJ da Isma'il suka miƙe suka hada baki wurin faɗin "MENE, FYADE"? Take kafafun Amin suka kasa daukansa,ji yayi idan ya ƙara minti ɗaya a tsaye tabbas zasu iya gaza ɗaukan nauyinsa. Cikin aro jarumta yafara magana yana stammering yace "mmmme ne? Fyaɗe? Bani bane wlh ƙarya takeyi, ni ban santa ba" dunƙule hannu Isma'il yayi azafafe ya kaiwa Amin wawan naushi abaki wadda yasa gefen bakinsa fashewa. Mamy da Ammi mezasuyi inba kuka ba. Raihanah da Mustapha kam sai murmushi suke, yau Allah ya tona asirin Amin. Miƙewa Amin yayi yafara kukan munafirci yana cewa "wlh bani bane. I don't know what she's talking about" bai gama rufe baki ba MJ yaƙara daukeshi da wata zazzafan mari both right and left cheeks ɗinsa. Abby daya kasa koda motsawa ne a hankali yayi ƙoƙarin saita kansa har ya tako inda Amin ke tsaye, collar rigarsa ya riƙe yafara jijjigashi yana faɗin "Amin why, why Amin. Meyasa duk cikin ƴaƴana kaine kawai ka zabi ka zubar mun da mutunci a idon jama'a. Mene ka nema wadda banyi maka ba. Son abun duniya dakuma son mata yakaika ga aikata babban laifi wadda Allah ya tsinewa duk wadda ya aikata wannan laifin. Yanzu mene ribarka nayin haka. Yanzu koda yarinyar nan ba jininka bace kenan dakana tunanin kaci banza. Toh bari kaji wlh Allah ma bazai barka ba. Kuma nima ba zan Barka ba, insha Allah sai na ɗau mataki. Daga yau ko kuɗi za'a baka ka kalli wata mace awaje da filthy tunani aranka bazakayi ba. Mujahid kuyi mun maganinsa" Kamar kuwa jira MJ da Isma'il suke, Abby na sakinsa suka kamashi sukayi ta jibgarsa, idan wannan yayi ya gaji sai ya jefawa wannan, sun maidashi kamar punching bag. Ammi sai kuka amma takasa hanasu dukan ɗannata. Ai daidai sukeyi, yakamata ahukuntasa daidai da laifinsu. Kallon Ameera tayi taga duk yadda yarinyar tabi ta rikice sai kuka itama takeyi. Sosai yarinyar tabata tausayi, yar karamar yarinya Amin ya lalata mata ta rayuwa da future ɗinta. Saida suka tabbata sunyi masa jina jina sannan MJ yakamo collar ɗinsa ya jawosa har gaban Ameera ya yardashi agaban ƙafafunta, da sauri takoma baya tana kama hannun ƴar uwarta. "Beg for her forgiveness Now" MUJAHID ya faɗa cikin kausashshiyar murya, da sauri Amin ya kamo ƙafanta yana kuka yace "dan Allah kiyafemun, wlh bazan ƙara ba. Na tuba nabi Allah" babu wadda yaji tausayinsa afalon saidai mahaifiyarsa wacce itama kuka takeyi kamar harda ita aka jibga. Zuciyar mahaifiya daban take🥹 Jansa Isma'il yayi ya wurgoshi tsakar falon sannan kowa ya zauna aka sashi a tsakiya. Innati dai ta kasa cewa komai sai ɓarin hawaye datakeyi. Allah kenan, ashe dai ba'a kan ƴarta yafara ba, gashi kamuwar Allah sai ya faɗa akan ƙanwarsa duk da baisan cewa itaɗin ƙanwarsa bace. Ajiyar zuciya Hajja tayi tace "gaskiya mun haɗu da babban jarabawa, munada bara gurbi a cikinmu wadda shine ɓata gari. Haƙiƙa Allah ba azzalumin kowa bane. Kuma ance "kama tudinu tudaan" duk abinda kayi inma Alkhairi ko sharri kaima sai anyi maka. Toh gashi Allah ya nuna mana, Amin tun ba'a je ko ina ba sai gashinan akan ƙanwarka Allah ya ramawa sauran innocent girls din daka dinga yiwa wannan abun. Kuma kasnii bafa Allah yabarka ahaka bane, kayi mata tsiyataku kaida abokanka kana tunanin cewa ai itaɗin ba komai bace. Allah yasa da asirinka ya tonu bainan jama'a, mene yakai haka kunya. Ƙannenka da yayyinka all are ashamed of you. Gashinan dai asanadiyyar wannan abun, abinda ba'a fata yafaru. Yanzu haka yarinyar nan tana ɗaukeda gudan jininka acikinta. Kaga ko there's no two way about it, Allah ya riga ya haɗa ƙaddararku" dammmmm Amin yaji azuciyarsa, me Hajja take nufi da Allah ya riga ya haɗa ƙaddararsu. "dan gidanku you're gonna get married to her whether you like or not. Babu yadda ka iya it's not up to you saidai in inta tace batada niyyar aurenka"MJ yafaɗa yanaji kamar ya miƙe yacigaba dayiwa Amin ɗin shegen duka dan har wani ciza lebe yake tsabar fushin dake cinsa aciki. Wani irin kururuwa Amin yayi yafara kuka kamar ƙaramin yaro yace "Babban Yaya bazan iya aurenta ba. She's not a virgin fa. Wlh bazan iya.." bai rufe baki ba Abby ya ɗaukeshi da wawan mari sau uku, har idonsa ya kumbura yayi jaa abun aji tausayinsa kuma abun takaici. Girgiza kai nayi ina ayyana irin rashin kunya na Amin, agaban iyaye da yayyi yake cewa bazai iya aurenta ba she's not a virgin, wane ya karɓi virginity ɗin nata da har ya iya buɗe baki yayi maganan banza. Ji nake kamar na ɗauko muciya nayita raɗa masa akai. Ni dukan ma da akayi masa wlh aganina kaɗan ne dahar yakeda bakin dazaiyi maganan banza. Kai amma anyi asara anan, kuma inshallah Ameera bazata taɓa auren wannan mazinacin ba. Ji nayi na ƙara tsanan wannan arrogant man ɗin saboda shiyakeso yayi haɗin da bai dace ba. Cikin kuka Ammi tace " Amin saifa ka aureta idan har mu mun isa dakai. Dama wakakeso ya aure maka ita bayan komai da hannunka ka aikata. Karkasa nayi maka baki wadda zai bika har makwancinka, shashashan banza kawai. Allah ya shiryeka idan har kaiɗin mai shiryuwa ne. Ameera dake kan matso hawayen takaici tace "Ni dai ba zan aure shi ba. Mugu ne azzalumi kuma dan iska. Na gwammace na zauna haka ba aure har ƙarƙen rayuwata idan har dashi zan zauna. Na tsaneshi na tsaneshi kamar mutuwata" Abby zaiyi magana hajja ta dakatar dashi ta hanyar faɗin"a'a ɗan Isa. Yarinyar tagama magana, tunda tace bataso to shikenan basai an tursasata ba. Shi kuma Amin shima nawane dan haka bazanyi masa mummunan baki ba. Allah ya shiryeshi yasa ya gane. Wannan taro danaso ayishi cikin farinciki amma sai gashi ran kowa aɓace yake dan haka babu wani jimawa dazamuyi. To yara da iyaye ga ƴata Nadeen wadda nayi shekara talatin da huɗu ina nemanta sakamakon wasu mugayen mutane da aka haɗa baki dasu wurin saceta. Munyi neman duniyarnan amma muka kasa gano inda ƴata take, Allah yau ya bayyana mun ita da ƴaƴanta watau jikokina. Allah yayi muku albarka. Mujahid ashe dai ƴar aikin ƙanwarka ce ta jini, yanzu dai sai a rage kiyayyar da cin zalin da akeyi mata" MJ dake wani cin magani ya kalli Aneesa yaga kanta aƙasa yake. Ƙasa ƙasa ya buga mata wani uwar harara kamar zai ciro idon waje. Abby dake lura dashi yayi wani murmushi ya girgiza kai. Yara kenan, ance mugun ƙiyayya na iya juyawa mugun soyayya . Ko me Allah zaiyi nan gaba shi kaɗai yabarwa kansa sani. Miƙewa Ammi tayi tazo har gaban Innati ta tsuguna kamar me neman gafara ta haɗe hannayenta wuri ɗaya tafara neman yafiyar Innati akan abinda Amin yayiwa ƴarta, cikin dakiya da juriya Innati tayi maza takamo hannunta ta miƙar da ita tsaye tace "haba dan Allah Antyna, Ni nariga na yafe masa. Ai ƴaƴan duka namu ne. Saidai muce Allah ya shirya kuma Allah ya kiyaye gaba" da farinciki duk suka amsa Ameen. Cikin sanyin jiki kowa ya miƙe yayi part ɗinsa. Raihanah takamo hannun Aneesa da Ameera zuwa part ɗin Mamy sai washe baki takeyi, yau itama zaman kaɗaici yaƙare. Ashe dai tanada cousins mate ɗinta, gaskiya tadaina kwana aɗaki ita kaɗai daga yau. Amin kawai aka bari da MJ afalon Hajja, ya durkushe awurin ya kasa miƙewa. Sai hawaye yakeyi yana danasanin abinda ya aikata. Ashe dama talala Allah keyi masa ya ɗauka kamar priviledge dinsa ne kawai yasa yake shanawarsa. Gaskiya daga yau zai fita harkan abokansa wadda sune sukayi influencing dinsa cikin wannan mummunan rayuwar. Shi kansa bazai iya cewa ga adadin matan dayayi lalata dasu ba. Cikin fushin da har yanzu bai subsiding ba MJ yace "mu friend, ka tashi kabar mun wurinnan, seeing you alone irritates me, kar ka ƙara shiga hannuna, stupid kawai wadda baisan ciwon kansa ba. Dama idan kasan akwai reminant din banzan tunanin nan aranka to tun wuri ka fidda mata muyi maka aure, cos it won't be funny idan wani case irin haka ya ƙara bijrowa. Shashasha kawai" jiki ba ƙwari saboda mazgar dayasha ya mike yana ɗingishi, ga kayan jikinsa farare ne duk sun ɓaci da jini. Kallon bayansa MJ yayi ya taɓe baki yaja tsaki sannan yacigaba da abinda yake yi a system. Da ƙyar muka samu nida Raihanah muka kwantarwa Ameera da hankali ta hanyar janta da hira. Saidai amarya ta kasance uhmm u'ummm an duk ta faɗa duniyar tunani, wasu lokutan har hawaye take yi. Muna nan zaune muna hira saiga Ammi ta shigo fuskarta ɗauke da ɗan damuwa, Ameera na ganinta taɗan saki ranta, bataso kwata kwata ta gane cewa har yanzu cikin damuwa take. Zama Ammi tayi ta kamo hannun Ameera cikin kulawa tace " ƴata, dan Allah inaso ki ɗaukeni a matsayin uwa. Duk wata damuwarki da zaki faɗawa innatinki inaso ki ɗaukeni nima a matsayin mai ciremiki baƙinciki. Kiyi kokari ki sake jikinki dani, abun dazai faru yariga ya faru, kuma nayi miki alƙawari Amin bazai taɓa shiga sabgarki ba matsayin kina gidannan. Zan baki duk wata kulawa dakike buqata. Tare zamuyi rainon wannan cikin har lokacin haifansa yazo kinji"? Hawaye na gangarowa daga idon Ameera ta gyaɗa kai. Shafa kanta Ammi tayi tace Allah yayi miki albarka. Duk suka amsa da Ameen. Bayan fitan Ammi taɗan sake har sukayi hira da ƴan uwannata zuwa lokacin Sallah kowa ya miƙe dan gabatarwa. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Yau sati ɗaya kenan da dawowarsu Innati gidannan. Babu wata kulawa da bamu samu, har ɗaki aka canza mana. Raihanah tace lallai ita saidai a expanding daƙinta ni na dawo muna kwana tare. Hakan kuwa akayi, an ƙara kayaki aɗakin inda aka samana babban gado mai kyan gaske. Ga wardrobe da Abby yasa nima ayi mun tawa kuma yasa Mamy ta ɗinko mun sabobbin kaya masu kyau da tsadan. Ya Isma'il ba'a magana, saidai idan baya gari amma kullum gidan Mamy yake yini dake shi ba'a gidan yake kwana ba akwai gidansa dake can gaban gidan Abby. Tun ina jin kunya idan yasa Raihanah takirani har ma daina ji, wasu lokutan ma ni da kaina nake zuwa inda muke zama shi yazo yasameni awurin. Yau ma kamar kullum ina zaune wurin shan iskan ina jiran Ya Isma'il dan ya cemun zai zo nan bada jimawa ba. Wayar Raihanah ne ahannuna ina kallon videos a Instagram bansan lokacin dayazo ba sai kawai jinayi an take mun ƙafata da ƙarfin gaske. Cikin jin zafi na yanka ihu sai asannan na ɗago na kalli wannan mara imanin. Ko ajikinsa haka ya wuceni ya zauna a ɗayan kujeran dake kallona. Ƙasa ƙasa na murguɗa masa baki tunda nasan idan nayi wata magana da kaɗan bai fasa mini bakin ba danshi mugune bana wasa ba. " Babu abinda mutum yasani sai mugunta, shiyasa kullum ake cikin tamƙe fuska ba farin jini. Ayita cin zalin mutum ba dalili..." Shiru nayi da sauri ina zaro ido waje, buuuu rabin zagi😂 Ashe dai ba'a zuciya nake magana ba. Ɗagowa nayi na kalli gefen dayake zama naga shima idonsa karr yake akaina. Fuskarnan tasa tamau kamar baƙin hadari, ina ganin ya miƙe nima na miƙe da sauri ina zaro ido waje, ganin yayo kaina a sukwane nabar wurin ina fallewa kamar ana ƙara mun iska a kafata. Baiyi gigin binta ba, sai girgiza kansa dayayi ya harari hanyar data bi, "this girl has got some nerves. Ta rainani dayawa, saina nuna mata the perfect place where she belongs. Stupid kawai". Bai ida zama ba saiga Ismail ya zo. Wani uwar harara ya banka masa yaja doguwar tsaki yace "aikin kenan, kabi ka nanewa ƙaramar yarinya kamar chewing gum. Saita fara rainaka zaka gane ai" ƴar dariya Isma'il yayi, lallai MJ case ne. Bai ce masa komai ba ya ciro wayarsa a aljuhu ya dialling numbern Raihanah, bugu biyu Aneesa ta ɗauka. Jin itace yasa shi sani lumshe ido cikin soft voice kamar ƙaramin yaro yace " sweetheart kin barni azaune inata jiranki kamar zanyi kuka uhmmm uhmmm" ya ƙarisa da shagwaba kamar Aneesan na gabansa. Wannan abun da yayi ba ƙaramin ɓatawa MUJAHID rai yayi ba, yaza'ayi soja Kuma ƙaton namiji dashi ya tsaya yana yiwa ƴar ƙwaila shagwaba, what a shame and slap on his face. Minti biyu da gama wayar saigata ta fito simi simi wannan karon harda hijabi kamar ta Allah sai wani sunne kai ta keyi. Dake tasan tayi laifi ko kallon gefen Mujahid batayiba, zama tayi a kujerar da Isma'il ya zauna ta gaida shi. Cikeda kulawa ya amsa mata yace " sweetheart baki gaida Babban Yaya ba" ƙasa ƙasa ta kalleshi ta cunno baki gaba tace "toh ai kona gaidashi ba amsawa yake ba" da mamaki MJ ya ɗago ya kelleta, yaushe yarinyar nan tayi baki har takeyi masa ƙarya ( MJ aji tsoron Allah 🙄🙄) kauda kai yayi daga kansu yacigaba da abunda yakeyi awayarsa. Su Alhaji Isma'il an cire kunya sai zuba love akeyi, wasu kalaman idan ya faɗa sai MJ ya ɗago ya kalleshi yaga anya wannan Isma'il ne da soyayya bata dameshi ba, toh wa ya koya masa irin wannan flaws dayake zubawa ƴar ƙwailannan. Ƙasa ƙasa yace "munafiki, ayi tayi kamar na Allah amma deep down ɗan bariki ne". Sun daɗe suna hiransu kafin suka miƙe suka shiga gida tare suka bar Oga awurin yana tada jijiyoyin wuya akan abinda bai shafeshi ba........ Kuyi haquri wannan short page ne, yau ban samu na zauna sosai ba shi yasa banyi posting da wuri ba. Ga wannan ayi manage. I love Y'all 😽 😽 ❤️ Like Comment And share fisabilillah 🙏🙏 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 46_50 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Lokacin da cikin Ameera ya kai watansa huɗu harya ɗan fara tasawa, kullum tana part ɗin Hajja babu inda take zuwa. Makarantar ma ta daina zuwa sai ta aihu. Babu abinda Innati batayiba dan taga Ameera ta sake amma sam kullum cikin ƙunci take. Hajja ma tayi iya bakin ƙoƙarinta duk a banza. Aneesa ce kawai ke iyasata murmushi idan suna ɗan hira wasu lokutan. Yau Innati ta raka Hajja asibiti, su Aneesa kuma sunje makaranta itada Raihanah. Dan yanzu Abby yasata amakaranta gaba ɗayansu su ukun suna haji na uku wadda kuma suna shirye shiryen rubuta WAEC da JAMB. Zaune take a wurin shan iskan gidan tana ƙurban pineapple juice da chocolate cookies ɗinta cikin kwanciyar hankali. Taƙara kyau da haske tayi ƙiba Masha Allah. Wani irin ƙamshin turare taji wadda yayi mata daɗi sosai amma kuma hakan baisa aman datakeji ya koma ba, da gudun gaske tayi wurin flowers din da aka kewaye wurin dashi tadinga amai ba ƙaƙƙautawa. Amin da gaba ɗaya ya fita hayyacinsa ya tsaya yana kallonta kamar yaje ya taimaka mata amma babu hali, kamar kullum ne idan ya zo inda take to kenan ranan babu zaman lafiya, ta dinga zaginsa kenan tana cin mutuncinsu kamar ba ɗan Adam ba. Duk ya rame ya ƙara duhu sai hanci da ido, makarantar ma ya daina zuwa. Numbersa dayasan abokansa sun san shi dashi duk ya canza. Duk wani abun dayasan zai iya alaƙantashi da mata duk ya share awayarsa. Yanzu kam sallah akan lokaci yakeyinsa ba fashi, kowani dare sallan nafila ba'a magana. Kuma yana iya ƙoƙarinsa wurin ganin ya shawo kan Ameera ta yafe masa, shi burinsa kenan. Koda ace babu soyayya tsakaninsu amma dai suriƙa mutunci tunda su ƴan uwan junane. Gashi Abby da Ammi duk sun fita harkansa. Wacce yake tunanin ma zata taimaka masa wurin shawo kan Ameera itama ya ɓata kansa a wurinta. Aneesa ta tsaneshi kamar dai yadda Ameera ta tsaneshi. Wasu lokutan ma itace take zuga Ameera tayi nesa dashi. Su Babban Yaya dasu Isma'il suma sun daina magana dashi, duk kuwa yadda zai gaidasu saidai kawai su gyaɗa masa kai amma babu batun magana a tsakaninsu. Wannan abun ba ƙaramin damunsa yake ba, ace kaida ƴan uwanka kazama bare babu mai son alaƙanta kansa dakai. Wasu zafafan hawaye ne suka gangaro daga idanunsa. Jin iskan mutum ya wuce ta gefensa yasashi dawowa daga tunanin dayakeyi. Can da nisa ya hango Ameera ta wuce kamar batasan da tsayuwansa awurin ba. Girgiza kai yayi ya furzar da iska mai zafi daga bakinsa ya zauna akan kujerar data tashi yakafe wuri ɗaya da ido ko ƙyaftawa bayayi. 🌷🌷🌷🌷🌷 Kwance take kan rugujajjen taburmanta sai tari take ba kakkautawa, duk ta fita hayyacinta kamar mai ciwon ƙanjamau. Idonnan gwala gwala, ga ƙashin wuya sun fito raɗau raɗau jikinta sam ba ƙwari. Kwana biyu kenan take wani irin amai da gudawa tun abu na fitowa cikin aman har ya koma ƙaƙari kawai take iya yi dan babu komai acikinnata. Gudawan kuwa saidai taje bayi tayita nishi kamar mai aihuwa amma babu komai dake fitowa, yanzu haka kasa zama tayi tsabar zafin da wurin keyi mata, har tsagewa yayi. Abba ne ya shigo da gudu da ɗan leda ahannunsa shima gaba ɗaya ya zabge kamar bashi ba, jikinnan ya sauka sosai sai yawo yake ariga kamar kwarangwal. Zama yayi kusada Goggo yana sannu Goggo sannu amma bata iya amsa masa saidai kawai ta gyaɗa kai alaman yawwa. Yadda rayuwa ta juya musu abun tsoro ne, komai sun rasashi tundaga kan aikin Abba, wasu abubuwan gidan ma sun siyar dasu ne dan kawai su samu na afawa abaki. Kusan sati ɗaya kenan kowani rana garin kwaki suke sha mara sugar. Abokan Abba masu ci daga jikinsa suma duk sun guje masa, inda suke zama da a majalisa sun daina zama awurin dan kawai saboda Abba. Komai ya juya musu kamar anyi musu asiri, amma sam ba haka bane. Alhakin bayin Allah ne ke bibiyarsu tun anan duniya. Baba Auwalu ma ya guje ma mahaifiyarsa balle kuma ɗan uwansa. Idan suka kirashi sai yagani kuma yaƙi amsawa. Yazo daga baya ma ya canza layi dan kawai saboda suna daina damunsa. A kullum Goggo saitayi kukan Innati, tana tsoron ta mutu bata nemi yafiyar wannan baiwar Allahn da ƴaƴanta ba. Tabbas sun muzguna musu sosai a rayuwannan, kuma wannan sakamakonsu ne daga Allah. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Mun gama last period kenan a makaranta bayan an buga ƙararrawa na closing time. Uniform ɗinmu mai kyau dashi, dogon tommy skirt ne wadda yaɗan wuce guiwa na kaɗan sai farar riga long sleeve da ɗan gajeren hijabi wadda tsawonsa iya cikina ne ssi dogon socks fari wadda ya kai har guiwa na. Class ɗinmu ɗaya da Raihanah da Mustapha, sai dai ni ina ɓangaren science ne, Raihanah tana arts, Mustapha kuma yana commercial. Na dage sosai da karatuna, wasu abubuwan dabana ganewa idan na dawo gida Ya Isma'il shike koya mun. Yau kusan watanni biyu kenan da bana ganin mugun mutuminnan agida, hakan kuwa ba ƙaramin daɗi yayi mun ba. Har suna Hajja ta samun wai ƙawar Mujahid. Ƙarfe biyar saura driver ɗinmu yazo ya ɗaukemu ya maidamu gida. Da sauri nayi part din Hajja dan na duba Ameera, nasan yanzu haka bataci abinci ba jirana take. Aikuwa kamar na sani, ina shiga ɗakin Innati na samu Innati sai masifa take mata akan rashin cin abincinnan nata. Itako wani ɓata rai tayi tace "Innati kullum sai kiyita cewa naci abinci saboda yaro yayi girma, Ni wlh banƙi ma idan na zauna da yunwa yaron ya mutu ba, ni banga amfanin zama da cikin da baida uba ba" tauuu Innati ta ɗauketa da wani irin gigitacciyar mari wadda yasa dakin gaba ɗaya ya amsa. Cikin fushi tace "naga alama Ameera kinaso fushina ya kasance dake, ke wani irin wawuyar yarinya ce. Toh dan Allah karkici abincin, ki mutu. Yarinya sai shegen kafiyar tsiya kamar dangin fir'auna" tana gama faɗin haka ta aje mata abincin saman gado ta fice daga ɗakin ko kallon Aneesa dake tsaye batayiba. Cikin sanyin jiki na ƙaraso wurin gadon na zauna kusada Ameera daketa kuka, kamo hannunta nayi cikin kulawa nace "haba Ameera, ke kullum kinfiso kiga ran Innati na bacewa akan wannan maganar. Anfa riga an hukunta mai laifi, kuma har yanzu yana karɓan hukunci mai zafi. To danme bazakiyiwa kanki ihsani dakeda yaron cikinki ba. Dan Allah ki taimaka ki riƙa sake ranki ko dan ran Innati itama ya kwanta" Ameera ba dai zuciya ba, duk wannan maganar da Aneesa keyi mata kamar da iska take yi. Miƙewa tayi cikin fushi ta shige bayi ta bugo ƙofan ɗa karfin gaske. Girgiza kai Aneesa tayi tace "Ameera Allah yasa ki gane". Hajja na zaune a falo saiga Innati tafito fuuu daga ɗakinta rai aɓace. Ganin ɓacin rai afuskar Innati yasa Hajja tambayarta meya faru, har hawaye na taruwa a idonta tace "Hajja, na rasa mezanyiwa Ameera. Yarinyar gaba ɗaya ta gwammace da halaƙa kanta. Kenan shi dan Adam Allah bazai jarabci bawa ya ɗaukeshi da kyakyyawan zuciya ba. Akanta aka fara yin haka ne. Ni dai gaskiya bazan ƙara yi mata magana ba, ilduk abinda taga yayi mata daidai tayi" "uh'um Nadeen, ke kam bazaki gane abinda yarinyar nan ke ciki ba, kawai mu bita asannu har Allah ya sauketa lafiya. Babu abinda take buqata yanzu kamar kulawanmu, ki daina yi mata zafi da faɗa, baisan abinda ke damunta" ajiyar zuciya Innati tayi tace Allah yasa mu dace. Haka suka cigaba da hira can Innati tace "wai nikam nace Mujahid yanada mata ne"? Shiru Hajja tayi kamar mai tunanin wani abu tace "uhmm, Labarin da tsawo yake, amma dai barina baki takaice. Yaronnan yasha wahala arayuwarsa, Allah ne kawai yayi zai kai har wannan lokacin." Five years Back 🔙 Alokacin Mujahid na zama a US bayan yagama karatunsa harya fara aiki. A wani rana suka tafi national conference na cyber security a Florida USA. Mujahid alokacin mutum ne mai yawan son jama'a, baida matsala da kowa. Ya iya trusting mutum without any doubt, akwai friend ɗinsa kuma colleague sunansa Jaybash. Jaybash shine best friend ɗin Mujahid, komai tare sukeyinsa. Jaybash shiya haɗashi da wata cousine ɗinsa Neehal. Yarinya son kowa ƙin wadda ya rasa. Neehal yarinyace ƴar kimanin ashirin da ɗaya alokacin. Kyakkyawa ce na asali, iyayenta ƴan India ne amma suna zama a US. Tanada tarin ilimin boko amma zero percent aɓangaren addini. Akwaita da son kwalliya, wasu lokutan idan tayi shiri mutum bazai taɓa cewa ƴarinyar musulma bace. Tunda ta ƙyallara idanunta akan Mujahid tace shikenan idan bashiba saidai rijiya. Toh a wannan conference dinnan da Jaybash ya haɗasu yasa suka ɗan saba suka zama close friends da Mujahid. Shi a ƙawa kawai ya ɗauketa, itakuwa nufinta akansa dabanne. Tun baya kula advances ɗinta gareshi har ya fara saboda tana bashi support, tana bashi duk wani care dazaisa kaji mutum ya kwanta ma arai. Tasha wahala kafin tasamu ta shawo kan Mujahid harya faɗa tarkon ƙaunarta. Sosai suke soyayyarsu babu kama hannun yaro. A lokacin da ya bijirowa su Abby da maganan auren dakuma wacce yakeso ya aura, ba ƙaramin tashin hankali akayi ba. Hajja da Abby basu amince ba dan a yadda sukaga yarinyar sam sam bata dace da ɗansu ba. Tsoronsu shine kada wata rana tayi sanadiyyar raba kan ahalin. Ance Love is blind, shi Mujahid duk wannan abun da ake hango masa sam bai gani ba. Yace yaji ya gani kuma ahaka yake son Neehal. Daga ƙarshe dai bayan anyi duk wata ƙoƙari wurin ganin anshawo kansa amma yaci tura akace kawai ayi musu auren tareda fatan Alkhairi. Shekara ta farko bayan aurensu Neehal ta haifo ɗansu mai tsananin kama da ita. Babu abinda ya ɗauko na Mujahid. Shiko Mujahid duk wata so na duniya ya ɗauka ya ɗorawa yaron mai suna Akeer. Suna zama cikin kwanciyar hankali da farinciki. Duk wani abu dazai farantawa Neehal Mujahid yana ƙoƙarin yaga yayi shi, duk wani abun dazai baƙanta mata shima yana ƙoƙarin ganin ya avoiding ɗinsa, soyayyar da suke wa juna abun burgewa ne ga duk wadda ya gani. Har Akeer yakai watanni shida, yaron yana ƙara girma kullum sai ƙara kama yake da mahaifiyarsa. A wani rana ne wadda gaba ɗaya ahalin Mainoma suka laƙaba masa suna da "Darkest Day of their life". Kwatsam rana ɗaya Akeer yafara ciwo ciwo ciwo yaƙi ci yaƙi cinye wa. Da aka kaishi asibiti aka ce dole sai anyi masa operation sakamakon wani tumoil daya fito masa a ƙwaƙwalwa. Ba ƙaramin tashin Hankali Mujahid ya shiga ba jin yaronsa mafi soyuwa agareshi ya kamu da irin wannan deadly ciwon. Haka itama Neehal sosai tashiga firgici, da ƙyar Mujahid yasamu ya kwantar mata da hankali. Aranan da za'ayi wa Akeer operation,likitoci sukayi demanding jini daga ɗaya acikin iyayennasa. Abun mamaki da aka gwada Neehal jininta bai matching ba. Babu wadda ya kawo komai ransa, akace za'a gwada na Mujahid. Wannan karon kam tsorone ƙarara afuskar Neehal kamar dai mara gaskiya. Duk yadda zata yi ta hana ayi wa Mujahid test amma batayi nasara ba. Mujahid ya shiga aka gwada jininsa ko zai matching amma babban tashin hankali shine da result yafito aka gano cewa kwata kwata ma chromosomes ɗinsa babu shi ajinin Akeer, hakan yana nufin cewa akwai matsala. Idan maganar chromosome yataso dole maganan DNA ya biyo baya. Sosai ya ƙara shiga cikin firgici, da farko yaso yaƙi amma Abby yace wa doctors din ayi kawai. Kusan thirty minutes kowa na zaune anyi shiru. Neehal dake ta kai komo ta kasa sukuni sai addu'a take a zuciyarta kada abinda take tunani yazamo gaskiya. Wata nurse ce ta fito ta mikawa Mujahid result ɗin. Da sauri ya buɗe, su Abby duk sun matsa suga menene sakamakon amma kamar an dasa dutse. Ya kafe idonsa akan paper ya kasa koda motsa hannunsa ne, zirrr saiga hawaye na ɗigowa daga idonsa yana sauka akan paper. Suna cikin haka Jaybash yazo, halin dayaga abokinnasa acikine yabashi tsoro. Su Abby ma kowa yayi kansa ana tambayarsa menene, Isma'il ne yayi saurin karɓan papern dan karanta mene aciki daya sanya MJ kuka. Tashin hankali wadda ba'a sa masa rana. Neehal da tariga tasan menene acikin papern ta durkushe awurin sai kuka. Ita kanta batasan ya hakan ta faru ba. Kuma wlh babu wadda ya taɓa nemanta sai mutum ɗaya "JAYBASH", kenan yana nufin Akeer yaron Jaybash ne ba na Mujahid ba. Ohhh God. Suna ciki da haka likitoci suka fito da sauri suka sanar dasu news ɗin daya ƙara kiɗimar da duniyarsu. Akeer yace ga garinku nan. Jin wannan mummunan News din yasa Mujahid miƙewa yasaki wani irin kuka da gaba ɗaya saida mutane suka taru awurin suna kallon yadda babban matashi irinsa yake kuka kamar ƙaramin yaro. Da sauri Neehal ta taso ɗanta riƙe mijinnata ya daka mata tsawa da bai taɓa yi ba tun farkon haɗuwarsa yace mata "whyyy Neehal, whyyy? Menayi miki wadda na cancanci kinsakamun da wannan irin mummunan abun, nace menayi miki"?? Itama cikin kuka tace "dan Allah dear.."? Bata rufe baki ba Abby ya ɗauketa da wani irin gigitacciyar mari yace "kika kuma kiransa dear sai dai kisa haƙoran karfe abakinki dan saina rugurguza miki wadda kike dasu" durƙusawa tayi awurin tana kuka tace "dan Allah kuyafe mun, ba laifi na bane, Mujahid.." Idonsa dayayi jaa zur yace "who's the Father? I said who's the damn Father "? Ɗago ido tayi ta kalli Jaybash daya matsa can gefe yana zuruzuru da ido, daka kalleshi kaga rashin gaskiya ƙarara a idonnasa. Mamy ta saki salati tace " amma Neehal kin cucemu, kin cuci rayuwar ɗana. Ki jira sakayyarki awurin Allah. Kai kuma Jay, idan mutum yanada aboki irinka gara ya gwammace ya zauna da makiyinsa tunda yasan kiyayya ce a tsakaninka da mutum ba abota ba. Kaje dakai da ita da gawan ɗanku, Allah ya isar mana". Tsabar mamaki Mujahid ya kasa cewa komai, har Neehal da Jaybash suka bar asibitin bai bar kallonta ba, this is the most darkest day in his life. Kwata kwata soyayya batayi masa rana ba. He has totally lost trust in love. Har yayi watanni uku gaba ɗaya ya canza ya rikide yakoma kamar ba Mujahid da kowa yasani ba mai yawan fara'a. Da wuya kaga yayi murmushi ko dariya, inko yayi hakan tona mugunta ne. Damuwar dayasawa ransa shine ya haddasa masa hypertension Kuma ya jefa shi cikin depression. He became so consumed to his self. Baya shiga cikin mutane, ya daina yarda da kowa idan ba family member ɗinsa ba. Tundaga ranan bai ƙara kallon wata mace ba da maganan soyayya, kallon mata yake dukansu haka suke, baida aboki. Shi yasa yanzu yasa aikinsa kaɗai a gabansa bai bawa kansa wani lokaci dazai zauna yayita tunani. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Back to story. Sosai Innati ta tausaya wa Mujahid, ashe dai shima yasha ta arayuwa. Allah sarki bawan Allah, Allah ya kawo masa wacce zata rikeshi da amana. Ina tsaye tun lokacin da Hajja tafara bawa Innati labari. Inata mamaki wai dama abaya can mugunnan na dariya ashe, lallai kam. Har imagination nakeyi yadda fuskarsa zata kasance idan da yana dariya. Ni kwata kwata bai wani bani tausayi ba, saima Allah ya ƙara nace azuciyata na wuce part din Mamy. Ɗaki na shiga nayi wanka sannan na yi Sallahn maghrib dan har an idar. Fitowa mukayi nida Raihanah zuwa farfaɗan gida wurin swimming pool wadda aka ƙawata wurin ruwan da wasu irin fitillu masu hasken gaske, wurin yayi kyau. Ga iska mai daɗin gaske yana kaɗawa ahankali. Zama mukayi nida ita muka sanya kafafu cikin ruwan muna wasa. Can Raihanah ta debi ruwan ta watsa mun afuska, nima nayi haka. Taƙara yi, ina kai hannu zan ɗebo wani naji kamar anjani cikin ruwa sai kawai ganina nayi aciki dumu dumu. Ga ruwan da zurfi bana wasa ba, Raihanah da itama bata iya fito ba tayi saurin miƙewa tayi cikin gida da gudu wai donta kira wani yazo ya ceceni. Bubbuga hannu nakeyi a ruwan ina neman ceto, har gani nake kamar lahira tafara yi mun sallama. Gashi inata shaƙan ruwa kamar zan shiɗe. Babu kowa daya fito har kusan mintina biyu. Daga lokacin ban ƙara sanin inda nake ba. Sai ji nayi kawai gaba ɗaya na lume cikin ruwan ko kaina bashi asama. Dawowarsa kenan daga masallaci, agajiye yake saboda saukan yamma yayi, har yazo zai shiga cikin gida yaga kamar kumfa ke tashi acikin ruwan swimming pool. Da sauri ya ƙarasa wurin, ya leka, ai kuwa sai gani yayi gashin macene ke rito asama gaba ɗaya gangan jikinta na cikin ruwan. Baisan lokacin daya tuɓe jallabiyarsa ba yarage dagashi sai dogon wando ya faɗa cikin ruwan. Alokacin daya fito da ita tariga ta sume. Hannu yasa ya ɗanne cikinta amma ko motsi batayi ba. Ya ƙara dannawa amma still bata motsa ba. Last option ɗin dayake dashi shine yayi mouth rescue. Runtse ido yayi ya sa hannu yasa hannu ya rufe hancinta sannan ahankali yakai bakinsa kan nata yabata iska ta bakin cikin ƙwarewa. Wani irin numfashi taja sai tafara furzar da ruwan daga bakinta direct afuskarsa. Matsawa baya yayi yana yatsina fuska daidai su Mamy sun ƙaraso wurin itada Isma'il da Raihanah. Ganinta sukayi akwance aƙasa sai tari take yi. Da sauri Isma'il ya ƙaraso wurinta yasa hannu ya dagata cak kamar baby yayi cikin gida da ita, juyowa tayi awahalce tana kallonsa, yana tsugunne awurin bai miƙe ba shima itaɗin yake kallo da wani irin cold expression a fuskarsa. Murmushi Raihanah tayi tace " sannu Babban Yaya" harara ya hurga mata ya miƙe yana tsane gashin kansa daya jiƙe sharƙaf ya matse ya wuce yabarta awurin. Yana shigowa yasamu Isma'il sai murza mata hannu yake tana kwance saman doguwar sofa sai numfashi take sama sama. Ko kallon gefensu baiyi ba ya wuce sama abunsa. Ƙarfe tara ya sauko ƙasa ya tadda Mamy ne da Abby kaɗai a falon. Gaidasu yayi shima ya nemi wuri ya zauna yana kallon TV, coffee Mamy ta haɗa masa ta bashi don tasan shima ma'abocin shan sa ne kamar Abby. Hira yayi hira Mamy tace Abby " dear, gsky Yakamata afara shirin auren yarannan, kullum sai soyayya suke kamar zasu cinye junansu, gara kawai ayi musu auren idan yaso saitayi graduation agidansa" Abby dabaisan wa Mamy ke magana akai ba yace "wasu yara kenan"? Ƴar dariya Mamy tayi tace "dear kenan, Isma'il da Aneesa mana" Mujahid daya kai coffee bakinsa yana ƙurba baisan lokacin daya ƙware ba jin sunan wadda aka ambata.... Chakwakiya 🙆🙆🙆 Like Comment And Share 🙏🙏🙏 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 51_55 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Kallonsa Mamy da Abby sukayi cikeda mamaki, ya daga maganan auren kannennasa kawai zai shaƙe. Tari yake yi ba ƙaƙƙautawa har abun yafaraa basu tsoro Mamy tayi saurin kawo masa ruwa yasha. Abby Yana yi masa sannu. Har idonsa yayi jaa, saida abun ya lafa masa sannan Abby ya tambayeshi ko lafiya. Girgiza kai yayi ya sosa ƙeya yace "Abby kawai gani nake kamar ita yarinyar tayi ƙarama ace za'a yi mata aure tun yanzu. How old is she"? Tsaki Mamy taja tace "kaji Babana da wani shirme, to ni bari kaji na faɗa ma ina shekara 16 nayi aure kuma na haifeka ina 17, to saikace child abuse kenan iyayena sukayi? Kuma ba kai bane kacewa Amin zai auri Ameera, how old is Ameera ba 16 bace yanzu? Ɗan sosa ƙeya yayi cikeda kunya yace "Mamy her situation is different.." murmushi Abby yayi, idan ba karya zuciyarsa keyi masa ba kamar yaso ya gano wani abu a wurin Mujahid, amma dai bari yayi shiru ya zuba masa ido yaga gudun ruwansa. Kwata kwata ma yaji zaman falon ya ishe shi, miƙewa yayi ya musu saida safe ya wuce ɗakinsa. Yana shiga falonsa ya rufe kofa yaja wani dogon tsaki kamar bakinsa zai manne da ƙofan ɗakinsa yace " fisabilillah just how old is that gurl dasu Mamy keso suyi mata aure. Ni banmaga laifinsu ba, shi Isma'il daya tsaya yana bibiyar ƴar karamar yarinya. Toh ni inama ruwana. Why should I bother myself, at least zata tafi zan huta da rashin kunyarta" wani abu azuciyarsa yace (MJ yaushe ta taɓa yi maka rashin kunya🤔) shrugging shoulder ɗinsa yayi ya wuce bedroom ɗinsa. Koda dare kasa bacci yayi sai faman juye juye yake yi agadonnasa. To meyasa ma abun yadameshi. Dama yasani yabarta acikin swimming pool dinnan ne ta mutu kowa ya huta🙆🙆. Haka yayi tayi har Bacci ya ɗaukeshi. Da asuba daya tashi yayi mamakin daren jiya kwata kwata baiyi tunanin Neehal ba, chabbb aiki na gaba. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Nagama shiri kafin Raihanah, hijabina na hannu na kama gashina da ribbon nasa ta kitsa min jelar bayan na shafa masa mayuka masu ƙamshin gaske. Fitowa nayi rataye da school bag ɗina na fito falo. Babu kowa dan haka na wuce dinning zanyi breakfast. Serving kaina nayi Irish da fish pepper soup sai black tea na zauna zan fara ci kawai naji anyi sama da plate ɗin. Juyawa nayi na gansa akaina riƙe da plate ɗin abincina ya tsoma hannu aciki yana ci hankali kwance. Raina idan yayi dubu to ya ɓaci, wannan wani irin abu NE fisabilillah. Saikace abinci ya ƙare da bazai iya sa nasa ba, dana lura dai kawai yana neman magana ne na share shi na dau wani plate ɗin nakara serving kaina, ko kulashi banyi ba ya dau kofin Black tea ɗina yafara ƙurba, sip ɗaya yayi ya furzar dashi yace " kirage shan sugar, sugannan yayi yawa" ƙasa ƙasa nace " ai dama ba kai na haɗa mawa ba" ji nayi yace " how i wish I didn't save you from drowning in that swimming pool, yarinya sai shegen rashin kunya kamar tare aka haifoku" rai aɓace na miƙe na kalleshi nace " nidai banida rashin kunya tunda ba haka Innati ta koya mun ba. Ai idan Babba bai kama girmansa ba dolene ƙarami ya hau ya take" ban jira me zai ce ba kawai na dau jakata da hijabi nayi gaba har lokacin Raihanah bata fito ba. Yana tsaye awurin ya daskare yama rasa mezaice, gyaɗa kai yayi yace "ungrateful human being, na ceceki amma ko godiya baki iya yi ba" Raihanah da fitowar ta kenan ta iske shi yana magana shi kaɗai tace "Babban Yaya wai dani kakeyi ne"? Wani uban harara ya watsa mata ya wuce, tabbas ko ba'a faɗa mata ba tasan dawa yake don kuwa ƙamshin turaren Aneesa na nan afalon har lokacin. Murmushi tayi tace "kar dai kar dai Babban Yaya ya fola, kai amma da wasannan yayi daɗin kallo". Da yamma da muka tashi Ya Isma'il dakansa yazo ɗaukanmu. Bai wuce damu gida direct ba yakaimu cold stone yayita kwaso mana kayan maƙulashe nida Raihanah hardana Ameera. Damuka fito kuma ya ɗau wani hanya daban, munyi tafiya mai nesa kafin muka tsaya a wani babban shago inda naga anrubuta " Tecno", fitowa mukayi gaba ɗayanmu muka shiga cikin shagon. Babban shago ne wadda aka cikashi da wayoyi manya manya na zamani masu kyau da tsadan gaske. Na kasa rufe baki, sai ji nake inama na mallaki waya guda ai dana ji daɗi, nima nayita kashe hotuna yadda nake ganin Raihanah tana yi. Kamo hannuna Raihanah tayi muka bi bayan Ya Isma'il. Salesboy Ya Isma'il yayiwa magana naga yafara fidda wayoyi different designs Yana jerawa saman table ɗin. Kusan kala shida ya aje, kallona Ya Isma'il yayi da murmushi afuskarsa yace "sweetheart ki zaɓi wadda ya miki acikin wayoyinnan" baki sakato na tsaya ina kallonsa, ni yaushe nakeda hurumin na zaɓi abinda nakeso bayan ba haka aka sabar mun ba. Ai ni kawai duk abinda aka bani inaso ne, girgiza kai nayi nace "a'a Ya Isma'il kowanne ka ɗauka mun Allah inaso" danaga dai kamar ransa bai so haka ba kawai nasa hannu kan wata wayar wadda naga anrubuta "Camon 20 premier ", saida ya kara tabbatar cewa shiɗin nakeso kafin yabada katinsa aka zari kuɗin wayar. Anan akayi mun registern layi na MTN, da farinciki muka fito daga shagon ina washe baki, nima yau nayi waya. Ai ina zuwa gida zan nunawa Innati. Muna isowa gida har anfara kiran Sallan maghrib dan mun jima awaje. Part ɗin Hajja na tafi inda duk na samesu afalo harda wannan arrogant man ɗin suna ɗan hira amma shi hankalinsa na kan system kamar kullum. Gaidasu mukayi nida Raihanah ko kallon gefensa banyi ba, ni tuni na warkar da kaina daga gaidashi tunda ba amsawa yake ba. Nunawa Innati sabuwar wayata nayi kuma na faɗa mata wadda ya siyomun. Hajja ma ta karɓi wayar ta duba duk sukasa albarka sannan sukace na ƙara yiwa Ya Isma'il godiya. Raihanah dake tsaye agefen Innati ta saci kallon MJ, yayi wani kicin kicin da fuska sai jefa wa wayan harara yake kamar zai yi bindiga. Batasan lokacin da dariya ya kubce mata ba, bulusi, wlh kishi ne ƙarara a fuskar Babban Yaya. Kai amma Alhamdulillah, Finally ya faɗa tarkon son wata bayan shekara biyar. Suna haɗa ido tayi saurin juya kai tana kunshe kariyar da cinta aciki. Da daddare, bayan munyi shirin kwanciya har ma munyi addu'a naji vibration ɗin wayata. Dubawa nayi naga " My love" asaman screen ɗin, murmushi nayi na amsa kiran. Cikeda soyayyar juna muke waya. Itako Raihanah sai dariya take, akwai matches agidan Abby, wa da ƙani suna son mace ɗaya ya abun zai kasance kenan. "Sweetheart, gobe insha Allah zanyi tafiya zuwa wani taron mu na sojoji. Da na dawo zanyiwa Abby magana sai afara shirye shiryen aurenmu " wani kunya naji ya rufeni har na sa hannu na rufe fuskata kamar yana wurin. Allah ya kaimu kawai na iya cewa sannan muka yi sallama nayi addu'an bacci na kwanta. Kamar yadda Ya Ismail ya faɗa, kwana biyar yayi a tafiyar da yace zaiyi. Yana dawowa ya sami Abby yayi masa magana. Nan Abby bai musa masa ba ya amince sannan yace shi da kansa zaije Adamawa ya nemawa Ya Isma'il ɗin auren Aneesa awurin Abba. Da ya faɗawa Mujahid maganar neman auren, duk da bai nuna ya damu ko kuma yanada wata matsala ba amma tabbas ranan sai da yaji kamar yasa hannu akai yayita ihu ko zaiji sauƙin abinda yake ji azuciyarsa. Da Innati akayi shirin tafiya Adamawar harda Hajja. Da farko Mujahid baiso yabisu ba amma ganin idan yayi haka Abby bazaiji daɗi ba ya amince za'ayi tafiyar dashi. Tundaga ranan kuma ya fita aharkar Aneesa, ya daina tsangwamarta. Babban abinda yake yi masa zafi shine itama ba shiga harkar sa take yi ba, infact idana taganshi afalon Mamy ko Hajja saitayi kamar he's invisible. To meyasa yake jin zafin haka bayan shima he doesn't care about her. Ranan Saturday da sassafe sukayi mota biyar uku na sojoji biyu na mutanin gida aka kama hanyar Adamawa. Gaba ɗaya mazajen gidan Abby, Mujahid, sultan, da ango Isma'il sune suka tafi. Sunyi shirin manyan kaya ba ƙaramin kyau sukayi ba. Innati tunda suka fara tafiya taji kwata kwata hankalinta ya kasa samun nutsuwa. Ƙarfe ɗaya saura suka iso cikin garin Adamawa sannan aka kama hanyar unguwar dasu Abba ke zama. Tunda suka shigo cikin unguwar yara da matasa sai faman fitowa suke suna kallon wannan danƙararrun motocin ga kuma sojoji duk sun wani tamƙe fuska kowa na riƙeda bindiga ahannu. Suna shigowa layin gidansu Abba matan layin sai leƙowa suke daga katanga wasu kuma har fitowa sukayi waje anata kalle kalle, daka kalli motocin an kasan babban mutum ya shigo gari. Agaban gidan Abba motocin sukayi parking. Tunda Hajja ta kalli Kofar gidan sai kawai ta fashe da kuka wiwi, Abby da Innati dake motar hankalinsu ya tashi suka fara yi mata tambaya, cikin kuka tace "Nadeen yanzu dama wannan gidan kike rayuwa har tsawon shekaru ashirin? Kalli irin kwangon gidannan fa wayyo ni Aneesatu, Allah ya isa tsakanina da mutanin dasuka jefaki cikin wannan halin. Yiyiyuyuiiiii" taƙara ƙara sautin kukanta, murmushi Abby yayi ya girgiza kai, Hajja rigima. Saida suka samu tayi shiru sannan aka buɗe musu Kofar motan suka fito. Haire dillaliya makwabciyar Innati tunda ta kafe Innati da ido taji aranta tabbas akwai inda tasan matar nan, tayi mata bala'in kamada Hussaina matar Zaidu saidai wannan mai kuɗice kuma tafi Hussaina haske da murmurewa. Kamar kuwa innati tasan me take tunani tace "Haire baki ganeni bane? Nicefa Hussaina matar Zaidu" cikeda mamaki Haire tace "kai dan Allah wacce Hussaina, yaushe Hussaina tayi wannan arziƙin da har zata shiga cikin wannan danƙareriyar motar" Hajja ce ta tari numfashin Haire ta hanyar cewa "to itaɗin ce, idan baki yarda ba saiki ja bakinki kiyi shiru" tsit Haire tayi da bakinta suna ta kallon ikon Allah. Yara ƴan matannan sai faman kallon samarin gidan Jenar suke suna sanyi su musamman MJ wadda yasha wankan danyan boyel yard honey colour baisa sanya hula ba amm gashin nan nasa yasha gyara ta musamman sai wani kyalli yake yi. Ango Isma'il bakinsa yakasa rufuwa, yau gashi a gidan surukanninsa. Innati ce tayi gaba da sallama abakinta ta ƙusa kai cikin gidan. Gabanta ne yayi rassss ganin Goggo cikin wani irin yanayi sai ƙaƙarin amai take yi amma takasa, Abba na gefenta yana bubbuga bayanta sai faman sannu yake yi mata. Ɗagowa Goggo tayi tana kallon baƙuwar fuskar dake tsaye abakin ƙofa. Awahalce tace "baiwar Allah wakike nema"? Innati batasan lokacin data fashe da kuka ba da sauri ta ƙaraso wurin Goggo tace "Allah sarki rayuwa, Goggo yanzu kina nufin baki ganeni ba? Nice fa Hussaina" Goggo da Abba suka kalleta da kyau, ai kuwa itace. Iko sai Allah, Abba yace "Hussaina dan Allah ina kikaje. Yanaganki ke kaɗai ina ƴaƴana" bai gama rufe baki ba saiga Hajja da Abby sun shigo suma da sallama abakinsu. Da sauri Abba ya miƙe yana kallonsu, wannan dattijuwar tabbas tayi kamada Hussaina, toh amma shi kuma namijin da wanene shi tunda bawani kama sukayi ba. Take yaji ransa ya ɓaci, badai har Hussaina tayi aure ba. Kewarta dayayi duk yaji ya kau a lokaci guda kishi ya mamayeshi. Goggo ta miƙe da ƙyar ta zauna takamo hannun Innati tafashe da kuka tace "Hussaina, na cece rayuwarki dana ƴaƴanki, dan Allah kuyafe mun. Allah na gode maka daka nuna mun Hussaina kafin na mutu, alhamdulillah" ta ɗago ta kalli Abba tace "Zaidu shimfida musu taburma su zauna mana" rai aɓace Abba ya juya ya shiga ɗakinsa ya ɗauko wani ɗan madaidaicin taburma ya shimfida wa su Abby suka zauna akai shida Hajja. Su MJ suna waje dake Abby yace su tsaya tukunna zai kirasu. Komawa Abba yayi ya zauna a Kofar dakinsa idonsa ƙyam akan Innati, gaba ɗaya ta canza masa tazama wata Babbar mace son kowa ƙin wadda ya rasa, Allah sarki ashe dai matar tasa kyakyyawa ce amma ya gaza gane hakan gashi yanzu ta zama matar wani. Goggo tace "Hussaina inasu bahaguwa, ya jikin Ameera Allah yasa dai babu wata matsala ko"? Take Innati taji komai daya faru ranan yadawo mata sabo fil, duk irin cin mutuncin dasukayi musu aranan da zasu bar gidan itada Aneesa. Hawaye na taruwa a idanunta tace " duk sunanan kalau, wannan dakike gani Goggo itace mahaifiyata. Tafiyata daga gidannan Babban Alkhairi ne agareni, Allah ya haɗani da ƴan uwana na jini. Wannan kuma Babban yayana ne, yanzu haka munzone dan neman auren Aneesa ahannun mahaifinta" jin haka yasa Abba yayi saurin gyara zama, ashe dai surukanninsa ne azaune agabansa shine yaketa yatsina fuska. Ai gara ya maintaining kansa kodan suji tausayin halin da suke ciki su taimaka su fidda su daga wannan akurkin gidan. Mutum bazai taɓa canzawa ba. Abby ya kalli yadda Abba ya canza fuskarsa immediately, murmushi kawai yayi yace " sannu inna, na gode ƙwarai da riƙe mun ƙanwata dakukayi. Allah ya biyaku" washe baki Abba yayi kamar soko yace "Allah sarki Alhaji ai yiwa kaine, Hussaina badai kirki ba, tanada biyayya, kaddara ce ta rabamu kuma gashi ta hadamu. Ni dama na daɗe da maida matata wlh. Na gane kuskure na Allah kuma ya yafe mana" wani irin kallo Hajja ta watsawa Abba yadda yake magana kamar mai tabon hankali, ita koda wasa zata bar Nadeen tadawo gidan wannan mara imanin bayan labarin da Innati tabasu akan irin rayuwar dasuka yi. Ita badon Abby yaƙi Bama wlh da anyi aurennan kawai asiri a rufe, ai ana iya canza waliyyi. Flashing Abby yayiwa su MJ sannan ya maida wayarsa ya aje. Da sallama suka shigo cikin gidan, sosai hankalin Abba ya tashi da ganin MJ kamar yasanshi a wani wuri. Wannan ai shine shugaban EFCC da ake yawan magana akai. Ikon Allah, yau shine agidansa ainun. Su Isma'il suma suka shigo duk suka gaidasu Abban, mezaiyi kuwa idan ba washe baki ba, da fara'a ya amsa musu gaisuwan idanunsa ƙyam akan MJ wadda shi duk tunaninsa shine yaron da akeso anemawa Aneesa aurensa. Innati ta girgiza kai" Zaidu bazai taɓa canzawa ba, idan ma mafarki yake akan cewa ya maida ita to gara ma tun wuri ya farka, dan ita dashi har abada walau fiddunya ko alahira. Goggo ta kalli MJ tace "ikon Allah, kalli yara kamar ba ƴan kasan hausawa ba. Kyawawa daku kamar kannen naku" Isma'il daketa sunne kai yayi murmushi, MJ ya faki idon kowa ya zabga masa uwar harara ƙasa ƙasa. Abby ne ya fara maganan abinda yakawosu, ko musawa Abba baiyi ba yace shidai baida damuwa, ai auren zumunta abune mai kyau, zumunci zai ƙara kullluwa dakyau kenan. Sunyi farin ciki matuka da Abba bai wani jujjuyasu ba( toh inashi ina juya ku bayan yaga shugaban EFCC). Shidai Abba duk kallon MJ yake a matsayin shine angon, sukuma duk basu sani ba. Bayan sungama magana Goggo taƙara neman yafiyar Innati, itako Innati tace ta yafe musu Allah ya yafe musu gaba ɗaya. Lokacin tafiya yayi Abba yaga innati tana haɗa handbag ɗinta itama, ai lokacinne ido ya raina fata. A fakaice fa yace musu ya dawo da ita amatsayin matarsa kodai basuji bane. Makudan kudade Abby, MJ da Isma'il suka aje musu wadda zai kai kimanin dubu ɗari da ƴan kai. Gefe Abba yaja Abby yace "Alhaji dan Allah wani alfarma nake nema. Atayani yiwa Hussaina magana, dan Allah ta yafemun tadawo mucigaba da zama a matsayin mata da miji. Wlh yanzu na gane kuskure na" take ran Abby ya juya yayi baƙi ƙirin. Me wannan mutumin yake nufi dasu, shi baisan kunya ma kenan ba. Yanzu har zai iya kallon idonsu yace Nadeen ta dawo gidansa, aiko sai inda ƙarfinsa ya tsaya indai haka ne. Dake Abby mutum ne wadda yasan yadda ake zama da mutane iri iri, yayi ƙoƙarin danne abinda yaki azuciyarsa kodan asamu ayi auren yarannan cikin kwanciyar hankali yace "karka damu zanyi mata magana idan mun koma gida. Duk abinda ta yanke zan jira ka na faɗa maka" godiya Abba yayi masa sannan ya rakosu har bakin kofar gidan shida Goggo dakeji kamar itama a falle da ita cikin wannan motar mai rai da motsi. Ko kallon Abba Innati bata ƙara yiba, har akayi reverse motocin suka fara tafiya. A ɗayan motan angwaye sai tsiya Sultan yakeyiwa Isma'il yana cewa " ango mai jiran gado. Kai amma Aneesa tayi Sa'a, wannan jarumi haka. Kai tabarakallah Masha Allah, Allah dai ya nuna mana" MJ yana zaune ya maida kansa ga wayarsa amma zuciyarsa wani irin ƙuna take masa. Wai yaya ne? Me ke damunsa wai, kwana biyunnan meyasa yake yawan tunanin yarinyar nan, zuciyarsa tabasa amsa "maybe you've fallen for her" baisan lokacin daya furta impossible ba har hakan yasa su sultan juyawa suka kalleshi, ko lafiya. Girgiza kai yayi kawai yacigaba da latsa wayarsa wadda shima kansa baisan meyake dannawa ba😂 Wunin yau cikin fargaba na yini, duk tunani na yana can wurin mutanen Adamawa, ko ya za'a ƙare da Abba, zai yarda yabada aurena? Ko a'a. Su Raihanah da Ameera sunata hira nikuwa na sharesu natafi duniyar tunani. Ƙaran text naji awayata nayi saurin dubawa, " our dream is finally coming true Habibty❤️" wannan shine abinda Ya Isma'il ya turo mun. Ban san lokacin dana saki ihun murna ba, wani irin farin ciki ne ya ratsani, wayyo Allah harna hangoni agidan Ya Isma'il amatsayin matarsa🙈 Sai bayan Sallan maghrib suka iso cikin garin Kano. Agajiye suka shigo gida gaba ɗayansu, sauran mutanin dake gida duk suka fito sunayi musu sannu da zuwa. Wurin motar su Abby su Raihanah suka tafi don yi musu Barka da dawowa, Hajja tace "takwara amarya, jeki kiyiwa angonki sannu da zuwa" rufe fuska tayi saboda kunya ta wuce wurin motar tasu, inda suma sai lokacin suka fito. Isma'il na ganinta ya buɗe mata hannu alaman ta taho ya rungumeta, wani haɗe rai MJ yayi yace "malam banason iskanci da tantiranci, ai ka tsaya a ɗaura auren tukunna. Mtcheeew " ya wurga musu harara dagashi Isma'il ɗin har ita Aneesan ya wuce ciki fuuu kamar zai tashi asama. Binsa da ido Sultan yayi, tunda aka fara maganar wannan auren ya lura mood ɗin Mujahid ya canza. Allah yasa ba abinda yake zargi bane. Washe gari da sassafe ƙarfe bakwai MJ da tawagarsa suka lula zuwa birnin tarayya Abuja. Gara ya koma aiki ko zaiji dama daman abinda ke damunsa. Kawai kawai yarinya zata hanashi peace of mind ɗinsa. A'a gaskiya, Gara ya koma yayita lodawa kansa aiki kodan yasamu sauƙin wannan yawan tunanin dakeyi masa kawanya azuciya. Ansa ranan biki nan da wata guda. Tundaga lokacin kuwa shirye shirye ta kankama. Ammi ce ta ɗauki nauyin lefe, Mamy kuma ta ɗauki nauyin kayan kitchen. Tuni Hajja ta kira masu gyaran jiki daga Maiduguri da Nijar, wadda zasuyima amarya gyaran jiki na tsawon sati Uku har cikin satin bikinta. Kullum sai Innati ta dura mata wasu abubuwa marasa kan gado, wasu da daɗi wasu kuma shegen dacine dasu. Cikin sati ɗaya ta fara wanke wa tana canzawa kamar ba itaba. Raihanah duk tabi ta damu tsakani da Allah ita tafiso ayi wannan auren da Babban Yaya, tabbas Ya Isma'il ɗan uwanta ne amma auren soja wai, ba ƙaramin haɗari ne dashi ba. Kuma ta gama gane cewa Mujahid ya daɗe da kamuwa da son Aneesa amma girman kansa yasa bazai iya yarda da hakan ba, yana ganinta ƴar ƙwaila. Idan kuwa baiyi wani abu akaiba dole itace zata yi, koda kuwa daga ƙarshe angano gaskiya ai auren ya riga ya ɗauru dan haka babu abinda za'ayi. Kwana biyunnan Amin bai cika fitowa cikin gida ba. Kullum yana maƙale aɗakinsa, duk mai tausayi idan ya kalleshi dolene kawai yaji tausayinsa. Yagama ramewa kamar ba Amin the rockstar kamar yadda abokansa ke kiransa ba. Yau fitowa yayi cikin shirinsa na kamala, afalon Ammi ya tadda anyiwa Ameera kitso, tsayawa yayi yana kallon ta kamar zai hadiyeta. Matashin cikinta ya kalla, sosai yake jin wannan cikin har cikin jininsa, kuma ya kamu da son abinda zata haifa. Ada ne yake cewa zuciyarsa gara azubda cikin, amma yanzu idan wani yayi maganannan sai inda ƙarfinsa ya ƙare. Ammi ta kalleshi, sosai yabata tausayi. Gaskiya Amin ɗin yanzu bana da bane, yagane kuskurensa, wannan azaban ya isa haka. Kallon Ameera ta kumayi taga tayi kicin kicin da fuska da alama itama taga Amin ɗin. Murmushi tayi ta girgiza kai, ta wuce ɗakinta tabarsu daga shi sai ita sai mai kitso. Ƙarasa shigowa falon Amin yayi, yace "sannunku, ashe kitso kukeyi. Sannu Ameera" ko tasan da mutum awurin balle tajuya ta kalleshi, ƙara gaida ita yayi wannan karon mai kitso tace "ana gaidake" dan dai kawa karta gane wani abu na faruwa tace uhmmm. Murmushi yayi yace "saina dawo", binsa da ido mai kitson tayi tace "kirika haquri fa Hajiya, mazanne sai ahankali, sun iya ɓata maka rai su dawo suna lallabarka"ita duk tunaninta Amin ɗin mijin Ameera ne. Itadai Ameera ta ace mata komai ba suka cigaba da kitson. Ana sati biyu biki, amarya ta canza kamar ba itaba. Ayaune Abby yace suje itada Isma'il ayi musu genotype test. Raihanah ta dage ita lallai zata bisu, dake itama Aneesa kunya takeji tace lallai saidai Sutafi da Raihanan. Suna isowa asibiti batare da ɓata lokaci ba lab attendants ɗin suka debi jininsu su biyun, akace Sutafi sai can da yamma result zai fito. Wani ƙarya Raihanah ta buga musu tace wai akwai wata maman ƙawarta da batada lafiya kuma tana wannan Asibitin ne zata je ta gaidasu. Duk yadda Aneesa taso ta rakata tace a'a kawai suje gida da Isma'il, ba jimawa zatayi ba. Basu kawo komai ransu ba suka tafi suka barta a asibitin. Tana ganin tafiyarsu tabi bayan wannan lab attendant ɗin. Bata jima ba ta fito da murmushi afuskarta tace "insha Allah, wannan auren da Babban Yaya za'ayi ta"... Like Comment Share 🙏🙏🙏 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 56_60 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Akwana a tashi yau kwana biyar biki, gida ya cika maƙil da jama'a kamar yau ne biki. Mutane daga gefen Hajja, Mamy da Ammi duk anzo. Su Raihanah babu sukuni yanzu ana nan anjima tana can. Duk wani shiri da akeyi kusan komai itake supervising. Allah Allah take MJ ya dawo dan akwai plan ɗin data shirya wadda idan bata aiwatar ba saidai kuma kawai abinda Allah yayi. "Karɓa Kisha karna ɓata miki rai takwara, meyasa kike haka saikace guba nake baki sai faman muzurai kike mun" kofin na kafa abakina na matse ido da ƙyar na shanye tass inaji tsigan jikina suna mimmikewa. Wai wannan wani irin maganine da kullum Hajja sai ta ɗura mun, tsakani da Allah nidai na gaji, haba safe rana dare aikin kenan, daga Hajja ya kawo nata sai Innati itama da nata. Gyaran jiki kam tuni aka ƙara himma, tayi wani irin haske kamar ka taɓa jini ya fito. Gashi ta ƙara ciccikowa, ko ina yayi daram Masha Allah. Hajja ta hanata fita ko da nan da nanne, ko ƙofan falon Hajja ba'a bari Isma'il ya shigo balle cikin part ɗin. Idan ya kirata awaya ma hanawa Hajja take ta ɗauka, ango ya cika yayi famm wai don me za'a hanashi ganin amaryarsa. Yau biki saura kwana biyu akesa lalle. Anyi decorating babban compound din General inda za'ayi henna party, event planners na musamman aka gayyato suka decorating wurin da golden and black balloons, akayi wani ƙaton banner inda aka rubuta "Aneesa's henna party". Ƙawayen amarya sun sa black with touch of gold material, sun zauna alayi can tsakiyan su kuma aka yi tsarin hausawa inda aka sa fillow aka zagaye wurin da carpet. Amarya tana zaune a tsakiya, sanye take cikin simple material golden colour ta miƙa hannunta ana yi mata jan lalle mai azaban kyau. Jiniyan motoci ne tundaga gate akeji suna jerowa cikin gidan da gudu. Wuff Raihanah ta miƙe tana washe baki, Babban Yaya ya iso. Anayi mata lalle ne amma haka tasa mai lallin tabar yin lallin, aguje ta afka tabar wurin sai inda motocin Mujahid suke parking. Wani dogon tsaki Aneesa taja azuciyarta tace "yanzu saboda wannan mara imanin mutumin yasa tace abar lallinta. Lallai ma Raihanah" . Yana fitowa amota cikin takunsa mai cikeda isa kamar bazai taka ƙasa ba yake tafiya, mutane gaba ɗaya hankalinsu ya dawo kansa. Sai ji yayi an afka jikinsa, mamaki ne ya kamashi wane wannan yake neman ya tarwatsa masa nutsuwarsa a bainan jama'a. Ɗagowa Raihanah tayi cikeda farin ciki tace "Babban Yaya Welcome" ɗan banzan kallo ya watsa mata yace " yaushe nafara irin wasannan dake Raihanah" cunno baki tayi tace "kai Babba Yaya, ai da dabanne nidai dan Allah yau bakaga ta zama ba, akwai inda nakeso ka rakani yau dinnan. Plssss" da mamaki yake kallonta, ehhh lallaine influence din mara kunyarnan yafara tasiri akan Raihanah, idan ba haka ba yaran dake bala'in jin tsoronsa shine har yau takeda fuskar datake wani manne masa tana magana dashi kamar tsarar ta. Sai raba ido yake kome yake nema Allah kaɗai yasani. Can gefen part ɗin Hajja yaga an decorating wurin da flawowi masu kyau yace wa Raihanah"me ake yi awurin can" murmushi tayi tace "anayiwa amaryarka ne kunshi, uuffff sorry anayiwa amaryar Ya Isma'il ne ƙunshi" taɓe baki yayi ya wuce part din Mamy inda tundaga kofa yafara haɗuwa da babanninsa, alhalin ya gaidasu sune suke gaidashi yana ɗaga musu kai. Yana shigowa falon yayi turus ganin kamar jama'a dake cikin falon ma sunfi na waje yawa. "Goshhh" yafaɗa yana dafe kai, shi kwata kwata arayuwarsa ya tsani yaga anyi cunkoso haka wlh, shiyasa ma sam baya zuwa wani taron biki ko makamancin su. Ratsasu yafarayi yana wucewa Raihanah na biye dashi abaya sai washe haƙora take. Sallama yayi a ɗakin Mamy ya shiga, tana zaune a bakin gado tana buɗe wasu danƙararrun jewelry set masu azaban kyau sai walwali suke. Tana ganinsa ta rufe tace "a'a mutanin Abuja har kun iso kenan" murmushi yayi ya zauna aƙasan ƙafafunta ya kwantar da kai saman cinyarta yace "Maamyynaaa, i missed you" shafa lallausan gashin kansa tayi tace "Allah sarki Babana, nima nayi kewarka. Kaga dakana da mata da damuwan ya ragu maka sosai ai, amma idan nayi maganan sai ka fara tura hanci" ƙasa ƙasa Raihanah tace " ai Karki damu komai ya kusa zuwa ƙarshe" kallon MJ yayi tace "Babban Yaya kaifa nake jira, banaso dare yayi bamu gama abinda nace zamuyi ba" kallon mamaki Mamy tayi musu dagashi har ita Raihanan tace " me zakuyi daga dawowarsa" ɗan sosa ƙeya Raihanah tayi tana tunanin wani ƙarya zatayiwa Mamy, shima MJ tsareta yayi da ido yana jiran yaji mezata ce, surely this girl is planning something, she's been acting weird" . Turo baki Raihanah tayi tace " Mamy wannan tsakanina da Babban Yaya ne, kedai kawai ki zuba ido" . Da ƙyar tasamu Mujahid ya fito suka wuce part ɗinsa tare, sai faman kama masa hannu take yana fizgewa har suka shigo falonsa da komai yake agyare tas tas. Juyowa yayi yace "now tell me, what is it kike buqata" sosai Raihanah take kallon cikin fuskarsa tace nifa babu komai, dama kawai wai dama inaso nace maka ne idan ka huta inaso muje asibiti, a makaranta ance muje genotype test mukawo result ranan Monday. Toh Kuma kar shirin biki ya ɗaukemun hankali shi yasa nace idan ka dawo sai ka rakani naje nayi. Sakato ya tsaya yana kallon wannan ƴarinyar, yanzu dama abinda takeso tace masa kenan taketa wani binsa up and down. Zuciyarsa na raya masa wani abu daban yace "meyasa bakuje kunyi da wannan yarinyar ba, I thought makaranta ɗaya kuke ko ita ba'a buqatar nata ne"? Dake Raihanah tariga ta mastering karyayyakin dazata yita zubawa MJ tace "wace yarinya kenan Babban Yaya"? Yatsina fuska yayi yace " wannan ƙawartaki mana " yi tayi kamar batasan meyake nufi ba tace "ai wai Nazlah Adam, ai su tuni sunyi nasu" kamar ya kwadeta da mari haka yaji, shi zata rainawa wayo tace batasan wayake nufi ba? Ɓata rai yayi ya koma real Mujahid ɗinsa yace " idan kin gama shirmenki sai ki fice mun aɗaki I need to rest" kamar zatayi kuka tace "kai Babban Yaya, yanzu wai Aneesan ne bazaka iya furta sunanta ba. Toh ai ita tuni sunyi nasu itada angonta" kalmar ango da Raihanah ta furta yasa MJ yaji ransa yayi baƙi ƙirin, har hakan ya gaza ɓoyuwa a fuskarsa. Buɗe ƙofa yayi a tsawace yace mata "Gettt outtt", kamar balbela haka Raihanah ta nemi hanyarta hartana harde ƙafa. Kai amma Babban Yaya da wiyan sha'ani yake. Tana fitowa ta tadda an riga angamawa Aneesa kunshi ta, zama tayi akayi mata simple flower sai faman kallon ƙofan part ɗin Mamy take ko zai fito amma shiru. Can na hango shi tsaye abakin windown sa asama ya kafe Aneesa dake zaune hannu abubbuɗe da ido. Yana iya hango lallin dake hannunta and it looks so beautiful, inama shi akayi wa. Wani abu ne ya kwaɓe shi yace " MJ she's your brother's wife to be", iska mai zafi ya furzar daga bakinsa ya koma ya zauna agefen gadonsa ya dafe kai da hannu biyu. Allah kaɗai yasan halin daya shiga a sati biyunnan daya koma Abuja, aiki mai kyau ma ya gagareshi, he's lost. Yana ji kaman wani abu mai muhimmanci yana neman suɓuce masa. Tunanin ƴarinyar nan ya mamayeshi, ko wayarsa ya ɗauka kaman fuskarta yake gani a madadin hoton Neehal dake screen saver ɗinsa. Wayan ya ɗauko ya kunna, hoton Neehal dake kai ya cire sannan ya deleting hoton a gallery ɗinsa, ba kamar da da idan ya kalleta saiyaji kewarta duk ya addabe shi, amma yanzu daya kalleta sai yaji sani haushi ya kamashi. Jefar da wayan yayi ya miƙe ya shiga toilet. Angama sa lalle lafiya, Ango da abokansa sunzo sunyi ɓarin kuɗade masu yawa. Isma'il ya kasa daina kallon amaryar tasa saboda tsananin kyau datayi, ga wani sihirtaccen ƙamshin dake fitowa daga jikinta wadda ke ƙara haukata shi har ji yake kamar kar yabar wurin. Sunyi hotuna masu kyau, sannan ya aje mata bundle din One thousand guda biyu wai incase akwai abinda zata yi tunda ba waya suke ba. Godiya tayi masa sosai suka ɗan sha love kafin ya tafi da tarin kewarta azuciyarsa🥹 Sai karfe huɗu MJ yaga daman fitowa. Tuni Raihanah ta shirya tana jiransa a corridor din part ɗinsa. Har yanzu fuskarsa a daure take alamar akwai damuwa acikinta. Amma haka ya daure suka fita shida Raihanan. Suna zuwa asibitin data faɗaasa tace lallai sai ya rakata. Da suka shiga aka debi jininta tace mai shima kawai yabayar da jininsa shima ayi masa test ɗin dan ya ƙara tabbatar da genotype ɗinsa. Sarai yasan rigiman Raihanah idan ya tashi, dan haka he had no choice but to give in. Yana fita ta kalli wannan nurse din dasuka haɗa baki da ita tace tanason ta ƙarbi result in the next 30 minutes. Haka kuwa akayi, a reception suka zauna hira har ƙarfe biyar sannan nurse ɗin ta kawo musu result. Bata bari yagani ba, shima kuma bai damu ba tunda dama can yariga yasan genotype ɗinsa. Washe gari akayi shirin dinner. Ango ya cakare cikin light blue shadda ɗinsa mai tsananin kyau, inda amarya kuma tasha adon Black princess gown Mai adon stones. Sunyi kyau kamar asacesu agudu. Mutane sunata fitowa ana shiga motoci wasu har sun riga sun kai venue dazaayi dinnern. Sai kuma wadda zai kai amarya da ango wata danƙareriyar Gwagon ne Black colour na ango shida abokansa suma wadda sukayi to match ɗin motoci. Saiga layin Gwagons gida biyar a tsakiya motocin sojoji kuma guda huɗu, biyu a baya biyu a gaba. Isma'il yakasa sukani sai kai komo yake yana Allah Allah afidda masa amaryarsa su yi chalo. Can saiga tawagan amarya sunyi layi suna jerowa ƴan ɗagwas ɗagwas dasu gwanin sha'awa. Tunda Isma'il ya ƙyallara idanunsa akan Aneesa ya riƙe numfashinsa yana ayyana irin haduwar datayi. Wani abokinsa Captain Sadik ya ɗan taɓashi yana yi masa zolaya yace "man take it easy, she's all yours fa nan da ƴan awanni" harara Isma'il yayi masa yacigaba da kallon sarauniyarsa har suka ƙaraso inda yake. Hannunsa ya miƙa mata, itakuma tsabar kunya takasa saka hannun nata cikin nashi tana ɗari ɗari. Kamar Raihanah zatayi bindiga tace"kaii Ya Isma'il, ai ka bari aɗaura igiyar tukunna. Inka taɓata yanzu ka taɓa haramun" bai tanka mata ba ya budewa Aneesa ƙofan baya tashiga shima ya zagaya ya shiga tasa side din. Ƙawayen amarya kuma suka shige sauran motocin abokan ango aka fara tafiya in convoy. An iso meenahs event center Kano, wurin yayi bala'in haɗuwa sai jin sautin romantic music kake yana tashi softly aciki. Wurin ya cika maƙil da jama'a, wadda aka gayyatar da kuma wadda ba'a gayyata ba. Batareda ɓata lokaci ba Dj yasa waƙar "perfect by King promise" waƙan dake tashe ayanzu. A hankali ƙawaye da abokan ango suka fara takawa cikeda class, inda amarya da Ango ke bayansu suma suna ɗan bada steps ahankali. Bayan sun shigo suka zauna a inda a tanada musu sannan aka fara gabatar da abinda yakawosu. Na kasa samun nutsuwa tunda nazauna akan kujerar nan sakamakon jin ido ajikina danaketaji. Waiwaye nafara yi, karaf idona ya sauka kan mutum dake zaune ta can gefenmu akan high table ya kafeni da shanyayyun idanunsa wadda sukayi bala'in rikicewa zuwa wani colour dani kaina ban sansu ba. Ban san lokacin da bakina ya furta Masha Allah ba, gaskiya wannan bawan Allahn ya haɗu iya haɗuwa. Ya kai duk abinda ake nema awurin namiji ga duk macen datasan metakeyi, haɗuwar tasa har kusan kamar yafi Ya Isma'il ma. Sanye yake cikin Light brown getzner mai simple ɗinki, an mai irin babban riga na zamaninnan ne mai guntun hannu. Kansa yana sanye da hular yarbawa irin wadda ake lanƙwasa gefe ɗaya same colour da kayan jikinsa, wutsiyar gashinsa na kwance akan wuyarsa, duk da spec mai duhun haske yasa bai hanani kallon idanunsa ba, sosai bani ƙirjina ya buga. It's so unusual irin kallonnan, kamar wani magnet ne ke jawo idanuna gareshi. Na kasa ɗauke idonnawa akansa, shima kuma haka. Wani gentle murmushi ya sakarmin wadda ban taɓa gani ba tunda nake dashi a gidan Abby, hakan ya ƙara fidda baiwar kyau da Allah yayi masa, two sided dimples dinsa suka ƙara fitowa da kyau, idan ba idona ne ke yaudarata ba da sai ince kamar fatar laɓɓansa yayi motsi alaman akwai abinda ya furta wadda kinda looks like "YOU LOOK GORGEOUS". Da sauri na kauda idona daga kansa na mayar kan su Raihanah daketa tiƙar rawansu a cikin fili ita da sauran ƙawayena na makaranta. Murmushi na ƙaƙaro amma sam bansan meyasa ƙirjina yaketa bugun tara tara ba. Yadda Mujahid ya dage yana kallonta sai ka rantse bai masan abinda ake yi awurin ba, Sultan dake gefensa ya taɓashi har ya gaji amma ko gizau dan uwannasa baiyi ba, daya juya ya kalli inda Mujahid ke kallo yaga idonsa ƙyam akan Aneesa ne. Shi abunma ɗaure masa kai yake yi, to wai idan dama MJ yanasonta meyasa baiyi ƙoƙarin winning heart ɗinta ba yabari har Isma'il ya riga shi. Hmmm shidai saidai ya zuba ido, amma kam idan Aneesa ce tayi mai nesa saidai yadda Allah yayi da lamarinsa. Da aka kira ango da amarya suyi rawa, MJ kamar zaiyi bindiga, yadda yaga Isma'il ya dora hannunsa saman ƙugunta suna rawa kamar ya tashi ya yi masa ɗan banzan duka. Mace mai sa ƴan uwa faɗa 🙆. Lallai yanzu he can assure himself cewa ya kamu da tsananin ƙaunar yarinyar nan, he's head over heels for her. Irin son dayake mata ma baijin yataba jin haka akan Neehal, kodan saboda Neehal itace ta fara nemansa da soyayya oho. Amma wannan kam ya kusa rasa nutsuwarsa akanta, duk abinda yagani aknmanta ayanzu yana affecting ɗinsa seriously. Yana kishinta kamar me. Bai iya zama awurin ba kawai ya miƙe ya fita, fizgar motarsa yayi kamar zai tashi sama da sauri securities ɗinsa suka bi bayansa. Yadda yake tuki atitin Kano su kansu masu gagara saida suka matsa masa. Yana tuki ne aguje amma kuma cikin sukuni yake yi. Yadda yake overtaking motoci kai ka rantse race yake yi irin na film din Fast and furious. Ikon Allah ne kawai ya kawo shi gida lafy. Bai gama tsaida motan ba yafito yabar ƙofan motarma abuɗe. Ɗakinsa yashiga ya wuce direct saman dressing mirror ɗinsa yafara zubar da kayan dake kai kamar zaiyi hauka dan kawai kishin dake cinsa akirji. Wani irin naushi yakaiwa mirror ɗinsa take ya tarwatse, saiga jini nabin hannunsa tundaga yatsa har guiwan hannu. Bai damu da haka ba, ya zauna saman gado ya kama kansa da hannu biyu, yanaji yadda kannasa ke sarawa kamar zai tsage gida biyu. Sultan ne da Raihanah suka shigo ɗakinnnasa aguje cikin tashin hankali. Ashe tun lokacin daya bar wurin suma suka bi bayansa tareda security. Yadda sukaga ɗan uwannasu, hakan yasa suka shiga tsananin damuwa. Raihanah ce ta kawo first aid box takamo hannunsa, baimasan sun shigo ba saida yaji an riƙe hannunsa. Kallon Raihanah yayi da jajayen idanunsa, ya maida kallonsa wurin Sultan yace "wtf are you guys doing here. Kuje can wurin dinner din ɗan uwanku mana. Damn it" Sultan yace " and you think we'll live you in this condition. Hauka mukeyi. Why do you want to hurt yourself Ya Mujahid. Shimafa Isma'il ƙaninka ne, what do you think will happen idan yagano cewa matar da zai aura kakeso har kake hurting kanka akanta"? Kallonsa yayi da jajayen idanunsa yace "what else should I fucking do, yes I'm in love with her amd I know she's he's fiance but still, zuciya batada ƙashi. Ku nema mun mafita" Raihanah ta tace "Ya Sultan, wlh Ya Mujahid yafi Ya Isma'il son Aneesa, ni naga hakan a idanunsa tun ba yau ba. He's madly in love with her, nima kaina I'm not in support of her getting married to Ya Isma'il " sosai Sultan yaƙara shiga tashin hankali, wannan wani irin abu ne, saikqce Isma'il ɗin ba ɗan uwansu bane, shimafa zuciyace mai bugawa a ƙirjinsa, ya zaiji idan ƴan uwansa suna ɓakin ciki da abinda zai sameshi ma Alkhairi, har ga Allah he's not in support. Cikin son ya kwantar wa MJ da hankali yace " Ya MJ, shawarata kawai shine ka yi addu'a, Allah kaɗai yasan mezai faru tsakanin yau da gobe. Idan Allah yayi itace matarka we have nothing to do about it. Amma Dan Allah inaso idan har Allah yayi Isma'il shine mijinta, to ka fawwalawa Allah komai. Shima yasan da zamanka kuma yasan yadda zaiyi dakai" daga haka kawai ya juya ya fice daga ɗakin. Saidai Raihanah tagama dressing masa hannu sannan ta kwashe komai ta fitar. Ita dai birninta kawai Babban Yaya ya mallaki Aneesa, kuma shine burinta Allah ma zai taimaka mata wurin tabbatar da hakan. Sai ƙarfe goman dare aka tashi taron dinner. Bayan sun dawo gida kowa agajiye akayi wanka sannan suka bi lafiya gado. Aranan da wani irin zazzafan zazzaɓi Mujahid ya kwana. Harta mafarki saidai yayi wai gashinan an daura auren Isma'il da Aneesa, wai a masallaci ya dinga yi musu kuka yana cewa ba'a yi masa adalci ba😂. Karfe sha ɗaya ne ɗaurin auren, dan haka tun ƙarfe tara su Abby suka gama shiri. Su Mamy anata zirga zirga abincin da za'a kai wurin daurin aure. Raihanah da sassafe ta gama shirya plan ɗinta. Ƙarfe tara da rabi taje part ɗin Abby da papper ahannunta babu wanda taganta. Duk da bugun da ƙirjinta keyi hakan baisa tayi ƙasa aguiwa ba. Fortunately kuwa tasamu babu kowa a falonsa, papper tagani ansa cikin envelope, da sauri ta ɗauka ta bude tana addu'ar Allah yasa abinda take tunani ne. Hamdala tayi ganin genotype result ɗin Isma'il ne da Aneesa, da sauri ta dau na Isma'il tasa na Mujahid data riko, sai sunan ango da amarya wadda aka rubuta a different papper wadda za'a bawa Imam mai ɗaurin aure, shima tayi saurin rubuta wani inda tasa sunan Mujahid da Aneesa instead of Isma'il. Tana gama haka ta yi addu'a sannan ta aje da sauri tafita apart ɗin , har zufan wahala ta haɗa tsabar rashin Gaskiya. Abby kuwa yana fitowa bai bude envelope din ba ya ɗauka yasa a aljuhu sannan suka fito sai masallaci. Nan kuwa Aneesa tunda ta farka da safe takeji yadda zuciyarta keta bugun uku uku.har lokacin da ake yi mata makeup ma kasa natsuwa tayi. Sai duba time takeyi, duk bugun da agogo yakeyi tik tok tik tok ji take kamar da bugun zuciyarta yake tafiya. Ta rasa farin ciki take ciki ko kuma fargaba. An cika a masallaci sosai, ba'a ɓata lokaci ba kuwa aka shiga masallacin. Bayan anyi duk wasu abubuwa, su Abba ansha kwalliya cikin babban riga sai faman washe haƙora yake tunda yaga Mujahid, shifa yariga ya gama sawa ransa har yanzu cewa MJ shinee angon. Balle kuma yadda yaga yasha kwalliyan farin shadda kamar angon kuwa. Envelope din Abby ya ciro ya mikawa Imam, shiko limamin daya karanta yaga ai sunan wadda ke cikin result shine yake cikin paper da aka rubuta, yayi murmushi sannan yace akawo sadaki. Da sauri Isma'il ya ciro bundir ɗin fice hundred guda uku ya aje gaban Limami, ga shaidu ga komai da ake bukata. MJ ya rufe idanunsa gam babu irin addu'ar dabaiyi ba azuciyarsa, ji yake idan ya rasa wannan yarinyar tabbas zuciyarsa zata buga. So masifa ne🙆🥹 Cikin sukuni Limami yafara magana kamar haka "akan sadaki dubu ɗari uku, da kuma shaidu kamar yadda addini ya wajabtar, an ɗaura auren Aneesa Zaid Ibrahim da angonta Mujahid Abdulazeez Isa"..... Like Comment Share🙏🙏 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 61_65 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Cikin sukuni Limami yafara magana kamar haka "akan sadaki dubu ɗari uku, da kuma shaidu kamar yadda addini ya wajabtar, an ɗaura auren Aneesa Zaid Ibrahim da angonta Mujahid Abdulazeez Isa", gaba ɗaya mutanin masallacin suka ɗago suna kallon imami banda Mujahid wadda ya ƙara runtse idanunsa gam bayaso ya buɗe yaga mafarki yake yi. Abba dasai washe haqora yake yana girgiza kai saboda ƴarsa ta auri shugaban EFCC Mujahid ABDULAZEEZ Isa. Abby ya kalli imami yace "Allah ya gafarci Malam, an samu matsala fa, ba Mujahid bane angon" da mamaki imami ya kalli Abby yace "subhanallah, toh ai gashi sunansa ne acikin wannan papern da kuma result ya akayi haka" da sauri Abby ya ƙarbi takardan ya duba, aikuwa sunan Mujahid ne toh amma ya akayi hakan ya faru, kuma wannan rubutun ai ba nasa bane, kamar canzawa akayi. Cikin tashin hankali Isma'il yace "Malam baza'a iya warware auren ba"? Girgiza kai imami yayi yace "sai dai kayi haquri amma aure yariga ya ɗauru, sai dai idan shi angon yaga daman ya saketa" gaba ɗaya masallaci ya amsa da sallallami daga bakin mutane. Wannan ga wata sabuwa inji ƴan caca. Abby ya kalli Mujahid da har yanzu kansa aɗuke yake ya kasa ɗagowa ya taɓashi cikeda ɓacin rai, don shi yariga ya gama ganin cewa shi ne yayi wannan abun. Ɗagowa MJ yayi, su kansu saida suka tsorata da halin dasuka ganshi aciki, idanunsa sun ƙanƙance sunyi jaaa kamar ma hawaye ne acikin idon. Abby da ransa yariga yagama ɓaci ya ce "me kake nufi damu, aure wasa ne? Hauka kakeyi da zaka ci amanan ƙaninka ka aure masa mata? Mujahid yaushe kazama haka, Ni zaka tozarta bainan jama'a" shi kansa MJ yakasa motsa lips ɗinsa, to be sanma mezaice ba. Gaba ɗaya wannan turn of faith din baisan ya akayi lamarin ya juya ba. Kallon Isma'il yayi wadda shima kallonsa yake idanunsa sunyi jaaa yana jan zuciya, ko bai faɗa ba idon Isma'il yanuna cewa shima ya yarda MJ yaci amanarsa. Juyowa yayi ya kalli Sultan dake gefensa yaga shima ya kafe shi dana mujiya, he's dead. Asanyaye yace " Abby wlh bansan ya akayi hakan ta faru ba. Kuma meyasa zan ci amanar ɗan uwana fisabilillah" bai gama rufe baki ba yaji Sultan yace "because you love her" sai kuma kaji Masallacin ya sake ɗaukewa da salati, wasu har sun fara ƙuskus. Shock yakama Abby da Isma'il, MJ yanason Aneesa? Yaushe hakan ta faru? Miƙewa Abby yayi azafafe ya kamo collar din MJ ya miƙar dashi tsaye yace "yau zan nuna maka cewa na isa dakai. Yanzu nakeso ka saki ma ƙaninka matarsa" ko gizau Mujahid bai yi ba, Abby ya ƙara jijjigashi gana maimaita kalmar ya saki Aneesa, amma still ko motsi bai yi ba kamar mutum mutumi haka yakoma. Ko ƙasa da sama zasu haɗe bazai saketa ba, dama Allah ne ya qaddara cewa itace matarsa, sannan wadda ya haɗa plan dinnan duk inda yaganshi ba ƙaramin gift zai bashi ba, kuma sai inda ƙarfinsa yaƙare wurin protecting dinsa. Ɗaukan mari kakeji tassss, gaba ɗaya saida masallacin ya ɗauka. Abby ne ya wankeshi da wannan marin yace " Are You a human or a devil. Bakada zuciya ne? Zaka kalli ɗan uwanka yashiga wani hali saboda tsabar son zuciya, yaushe ka zama haka Mujahid" Abba da kwata kwata abun ma ya ɗaure masa kai, yadda yaga yanayin Mujahid tabbas in za'a cire son kai wlh yaron yana ƙaunar Aneesa, take yaji tausayinsa ya kamashi. Miƙewa yayi ya cewa Abby " Alhaji kayi haquri, amma Ni tun ranan da akazo neman izinin ƴata Ni Mujahid naba mawa, don tun ranan danaganshi na kwaɗaitu da shine ya zama mijinta. Gaskiya idan baida niyyar sakinta kar ayi masa dole" fuuuu Isma'il ya wuce ya fita daga masallacin abokansa suka bi bayansa da gudun gaske. Kafin su iso wurinsa har ya shiga matarsa ya figeta aguje, cikin matsanancin Tashin hankali suma suka shiga nasu suka bishi. Acikin masallaci kuwa, duk yadda za'ayi a tausasa zuciyan Abby amma hakan yaci tura, yace Abban Aneesa shima yaci amanarsu, ai Isma'il ne ɗansa daya nema masa auren Aneesa. Hawayen da MJ yaketa tarewa saboda kar girmansa ya zuba a idon dubban jama'a amma ya kasa, suuu sai gashi suna bin junansu ɗaya bayan ɗaya. He's never prayed for a day like this, ranan da zaiga tsananin ɓacin rai afuskar Abby saboda shi, amma he's also helpless,tsakani da Allah bazai iya sakin yarinyar nan ba. Ai dama can Allah yayi shine mijinta. Bakinsa na rawa ya kamo hannun Abby zaiyi magana, Abby ya buge masa hannunsa yace "meet me at home. We're not done with this" ya wuce yabarshi,durƙusawa yayi kan guiwowinsa kansa aƙasa, Imam ya taɓa kafaɗarsa yace "kayi haquri, wannan jarabawa ce, in Allah ya yarda zaka cinye ta da sakamako mai kyau. Idan kanason yarinyar nan, kada kabari arabaka da ita komai daren dadewa". Ahankali aka fara watsewa daga masallacin. Shine ƙarshe, asanyaye ya fito ya shiga motarsa driver yaja suka bar wurin. Horn yake bugawa ba kakkautawa, cikin sauri wani soja ya buɗe masa kofar. Yana fitowa ya wuce direct part ɗin Hajja, ko kula da mutanen daketa ango ango baiyi ba. Suma sun sha mamakin ganinsa cikin wannan yanayi, shida Yakamata ace angansa cikin farin ciki amma kuma sai ɓacin rai yadawo dashi. Masu son jin kwakwaf suka shiga part din na Hajja dan jin meyasa Ango yadawo da wannan yanayin. Ko sallama baiyi ba ya wuce zuwa ɗakin Innati inda anan akewa Aneesa shiri. Tariga tagama shirinta tsaf cikin atamfa mai kyan gaske tasha ɗauri Masha Allah. Sai ganin mutum kawai sukayi ya diro cikin daƙin rai aɓace. Raihanah dake yiwa Aneesa hoto tana ganin Isma'il a wannan yanayin tasan cewa burinta ya cika, amma sai ya bata tausayi. Hannun Aneesa Isma'il ya damke yace "taho mutafi" kallonsa tayi da mamaki, wai dama haka akeyi, ita ta ɗauka iyaye ne da ƙawaye zasu kaita Dakin mijinta, to meyasa nata zai zama different. Yadda taga ransa aɓace ba kamar yadda ta saba ganin shi ba shiyasata jin tsoro dan haka ta mike ta gyara mayafinta tafara binsa abaya. Su Raihanah da wata ƙawar Aneesa mai suna Anna Adam suka bi bayansu, yau ga wani abu suna kallo awurin Isma'il. Meta faru? Suna fitowa fakon Hajja saiga Abby ma da mutanensa su Sultan sun shigo, yadda Abby yaga ran Isma'il aɓace ga kuma Aneesa daya riƙe hannunta yana janta kamar kayan wanki, Hajja ma ta sauko dan Abby ya kirata, gasu Innati duk suna falon. Turus yaja ya tsaya yace "Abby, yau duk abinda zai faru saidai ya faru. He's divorcing my wife right now" su Mamy duk kansu ya kulle, me ake magana akaine wai. Hajja tace "kai Isma'il bana son rashin kunya, meye haka kanata jan yarinya. Ai daga ɗaurin auren bazama kabari akai maka itaba saidai kajata kutafi? Zai yi magana sukaji sallaman MJ, Yana shigowa suka haɗa ido da Aneesa har saida yaji gabanta yayi wani irin mummunan faɗuwa, idonsa ya juya tamkar garwashin wuta, fuskarsa har ja ja yayi. Raihanah na ganin yanayin Babban Yaya, har saida taji wani mugun fitsari yana neman ƙwato mata awando da sauri ta matse ƙafafunta tana haɗiye yawu ido yayi zuru zuru. Abby ya wurga masa harara tajuya ya kalli sauran mutanen falo wadda bakine yace "dan Allah inaso abamu space zamyi magana da iyalai na" batareda musu ba kuwa kowa ya fita sai ya rage mutanin gidanne kawai. Zama sukayi gaba dayansu, Abby yafara magana " wani babban jarabawa ya aiko mana sai dai muce Allah yabamu ikon cinye ta..." Gaba ɗaya abinda yafaru masallaci ya kwashe ya faɗa musu. Isma'il dake zaune agefen Mamy sai jifan MJ yake da mummunan kallo, gaba ɗayansu suka sa salati suna jimamin wannan al'amari. Mamy cikin fushi tace " Ni dama nasan hakan zai faru. MUJAHID kabani kunya ban taɓa expecting haka daga gare ka ba. Yanzu ka zaɓi ka cutar da ɗan uwanka saboda son zuciya, tsakani da Allah ka kyauta kenan"? Kansa na ƙasa ya kasa dagowa, duk abinda zai faɗa ba lallai su yarda dashi ba, amma shikam duk abinda zai faru saidai ya faru amma bazai saketa ba. Juyin duniyannan akayi da MJ ya saketa amma fafir yaƙi motsawa kamar bashi awurin. Hajja da Innati sun kasa magana, to me zasuce, MJ da Isma'il duk nasune, idan akace Mujahid ya saketa kuma bayan yana sonta ai ba'ayi masa adalci ba, shi kuma Isma'il idan akace ya haqura bazai ji daɗi ba, kar hakan kuma ya kawo gaba tsakaninsu. Tsananin tashin hankali Raihanah tashiga, yadda ta zaci abun zai zo da sauƙi ashe ba haka bane, Babban Yaya ya bata tausayi. Tabbas yanason Aneesa da ba haka ba da tuni ya saketa kamar yadda Mamy da Abby suka bashi umurni. Mujahid ne ya fara lura da yadda Aneesa ta kafe wuri guda kamar mutum mutumi, sosai ya lura da yadda take zaune bata motsi. Hajja ce taɗan taɓa kafadarta sai ji kawai sukayi timmm ta zube aƙasan tiles ɗin falon. Isma'il ne ya fara miƙewa daga inda yake zaune sai MJ shima ya miƙe aguje duk sukayi kan Aneesa arude. MJ ne ya fara kaiwa wurinta kafin Isma'il, bai damu dasu Abby da kowa dake zaune awurin ba umm ya sungumeta yayi Dakin Hajja da ita, Isma'il yabi bayansa. Suna shiga ɗakin ya kwantar da ita akan gado ya zauna agefen gadon ya kamo hannunta cikeda kulawa yafara murzawa yana kiran sunanta ahankali, Isma'il dake tsaye abayansa kamar yayi bomb kawai ya juya ya fice aharzuke. Su Hajja dasu Mamy suka shigo Dakin suma hankalinsu yayi matuƙar tashi, Sultan ne ya dubata yaga ai komai normal me, kawai shock ne data shiga. MJ ya kasa sukuni sai kai koma yake abayansu Innati dasuka rufe Aneesa. Wani wawan kallo Abby ya watsa masa yace "kagani ko? Dama abinda kakeso kenan. Toh ai gashinan, idan kanaso ka rasata shima Isma'il ɗin ya rasata ai gatanan sai kuyita yi" bai jira cewarsa ba ya fita adakin. Mamy ma saida tayi nata bombomin duk abanza don MJ ko ƙala baice musu ba, kamar da dutse suke magana. Wannan attitude ɗin dayake nunawa ba ƙaramin ɓata musu rai yake yi ba. Haka dai suka fita adakin don Sultan yace tana buqatar hutu ne ba hayaniya ba. Daga Hajja sai Raihanah dakuma Innati sai MJ daya ƙi fita adakin daka kalleshi saiya baka tausayi. Can ta fara motsi kamar zata farka da sauri ya haye saman gadon ya zauna kusada ita ya zubawa kyakyyawar fuskarta ido. A hankali nake buɗe idona danaji sunyi mun wani irin nauyi, ga kaina dake sarawa dib dib dib, dana tuno abinda yasani cikin wannan halin naji kuka mai ƙarfin gaske ya kwace mun. Buɗe ido nayi na saukeshi kan fuskarsa yana kallona da wani abu a idanunsa kamar damuwa, sosai nashiga yin kuka harda jijjiga, Innati ganin haka itama ta hayo kan gadon tafara rarrashina, nikuma kamar ance naƙara sautin kukan, haka naketayi. Ban san lokacin daya jawoni ƙirjinsa ba nidai kawai jina nayi ajikin mutum ya rungumeni tsamm yana shafa gadon bayana. Aharzuke na fara kiciniyar kwatan kaina amma yaƙi bani daman yin haka. Hajja dake tsaye agefenmu tace masa ya sakeni ya fice adakin tana so tayi mun magana. Badon yaso ba haka ya sakeni yanata ƙare mun kallo har ya kai wurin ƙofa, ayadda nakejin zuciyata tana hauhawa tabbas a wannan lokacin da za'a bani wuka da babu abinda zai hana ban daɓa masa shi a kahon zuciyarsa ba, tsanansa ya ƙara huruwa sosai azuciyata. Raihanah tabi bayansa da gudu tana fashewa da kuka, tabbas dolene taje ta faɗa abinda tayi kar ana ganin laifin ɗan uwanta. Ita ba haka taso al'amarin ya kasance ba amma tabbas ta tafka kuskure. Tana fita aɗakin taji anjawo hannunta zuwa wani gefe can kamar lungu. Mustapha ne yajawota, shima idanunsa sunyi jaaa alamar dai yasha kuka. Ta tsorata da yanayinsa badai yasan itace tayi wannan abun ba. Ƙasa ƙasa ya fara magana saboda kar kowa yajisu yace "why Reena? Meyasa kikayiwa Ya Isma'il haka? Kina tunanin babu wadda yaganki Right? To ni dinnan I saw you alokacin dakika canza result ɗin Ya Isma'il da kuma sunansa" itama ƙasa ƙasan tafara yi masa magana tace "plsss Mustapha karka faɗawa kowa, yanzu kazo ka rakani zanje wurin Ya MJ na faɗa masa cewa nice nayi wannan abun" a tsorace Mustapha yace " kaii, ke bakisan halinsa bane. Ai gara mu fadawa Abby than mu faɗawa Babban Yaya, a'a gaskiya kar muje" still bata yarda ba tace " nidai shi zan faɗa mawa. Ko ma mene zai faru saidai ya faru" tana gama faɗin haka tajuya tawuce, shima yabita abaya yana kiran sunanta. Basu tsaya ako ina ba sai gaban part ɗin MJ. Knocking tayi aƙofa, kusan mintina biyu amma shiru ba'a buɗe ba. Can dai suka ƙara kwankwasa kofar, saida yadau ƴan lokuta sannan ya buɗe kofar. Dagashi sai wandon getzner dinsa da farar singlet wadda ya ƙara fidda hasken fatarsa mai kyau da sheƙi. Gashin kansa kuma ya kunceshi ya barbaza a gefe da gefen kansa kamar mace. Fuskarsa dake dauke da cold expression yace "mekuke so" da gudu Raihanah ta ƙarasa jikinsa ta rungumeshi tana ƙara fashewa da wani kukan tana cewa "Babban Yaya I'm sorry, nayi maka laifi, Please ka yafemun" duk bai gane metake cewa ba, kuma bai rungumeta ba, shidai yana tsaye ne kamar dutse. Daya gaji da kukanta ya ɗago haɓarta dayayi gaja gaja da hawaye yace "it's alright, menene ya faru. Akwai abinda kika mun ne wadda ban sani ba" cikin kuka tace "nice na canza result dinnan na kuma canza sunan dake ciki" zaro ido waje yayi ya jawota da Mustapha cikin falonsa ya ƙulle Kofa kar wani yaji. Zaunar da ita yayi saman cushion ɗinsa yace "Reena why? Meyasa kika yi haka" share hawayenta tayi tace "saboda nasan kanasonta, that's why I wanted to help you" iska ya furzar daga bakinsa ya share mata hawaye yace "shikenan, kukan ya isa haka, but what you did was not right ko kaɗan, ya kike tunanin idan Abby yaji wannan maganan ai shima ransa bazai yi daɗi ba talkmore of Isma'il. Kinaso ki fice masa arai ko"? Da sauri ta girgiza kai tace "a'a Ya Mujahid, pls ka taimaka kar ka saki Aneesa, wlh na tabbata itama tana sonka. Saidai kawai ita har yanzu bata gane hakan ba" wannan furucin nata yayi masa daɗi, kenan ƴarinyar tana sonsa? To meyasa hakan bai nuna a idanunta ba, sai kuma ya tuna wannan unusual look ɗin data bashi alokacin da take hannun Isma'il daya saving ɗinta a swimming pool. Baisan lokacin da murmushi ya ƙubuce masa ba, dimples ɗinsa masu kyau suka lotsa ciki. Kallonsa galala Mustapha da Raihanah suka tsaya yi, to me kuma yasashi dariya. Gimtse fuskarsa yayi yace "yanzu dai, as your punishment Reena, keda kika haɗa auren ke zaki sa tasoni, and only if you promise me that, will I decide wether not to tell Abby" zaro ido waje tayi, shi Babban Yaya komai sai anyi masa ne? Soyayyarma itace zata sa Aneesa tayi masa? Cabb ɗin jan jan. Kallon Mustapha yayi yace "partner in crime, nasan dakai aka haɗa so you're also part of the punishment. Dariya sukayi gaba ɗaya suka rungume ɗan uwannasu. Tunani yafara ta yadda zai iya shawo kan iyayensa su haqura subar masa ita a matsayin matarsa. Magana sosai Hajja tayiwa Aneesa, ta kuma sanar da ita cewa wannan shine qaddararta, dama Allah ya riga ya zana tun fil azal cewa Mujahid shine mijinta uban ƴaƴanta, don haka tayi haquri kawai karta yarda tayi abun dazai sa Abby ya tunzura yace lallai sai MJ ya saketa. Duk wannan maganar da Hajja keyi, tamkar yana shiga ta wannan kunninne yana fita ta ɗayan, bata hangar zaman aure da wannan mutumin koda nan kusa ne, kwata kwata babu comparison tsakaninsu, personality ɗinsu Sam bai matching ba. Shi yanada rashin fara'a, kuma baya sakewa da mutane. Ba kamar Ya Isma'il wadda shi sam opposite ɗin dan uwansa yake, yanada fara'a yanada raha kuma yasan ta yadda zai bi da ita idan tana fushi dashi. Shiko wannan idan tayi fushi dashi ai saidai ya rufeta da dukan tsiya dama kuma halinsa ne. Suna cikin magana Baba Larai tashigo akan Aneesa tayi baƙo yana falon Hajja. Kamar zanyi bullet, waye kuma yazo zai ƙara mun baƙin cikin danake ciki. Innati ce ta gyara mata ɗaurin ɗankwalinta taɗan gyara mata fuskarta yadda baza'a gane cewa tayi kuka ba, sannan ta ɗora mata mayafinta suka fito falonn tare. Abba ne zaune akan ɗaya daga cikin royal cushions din falon Hajja sai faman kalle kalle yake yana girgiza kai, yana ayyana irin kuɗi da aka kashe a wannan gida tun daga bakin gate. Idonsa ne ya sauka kan innati wadda take sanye da danƙareriyar less purple colour ɗinkin bubu wadda ya zauna mata ɗass ajiki, ga ƙunshinta ja ahannu yayi kyau sosai. Ƴar light makeup ne afuskarta amma ta haɗu ba wasa. Ya ma mance da abinda yakawosu gidan saboda kallon Innati, take yaji wani tsananin ƙaunarta ya ɗarsu azuciyarsa. Tundana hango Abba zaune Afalon naji baƙin cikin dake zuciyata ta ninku. To ba dai yabada aurena ba, mekuma ya kawo shi wannan gidan. Kokuma yazo ne dan ya ƙara mun baƙin cikin danake ciki. Zama nayi a ƙasan cushion ɗin dake facing dinshi, kaina aƙasa na gaida shi ƙasa ƙasa kamar ansani dole. Innati ma ta gaida shi fuskarta babu yabo ba fallasa. Shi kuwa sai murmushi yake kamar zautacce yace "Masha Allah uwargida agidan Zaidun Goggo, Allah ya ƙara miki nesan kwana muyi rayuwa cikin soyayya". Kamar nasa hannu akai nayi ihu, badon Innati ta dafe Ni ba, da babu abinda zai hana na miƙe na koma ɗaki, dama kuma ga kaina dake kan ciwo har yanzu. Ganin Innati ta share shi kamar bada ita yayi ba, yasa ya gyara zamansa ya fuskance ni yafara magana " Aneesatu ƴar Baba, nasan kinada hankali, kuma kinada sanin Yakamata. Kinsan cewa babu abinda zai sameka a wannan rayuwar face abinda Allah ya qaddara maka. Kuma babu abinda zaka samu face Allah yayi wannan abun fa naka ne. Nasan tun kafin nazo anriga an sanar dake abinda ya faru a masallaci, dan haka ba wani doguwar magana zanyi ba. Inaso kisani, ni tun farkon ranar da aka zo neman aurenki, shi Mujahid shine dai zuciyata tayi na'am dashi, kuma tun a ranar shi naba aurenki. Kunga ko Allah ma yanaso shine ya zama angonki, shiyasa yabisu aranan da zasu zo Adamawa. Kiyi haquri, kiyi haquri, ki zauna da mijinki kiyi masa biyayya iya ƙoƙarinki. Kar ki taɓa muzguna masa dan kawai ba shine kika yi niyyar aure ba. Allah yasa mudace, kuma Allah ya baku zaman lafiya ya kauda fitina sannan yabaku ƴaƴa na gari", kuka ne ya ci ƙarfina, sosai nake kuka Innati kuma tana shafa bayana alamar nayi shiru, nikuma kamar tana ƙara tunzurani haka na ƙara ɓare baki ina kuka na tashi da gudu na koma sama ɗakin Hajja. Duk yadda za'ayi baƙi da suka zo biki kar su gane meke faruwa amma hakan ya faskara. Dake news kamar wild fire yake spreading kafin kasani ɗaɗɗaya ne acikin gidan Jenar basusan meke faruwa ba. Within short period of time aka fara watsewa, toh gaba ɗaya hankalin mutanen gidan babu shi akan baƙin da aka gayyato. Ƴan son jin kwa kwaf ne kawai suka rage suka ki tafiya. Da daddare ko ina yayi tsit kamar ba gidan biki ba, kowa ya watse harda ƴan gulma dasuka ce su babu inda zasu. Tunda rana da Isma'il ya fice agidan bai kuma dawowa ba, gidansa ma babu shi. Da Abby ya bincika kuma aka ce masa yakoma can wurin aikinsa a Port Harcout. Aranan kowa ya kwana cikin baƙin ciki, ba kamar Raihanah dake jin ranta sakai ba. Tunda de aikin gama ya gama ai lokaci kaɗan komai zai wuce. Aɓangaren Ango da amarya kuma, shi MJ ya kwanta ya rungume filo akirjinsa yana tunanin ko wani hali amaryarsa take ciki. On the other hand kuma ga Mamy da Abby dake fushi dashi, ko ɗazu ma kin magana dashi sukayi, ga kuma Isma'il, bayaso relationship ɗinsu ya ɓaci saboda wannan abun. Juyi ya ƙarayi to the other side ya zubawa bed side lamp ido. Kasa bacci nayi, abubuwa duk sun cunƙushe mun ma rasa yadda zanyi na warware su. Idan na tuno da fuskarsa sai naji wani baƙin ciki ya tokareni a maƙogwaro na. Wayata dake gefena na ɗauka na buɗe hoton Ya Isma'il lokacin dayana filin yaƙi da kakin sojoji ajikinsa. Dake Airforce ne, a background jirage ne irin na sojoji masu yawan gaske. Yayi kyau sosai, hoton na kafawa ido inaji kamar na shiga na rungumeshi konaji sauƙin wannan takaicin. Bansan iya lokacin dana ɗauka ahaka ba sai kawai duba agogo nayi naga ƙarfe 2:45AM, gashi idona garau yake babu alamun bacci acikinta, mikewa nayi na shiga toilet na dauro alwala sannan na fito ma yada Sallah. Bansan iya raka'o'in danayi ba amma har tafin ƙafafuna radadi suke yi mun. A sujjada kuwa kuka mai kyan gaske nakeyi ina kaiwa Allah ƙaran abubuwan da akayi mun, ban tashi ba saida naji hankalina ya ɗan kwanta, har sai lokacin wuraren 4:56AM babu baccin, dan haka na dauki Qur'an nafara tilawa har akayi sallan subh. Ina idarwa kuwa na ɓingire da bacci awurin. Gudu nake cikin wani lambu mai kyau ina sanye da white floral gown gashin kaina dake sake agadon bayana iska sai ƙadamun ita yake. Daidai ƙarshen gonan ina gudu ina kallon bayana kawai naji nayi karo da mutum. Juyawa nayi da sauri ina haki, sanye yake cikin farin jeans da farin T-shirt hannunsa na sanye take da agogon Rolex mai kyau ga wani irin sassayan ƙamshin dake fita ajikinsa. A hankali na ɗago ina kallon fuskarsa, ɗauke take da kayataccen murmushi inda dimples ɗinsa suka ƙara yi masa kyau. Nima murmushin nake mayar masa. Hannunsa yasa aƙuguna ya jawoni jikinsa inda yake fuskantata sosai. Nikuma hannu nasa na sakalo bayan ƙeyarsa muna facing juna, rufe idona nayi ina kusanto bakina zuwa nashi, tun kan nakai shi ya rigani ta hanyar maida hannunsa daya bayan kaina ya haɗe bakinmu wuri ɗaya. Deep emotional kiss yafara bani Yana yawo da harshensa a lungun bakina,nikuma ina yawo da yatsuna cikin tulin gashin kansa... Kamar an taɓani haka naji na miƙe wuffff ina dafe ƙirjina haɗi da salati abakina. Zufa duk ya wanke mun fuskana da jikina. Wannan wani irin mafarkine, kuma in rasa da wa zanyi saida wadda nafijin tsanansa azuciyata. Allah ya isa ban yafe ba wlh, Hannu nasa nafara goge lips ɗina kamar azahiri ya sumbace ni. Inayi inajin hawaye sharrr afuskata. 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 66_70 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Da safe ƙarfe bakwai inata jin hayaniya a falo. Da ƙyar na miƙe nashiga toilet nayi wanka sannan nafito na shirya cikin riga da skirt wrapper na atamfa, ko powder ban shafa ba kawai na yi simple ɗauri nafito. Turus na tsaya ina kallon mutanin dake falo, haba ashe shiyasa hayaniya yayi yawa. Gaba ɗaya mutanin gidane afalon, nida Ameera ne kawai babu. Dake ita yanzu cikinta yayi girma dan haka yana ɗan bata wahalan fita ko ina. Yana durƙushe kan carpet idanunsa aƙasa, ga Abby dayasashi agaba da faɗa, Hajja da Innati suna zaune kan cushion babu mai magana. Su Raihanah na hango can gefe itada Mustapha sun zuba min ido kamar zasu zaƙulo hanjin cikina. Ya Sultan ma haka, idanun kowa naga yadawo kaina har na fara tsarguwa. Asanyaye na ƙaraso cikin falon na zauna kusada Mamy, hannu tasa ta shafa dogon gashina tana tambayata babu abinda ke damuna dai ko. Girgiza kai nayi ina kallon shi yadda ya kife Kai aƙasa ya kasa ɗagowa. Abby naji Yana cewa "Toh gashinan ta sauko, yanzu nakeso ka rubuta mata takardanta kabata agaban kowa, kuma Bayan haka inaso kaje Port Harcout ka roki ƙaninka ya dawo gidannan a ɗaura aurensa da Aneesa" yafaɗa yana jefa masa paper da biro. Sai yanzu yaɗago na samu na kalli ƙwayar idonsa, ya canza launi yazama wani irin jaa mai ban tsoro, hawaye na gangarowa daga idanun nasa. Haɗa ido mukayi, yadda yake kallona har cikin bargona nake jin kallon, ban iya jure wa ba kawai na kauda kai. Ina addu'a a zuciyarta Allah yasa ya rubuta min takardata, Allah yasani bazan iya rayuwar aure dashi ba. Asanyaye ya ɗau papern har zai Fara rubutu naji Hajja tace "idan Mujahid ya rubutawa Aneesa saki, kusa aranku zamana agidannan yazo ƙarshe" da sauri duk muka juya muna kallon Hajja, mamaki ƙarara kwance afuskar Abby yace "Hajja, wani irin magana ne wannan fisabilillah, kiga halinda yarinyar nan take ciki. Ita ma fa ba sonsa take ba, dan meyasa za'a ɗora mata abinda batada niyya" kallona Hajja tayi tace "takwara kina don Mujahid ko kuma a'a, karkiji tsoron kowa. Nayi miki alƙawarin cewa idan kikace bakiso nida kaina zan sa ya rubuta miki takardanki", rasss naji zuciyata ta buga. A hankali na maida idanuna kansa, yadda yake kallona in a sympathetic way shiya sanya naji wani irin yanayi atare dani. Sauke kaina nayi ƙasa, bansan ya zan kira wannan moment ɗin ba. Na dai san cewa bana son shi, to amma meyasa nakasa buɗe baki na faɗa musu hakan. Nayi iya ƙokarina wurin ganin cewa na girgiza kai tunda bakina na muzanta abinda raina keso, amma kuma sai naji kamar wuyan nawa an riƙe ta. Kusan mintina biyu falo ya ɗauki wani shiru, ana jiran aji mezan faɗa. Hajja kuwa ganin haka yasa ta concluding cewa Aneesa tana don Mujahid. Kallon MJ yayi dake tsugune aƙasa, tace masa " Mujahid miƙe" kallonta sukayi suna jiran mezata ce, asanyaye ya miƙe still idanunsa na kan Aneesa da hawaye ke gangarowa daga kurmin idanunta tana amfani da ɗankwalinta tana sharewa. Abby kuwa sai jifansa yake da mummunan kallo. Hajja tace "kema takwara miƙe" da sauri na ɗago ina kallon ta, mekuma take so nayi yanzu. Miƙewa nayi ina kallon yatsun hannuna na kasa ɗagowa in kalli kowa Afalon. Ban farga ba sai ji nayi Hajja ta yafa mun mayafinta Wadda ya matching da kayan jikina, ta kamo hannuna sai ji nayi ta sanya shi cikin wani abu mai uban laushi. Sai da na ɗago naga cewa, hannunsa ne, kamar auduga haka hannun nasa keda taushi. Zuru zuru nayi da ido, me tsohuwar nan take shirin yi. Sai ji nayi tace " daga wannan falon, babu inda zaka tsaya sai gidanka. Inaso ka tafi da matarka yanzunnan. Duk wadda yasan ban isa dashi ba ya gwada tsaida ku" gaba ɗaya ƴan falon suka juya suna kallon Hajja. Tuni hawaye ya fara Zarya a idanuna, zan ƙwace hannuna naji ya ƙara damƙe wa da kyau, Hajja takoma ta bayanmu sai tura mu take yi har takai bakin ƙofan falonta sannan ta rungumemu gaba ɗaya ta sanya mana albarka ta sakemu muka fice afalon, kit kit naji tasa key a ƙofarta. Mun kai minti biyu ahaka, ban motsa ba shima kuma bai motsa ba, still hannuna na cikin nashi, mun kafe wuri ɗaya da ido babu ko kyaftawa, Ni da shi har yanzu cikin shock muke. Dama ance idan kaga kayi kuka to tashin Hankali bai kai ma ƙura bane, shine wannan case ɗin nawa. Hawayen ma kamar kafewa yayi, duk yadda nakeso nayi kukan amma na kasa. Duk girman kansa, yau sai yaji ƴar yarinyar nan tayi masa wani irin kwarjini ta cika masa ido. Ga laushin hannunta dake fuzgarsa ya kasa taɓuka komai. Lallai Allah yabar masa Hajja, Allah ya ƙara mata nesan kwana, tayi masa abinda iyayensa karan kansu sun kasa yi masa. Ahankali ya juya ya kalleta inda yaga itama shi take kallo da cold expression afuskarta. Kamar eye competition haka suka tsaya suka kafe juna da ido ga hannunsa sakale acikin na juna, idan mutum ya kallesu zai rantse kallon love akeyi, nan kuwa ita kallon tsana da takaici take masa, shine dai kawai yake mata kallon ƙauna. Kamar an tsikareta kawai ta ƙwace hannunta cikin nashi, tsoronsa da da takeji taji shima ya kau ta kalleshi tace "kana tunanin kaci galaba akaina ko? Kana tunanin ka rabani da masoyiyana kayi nasara akaina ko? Allah ma yasa mafarki kakeyi, wlh wlh kaji rantsuwan musulunci. Abinda matarka ta farko tayi maka nata nafila ne, tun wuri kayi abinda Abby ya faɗa ko kuma ka gwammace kida da rawa" yadda nake ta hayayyaki amma ga mamakina kamar ko ajikinsa, wannan kallon dai dayake jifana dashi bai canza ba, saima wani smirk 😏 danaga yayi yace "uhhh gurl, ban taɓa kuka akan mace ba, amma tundana fara akanki, just get ready to sign till death do us part with me. Ban fara sonki don na rabu dake ba, dan haka duk wani rigima dazakiyi i know the perfect way to handle you sweetheart " hannu nasa na toshe kunnina duka biyu, wannan kalmar so da kuma sweetheart dayake faɗa Kamar ranan mutuwata yake faɗa mun. Na tsaneshi, na tsaneshi da duk wani abinda ke raina. Hawayen dasuke maƙale ɗazu sune suka samu daman saukowa yanzu, wadda ba haka maso ba, banaso yaga gazawata ko kaɗan, badai dani yake wasan ba, zamu zuba dani dashi shege ka fasa. Signal yayiwa ɗaya daga cikin securities ɗinsa, kan kace me saiga motoci guda biyar sun jera kansu alayi ɗaya. Kallon ta yayi ta tsaya ta cika fammm kamar wacce aka activating da yeast hawaye na zubowa daga idanunta. Murmushi yayi mai ƙayatarwa, batayi aune ba sai kawai ji tayi anyi sama da ita. Duk wani mutsu mutsu datakeyi bai sa ya aje ta ba, buɗe masa mota akayi ya direta aciki sannan ya zagaya shima ya shiga yanajin ransa ƙal. Bai dawo Abuja da farin ciki ba, gashi yanzu zai koma da farin ciki. Yana shiga aka tada motar sai kan hanya. Baƙin ciki ya haɗu mun goma da ashirin, wato dan ya sameni yar ficika dani shine zaita ɗaukana ahannu kamar jaririya, wani abun ma samun wuri ke kawo shi, badon yaga fuskar ba da bai ɗaukeni ba amma ni nasan yadda zanyi maganinsa. Tsabar yadda naji raina a aharzuke, nama kasa yin hawayen kamar ɗazu, zuciyata tana tafarfasa inaji kamar zan yi bomb. Bakina na turo gaba kamar zai tokare driver dake tuki, ai yanzu na rantse shida ganin hawayena har abada. Ga wani ɗaci ɗaci dake taso min a maƙogwaro na na rabuwa da ƴan gida, kewar Innati da Ameera duk ya mamayeni, ko tunanin Hajja ban yi ba, tsohuwar nan ji nake itama na hadata da jikan nata in zauna a ruwan cikinsu ko zan samu sa'eeda. Nidai kallon hanya nake yi, yadda mutane suka kafe motocin da ido abin takaici sai kace sunga shugaban ƙasa ne ke wucewa. Bansan lokacin da naja dogon tsaki ba, cikeda takaicin komai ma. ALLAH sarki Ya Isma'il, nakasa mance bawan Allah, yanzu shikenan na rasashi? Wannan tunanin shiyaso kawomin hawaye, amma dana tuna alƙwarin danayiwa kaina sai na cije. A babban masallacin Niger state muka tsaya saboda lokacin Sallah yayi. Muna fitowa, biyu daga cikin sojojinsa suka take mun baya zuwa gefen mata, duk inda nayi suna biye dani saikace wata prisoner da ba'a so ta gudu, juyowa nayi na hararesu tun daga sama har ƙasa na zuba wani uban ashar, amma mutaninnan ko motsi basuyi ba kamar badasu nakeyi ba. Dan kaina na juya nacigaba da tafiya har wurin alwala, bayan na idar mashiga masallaci amma mutaninnan suna tsaye bakin Kofar shiga sun riƙe bindiga fuskarsu ba wasa. Dake ƙasaru zanyi kawai na haɗa da la'sar gaba ɗaya nayi. Ina fitowa naga dai suna tsaye kamar ɗazu, ban bi ta kansu ba nayi wucewata suka bini abaya. Awurin motar naga ya tsaya ya haɗe hannu a kirji ya zuba min wannan shanyayyun idanun nasa kamar mai cutar sikila, harara na watsa masa tundaga nesa har na ƙaraso wurin motar ban jira ya buɗe mun ba na bude da kaina na shiga. Sai wuraren ƙarfe shida na yamma muka iso cikin garin Baba Tinubu. Baki hanci da ido duk sun kasa rufuwa ina kallon hadewar wannan gari. Ashe haka garin yake, haba ai Dole mutum ya mance da Allah yacigaba da zaluntar mutane, na juya na banka masa harara nacigaba da kallon motoci masu kyau dake shawagi a titin. Asokoro🌷🌷🌷 Wani tangamemen Mansion 🏛️ ne mai girman gaske mai hawa biyu. Faɗin haɗuwar gidan ma kamar ɓata lokaci ne dan bayyana irin kyawunsa yana buqatar page guda ne. Horn suka fara inda gate ɗin dakansa ya fara wangale kansa batareda wani ya taɓashi ba. Masha Allah tabarakallah. A hankali suke jerowa cikin gidan ɗaya bayan ɗaya har gaban ƙaton ginin. Bayan duk sun fito, sojoji biyu sukazo gaban motar da MJ yake sannan suka bude kofar sunayi masa sannu da zuwa. Hannu kawai ya ɗaga musu sannan ya zagaya ta ɗayan gefen inda Aneesa take. Tun kafin yasa hannu ya buɗe ta tunkude masa hannunshi tawuce gaba kamar dama can tasan gidan. Sai da tazo gaban entrance door nan ake rigiman, tayi tayi ta buɗe kofa, kofa yace sai ki buɗe mu gani. Rigiman wannan ƴarinyar yana burgeshi, ta bayanta ya tsaya daidai wurin wani abu ajikin ƙofar kaman scanner ya scanning fuskarsa, sai yasa hannu daidai ƙugunta ya miƙar da ita saitin abun shima ya scanning fuskarta, kamar macece acikin Kofar sai ji tayi Kofar yayi magana yace "new owner approved" baki awangale ta tsaya tana kallo, itafa yanzu ta fara sarewa da lamarin bawan Allahn nan, wato shi ɗagata ko agaban uban waye ba matsalarsa bane. Ai shikenan tasan yadda zatayi tayi maganinsa. Kiiiii kofar tabude ahankali. Wani sanyi da ƙamshi mai daɗi sune suka fara yi mun sallama. Kasa shiga nayi saboda abinda idonsa ya gane mun, ba falo bane, wani wurine kamar corridor, abango Kuma water fountain ne inda ruwan ke saukowa tundaga sama har ƙasa yana shiga wani ɗan kurmi Karami. Cikin bangon kuma kamar da glass akayi, kifaye kala kala masu kyau suna yawo acikin ruwan. Na ma mance cewa da kwai mutum abayana sai ji nayi yace "welcome home Mrs Mujahid, muje ciki da sauran kallo ai, kuma duk nakine" da sauri na juya bayana ina kallon da, tsayinsa daidai nawa, kamar fuskarmu zata haɗe wuri guda. Saurin ja da baya nayi ina jifansa da harara naja tsaki nabi wani ɗan hanya wadda nake tunanin nanne zai sadani da cikin gidan. Nan ma Wani kallon ne sabo, kamar dai corridor dinnan, kusan rabin bangon falon glass ne wadda a cikinta akwai ruwa da kifaye masu kyau. Sama na kalla inda naga ceiling din samansa wani ƙaramin swimming pool ne, reflection din swimming pool din afalon sai yayi kamar muna ƙasan ruwane. Nidai Bature bazai kasheni da ƙaryan kire kire ba, yanzu fisabilillah kalli gidanmu na Adamawa, ahaka ma gara namu akan na wasu, muntane na kwana su tashi cikin yunwa amma ga wasu anan ji suke kamar duniyan ma nasu ne gaba daya. Kar yaga kamar nidin ƴar ƙauyece kawai na saita kaina, na juya na kalli dogon benen da zai sadaka da second floor inda gaba ɗaya stairs din na glass ne ga wasu fitillu masu kyau suna haska benen. Ina tafiya inaji yadda idanunsa ke yawo ajikina musamman mazaunaina amma na matse na cigaba da tafiya har na haye sama. Jerin ƙofofi ne guda uku nagani, na tsakiyan zuciya ta bani na shiga. Da sallama na murɗa ƙofan na shiga, wani sanyi mai daɗi ne ya ratsani ga ƙamshi. Makeken bedroom ne dayaji furnitures na alfarma kamar na sarki. Komai na ɗakin shiny dark purple ne daga labulen har furnitures din. Ga wani makeken King sized bed irin mai circle dinnan gwanin sha'awa. Wannan dai bai mun kamada da kamar an taɓa anfani da Dakin ba, dan komai sabo ne bazaka ce an taɓa wani abu daga ciki ba. Saida na rufe Kofar sannan na ƙarasa shigowa ciki, mayafin kaina na warware na kunce ɗankwalina na zubar akan gado. Kofar danake tunanin nanne toilet na wuce na shiga. Babban closet ne girma amma babu komai aciki, ga wurin takalma daban gana jewelries gakuma na kaya daban shima. Can gefe ne na hango wani kofa daban inda nafi tunanin nanne toilet. Addu'a a bakina na bude nashiga, Masha Allah komai yayi. Ga wani ƙatoton kwamin ruwa a tsakiyan toilet ɗin irin me cycle, nan kuma ta gaba wani tangamemen madubi ne da washing hand basin. Ga wardrobe na glass a gefenshi inda naga towels ne acikin kaloli daban-daban, ga kuma inda aka kewaye da glass wurin wanka kenan, yana dauke da different types of shower head, akwai wanda idan aka kunna ruwa kaɗan yake fitowa, akwai kuma wadda idan aka kunna ruwa normal ne ke fitowa sai kuma wadda zakaji ruwa shaaaa kamar ruwan sama yana fitowa, ga gefen ruwan sanyi gana zafi. Bakina ahangame duk saida nabi kowani lungu da sako na cikin bathroom ɗin kafin na tube kayana yarage dagamu sai pant da bra. Wardrobe ɗin da aka tanada na shampoo da sabulan wanka na buɗe na ciro wadda zan yi amfani dasu. Saidai na tsaya ruwa ya taru acikin bathtub din sannan na jefa shower bomb aciki, daya narke na cire sauran, shower gel da soft sponge na ɗauko sannan na shige cikin ruwan. Ajiyar zuciya na sauke, na kwantar da kaina ajikin tub din warm water dinnan yana shiga lungu da saƙo na jikina. Na dau lokaci dayawa sannan na fara cuda jikina da lallausan soson wanka ga sabulu mai ƙamshi. Bayan nayi wanka na wanke kaina na dauro alwala, sannan na cire ɗaya daga cikin towels dake wardrobe dinnan. Iron towel mai rigan nanne, igiyansa ta gefe yake na daura, na dau karami na daura akai dan na samu ya tsane mun danshin ruwa dake kaina. Saida na tabbata na tsane jikina sannan na fito daga toilet ɗin da kayana dana cire ahannu. Leda na hango saman gadon, ko ba'a faɗa mun ba nasan wadda ya aje shi. Harara na jefawa ledan, dagashi har mai shi suje su karata can bana buqatarsu. Sauri sauri na maida kayan jikina kar lokacin Sallah ya kure. Da mayafina nayi rolling na shinfida ɗankwalina aƙasan lallausan carpet mai gashi dake tsakar ɗakin na tada Sallah. Ina cikin sallah naji ya buɗe kofa, bai shigo ba ya tsaya abakin Kofar saida ya ƙare mun kallo son ransa sannan yaja kofar ahankali yatafi. Bayan na idar ina lazumi, naji irin disco da cikina keyi, tun safe banci abinci ba kamar wacce ke azumi. Kallon ledan dake kan gado nayi, ina hango takeaway dake ciki, dafe cikina nayi da ƙarfi ina haɗiye yawu, wani abu azuciyata na cewa " Aneesa babu kyau fushi da abinci" wani abu kuma na cewa " karfa kici, bakisan meyasa miki aciki ba", na kasa tantance abunda yakamata nayi, daga ƙarshe dai na making up mind Dina zanci abincin idan ma guba yasa aciki, gara na ci na mutu kozan huta da ganin mummunan fuskarsa😂😂. Warware mayafina nayi da rarrafo wurin abincin na dau ledan. Budewa nayi naga takeaway guda biyu ne sai strawberry milkshake da ruwan Cway aciki. Takeaway na farko stir fried pasta ne da grilled fish ɗayan kuma fruit salad ne. Pasta ɗin nafara ci, tunda nayi cokali ɗaya naji wani mugun daɗi ya mareni akumatu bansan lokacin dana fara hambula abuna ba. Tundana kafe kai cikin takeaway dinnan ban ɗago ba saida naga ƙarshen taliyar da kifin,sannan na balle murfin goran ruwa na kafa abakina. Saida najini saƙat sannan nayi gyatsa nayi hamdala. Dagowa dazanyi na ga mutum tsaye abakin ƙofa ya kalmasa hannu a kirji yana kallona cikeda nishaɗi afuskarsa. Kenan duk loman dana dinga yi a idonsa, amma mutuminnan ma ya mugun sameni. Cikeda borin kunya nayi ball da takeaway ɗin tareda strawberry milkshake daban sha ba. Miƙewa nayi na turo baki gaba ina hararansa kamar idona zai faɗi kasa. Murmushinsa mai bani haushi naga yayi ya ƙarasa shigowa dakin, gani nayi ya nufoni, da sauri nafara ja baya yana ƙara matsowa. Saida nakai bango naji dai babu inda zan iya zuwa kuma gashi faffadan kirjin nan nasa mai kama da flat screen TV yayi mun rumfa. Sosai ya matsoni sosai har ina iya jiyo saukan numfashinsa atsakiyar kaina. Ƙoƙari nake wurin hawa da saukan numfashi na saboda idan ba haka nayi ba, to duk hawan da ƙirjina yayi sai ya taɓa nasa kirjin. Kamar hakan baiyi masa ba, saida ya kara kusantoni da kyau wannan karon kam ƙirjinsa male male yake manne da ƙirjina. Wani irin nafara ji a jikina saboda yadda kirjin nasa ke gugan nawa. Aharzuke na buɗe baki zanyi magana naji ya sanya yatsansa manuni ya toshe mun baki dashi yace "shushhhhhh, bakinki yacika Surutu, ke baki gajiya ne"? Haka kawai na tsinci kaina dayin shiru kamar yadda ya umurceni. Handkerchief naga ya ciro daga aljihun wandonsa ya nufa bakina dashi, da sauri na juya kaina gefe. Banyi aune ba sai jin wani abu mai ɗumi a Kamatu na, pecking ɗina wannan mutumin yayi, mashiga uku ji Aneesatu takwarar Hajja, yagama dami wlh. Hawaye mai zafi nashi ya gangaro mun duk yadda nayi na taresu, juyowa nayi na sauri naga ya zubamin ido yana murmushi. Duk ƙarfin da Allah yabani nayi ƙoƙarin tunƙudeshi gefe, kuma Allah yabani nasara. Ina kuka nake cewa "Allah ya isa, ɗan iska kawai. Daga yin auren ma har iskancin naka yafara fitowa tsabar rashin ɗa'a irin naka? Kai ko kunya baka jiba, ko kuma rashin zuciya ne dakai, bama kajin zafin abinda ka aikata ba kenan. Ka aurewa ɗan uwanka matar daya kamata ya aura amma sam hakan bai dameka ba. Kai aganinka zan so ka? Wlh in mafarki kake ka tashi tun wuri, Ni da kai har abada. Bazan taɓa son ka ba, mugu mara imani.." magana na ne ya maƙale sakamakon jin bakinsa danayi cikin nawa. Azafafe kamar mayunwacin zaki yafara tsotsar bakina haɗida kamo kaina kamar zai ɓallata. 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 REEMAH ✍️ PG 71_75 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Saida ya tabbata ya kashe kowani kuzari dake tattare da ita sannan ya saketa yana kallon yadda fuskarta tayi jaga jaga da hawaye. Laɓɓan bakinta yayi jaa tsabar tsotsan dayasha, matsowa yayi gab da ita kuma ya sunkuyo daidai kunninta cikin rada yace " don't judge when you don't know the real truth baby", kiss ya manna mata a goshi sannan ya juya da sauri ya fice. Ina manne da bango, nafara sulalewa ƙasa ina jin tuƙuƙin baƙin ciki azuciyata. Kukan ma ya kasa zuwa, ahaka wai yakeso naso shi? Ta dole ake soyayyar? Ashe kuwa sai dai ya zauna da gangar jikina badai da zuciyata ba. Allah ya kaimu gobe rai da lafiya, zai gane cewa nima ba kanwar lasa bace. Washe gari, kiran Sallan farko akunnena, ban kwanta da wuri ba amma kuma bana makara sallan asuba saidai wani ikon Allah. Alwala nayi na fito na tada Sallah, bayan na idar nafara tilawar Qur'an da kai, sai da gari yayi haske na cire hijabina na koma gado, minti kaɗan bacci ya ɗaukeni. Ban san iya lokacin dana ɗauka ina bacci ba, dan kaina na miƙe ina miƙa da salati, garin yayi haske sosai har ina ganin reflection din rana a window. Saukowa nayi daga kan gado, can saman dressing mirror na hango leda, ko takanshi ban bi ba na wuce toilet nayi wanka da brush sannan na fito. Kayan jikina duk ya dameni da tsami, gashi babu wani kaya aɗakin balle na canza. Towel danayi wanka da ita, shi kawai na bari ajikina tunda ba fita zanyi daga ɗakin ba. Ledan nan na ɗauka bayan nagama shafa body lotion dake saman dressing mirrorn, ƙasan ledan na ga wani ɗan paper anyi rubutu da handwriting me kyau da jan hankali, karantawa nafara yi inda naga anrubuta "Good morning baby. Make sure when you wake up, eat and take Good care of yourself for me. I love you.." Ban gama karantawa ba na cukuikuya papern na yardashi ina sakin tsaki. Wannan so dai wannan so dai, inda haka akeso da mutane dayawa sun backoff. Kai kullum kana cikin matse fuska kamar namijin saniya amma haka wai kakeso mace tasoka, wace dakikiyar ce zata zuba ido kana matse mata fuska, anjima kazo kace you love her. Kai da love din naka go to hell. Allah yasani, bana wasa da cikina ko dan ulcer ɗina, dan haka banyi fushi da abincin ba na ɗauka naci kuma na rage na anjima dan bani da tabbacin zan samu wani. Gaba ɗaya naji duniyar tayi mun zafi, gashi ban taho da wayata ba balle na kira mutanin gida ko kuma nashiga yanar gizo ko zai ɗebe mun kewa. Ajikin window na tsaya ina kallon yadda sojoji ke shawagi a tsakar gida lungu da saƙo ana bawa ko ina tsaro, ga security cameras dake juyi a three sixty. Azuciyata nake tunani, yanzu duk wannan dubban sojojin suna gadin mutum ɗaya ne, kai Allah kabamu kuɗi mai albarka muji daɗin duniya damu da iyayenmu. Kano... Tun bayan tafiyarsu Mujahid, mutanin gidan sukaji kamar mutuwa akayi musu, ga Isma'il on the other hand dake kin ɗaukan kiran su. Su Abby da Mamy duk sun shiga damuwa, ko wani hali yake ciki Allah kaɗai yasani, dake akwai aiki sosai agaban Abby hakan yasa bai samu daman zuwa can Port Harcout yaje wurin Isma'il ɗin ba, to koma idan yaje mezaice masa. Yayi haquri? Innati duk tabi ta damu duk da bata nuna hakan ba, kowani hali ƴarta ke ciki Allahu a'lam, gashi ta tafi ko sallama basu samu sunyi ba. Kowa yana takansa, an mance da zancen Amin wadda kusan kwana uku kenan tun ana gobe bikin baya gidan, amma babu wadda ya lura da hakan, ciki kuwa harda Ammi. Ameera ce kawai ta lura saboda ta saba da addabarta kullum dayakeyi, da farko ana gobe ranan bikin da bata ganshi ba abun bai dameta ba, amma jiya ranan auren da kuma yau babu ko motsinsa dataji. Cikinta da yanzu yake watansa na bakwai ta ƙoƙarta tafito tana takawa ahankali. Falon babu kowa sai karan TV dake aiki, zama tayi saman cushion tana kallon TV amma hankalinta sam baya kai. Har ta gaji da kallon zata miƙe taga an hasko wani scene na accident inda motoci guda biyu ƙaramim mota da Babba sunyi clashing, wannan ƙaramin motar tayi raga raga babu wani abun da yayi saura a cikinsa sai dai plate number daya maƙale. Zaro ido tayi da kyau tana kallon plate numbern inda aka rubuta "Mainoma 001" wannan plate number ɗin tabbas ta Amince saboda same plate name dinnan shine wadda tagani aranan da rayuwarta ta taking a different turn. Ƙafafunta take ya fara rawa tun kan ta gasgasta abinda zuciyarta ke bayyana mata. Wani matashin Journalist Yana tsaye yafara magana " ayau 1st May, a Babban titin Kano mun samu labarin wani mummunan hatsari daya faru yanzu yanzu, inda wani babban motan ruwa da karamar mota ƙirar Buggati sun samu clash. Ayanzu haka mun kasa tantance wadda ke cikin mota ƙaramar amma tabbas mutanin dake zama awurin sun bayyana mana cewa motar mallakin ɗaya daga cikin ƴaƴan Jenar Abdulazeez ne..." Ahap tunda taji wannan bayanin tagama sallamewa cewa Amin ne acikin motar. Take cikinta yayi wani irin juyi har hakan yasa ta saki ƙara mai ƙarfin gaske. Innati dake abinci akitchen tafito da gudu da cokalin miya ahannunta tana nufo Ameera dake dafe da cikinta tana murkususu aƙasan carpet. Cikin tashin hankali Innati ta jefar da cokalin hannunta ta tallafo Ameera tana tambayarta meya faru, cikin kuka Ameera tace "Innati cikina, Ya Amin yayi hatsari kalli" ta ɗaga hannu awahalce tana nuna mata tv wadda har yanzu ana nuna accident scene dinnan. Hajja ma ta sauko daga saman bene da gudu tana tambayar meya faru, ganin jini na bin ƙafafun Ameera dake jikin Innati dukkansu kuka suke yi. Tana ƙarasowa tace "Nadeen mene haka, keda yakamata akira mota yakaimu asibiti kina nan kina kuka, banason shirme fa" bata bi takansu ba tafito da sauri takira ɗaya daga cikin sojojin dake cikin gida, da gudu yabiyota ya shigo falo inda Ameera take, sungumeta yayi kamar jaririya yayi waje da ita, motarsu ya shigar da ita Innati da Hajja suka shiga suma akayi wa motan wuta sai asibiti. Duk Ameera tafita hayyacinta, daga tace cikinta saikuma takira Ya Amin tana hawaye awahalce. Asibitin Sultan aka kaita, suna shigowa babu ɓata lokaci aka gungurata kan gado me taya zuwa gynea emergency, doctors on duty suka fara attending ɗinta da sauri tunda suka gano cewa ƴar gidansu Oga ce. Anyi nasaran tsaida jinin amma da alama sai anyi mata aiki saboda motsin yaro ya tsaya cak, bugun zuciyarsa ma ƙasa ƙasa akeji. Babu bata lokaci aka shiryata zuwa ɗakin theater, Sultan da ke aiki a office Yana attending ma patients tun da yaji ankawo wata daga gidansu yayi saurin fitowa. Ganin Ameera ce yayi saurin canza kaya zuwa theater outfit yace shida kansa zai yi mata operation ɗin. Hajja da Innati suna waje sai kai komo sukeyi, babu irin addu'ar da basu jero ba. Innati dake ta juya sunan Amin aranta tace to ko meyasa Ameera taketa kiransa, sai yanzu kuma ta tuna abinda Ameeran ke nuna mata a TV. Salati tayi ta juya wurin Hajja tace "Hajja.." bata gama rufe baki ba sukaga an shigo da wani a gadon taya nan da gudu, jini gaba ɗaya ya rufe masa jiki fuskarsa ba'a ganewa. Agogon dake hannunsa ƙirar Rolex mai kyau shine gafara jan hankalin Hajja, wannan ai agogon data bawa Amin ne kyautar Hajji data tafi last year. Mummunan bugu taji zuciyarta yayi, cikeda tashin hankali tafara tambayar wadda suka shigo dashi akan wanene wannan ɗin, ɗaya daga cikinsu yace "Hajiya, wani hatsari akayi ɗazu akan babban titi, wata ƙaramar Mota ce tayi clashing da babban mota, amma mutanin sun tabbatar mana cewa motar na ɗaya daga cikin yaran Jenar Abdulazeez ne" Hajja batasan Lokacin da ta sulale ƙasa tim ta zauna da ɗuwawunta ba. Amin ne, Amin ne wlh. Innalillahi wa inna ilaihi raji'uun, hannu tasa akai tasaki ihu mai ƙaraji tana cewa "shikenan na rasa ɗaya daga cikin jikokina. Wayyo Allah Ni Aneesatu naga takaina, wannan yaron yana ta neman yafiyar mu amma muka shareshi gashi yakoma ga Allah da fushinmu akansa, na shiga uku. Allahumma ajirnee fee musibaty wa akhlifnee Khairan minha " tacigaba da kuka tana dukan cinyoyinta, Innati ta durkusa ta kamo mahaifiyar Tata itama tana kuka. Gaba ɗaya wurin saida suka zubda hawaye🥹🥹 Kusan mintin talatin akayi da Ameera a theatre kafin aka fitar da ita, fuskarnan fayau tayi fari kamar mara jini ajiki. Miƙewa Hajja tayi da sauri ta ƙaraso gaban gadon yarinyar tace "itama na rasata ko? Ai na sani, wayyo Allah nidai yau naga takaina" Ya Sultan da fitowarsa kenan yaga irin kukan da Hajja take yi saikace nace Ameera ta rasu, shi baimasan qaunar da ake toyawa ba. Ƙarasowa yayid a saurin wurin kakansa yace "haba Hajja, wayace miki mun rasata, tana nan fa, bacci akwai takeyi. Yaronma an sashi a ƙwalba saboda bai kai lokacinsa koba. Cikin kuka Hajja tace "Sultan, mun rasa Amin, Amin ya rasu innalillahi wa inna ilaihi raji'uun" gaban Sultan yayi wani mummunan bugawa yace "bangane ba Hajja, wani Amin ɗin" Innati dake share hawayenta tace "yanzu aka shigo da gawan wani matashi, shine Hajja taga agogon hannunsa tace wai na Amin ne wadda tabashi, damuka tambayi mutanen dasuka kawo shi kuma sunce wai motar ɗaya daga cikinku ne" Sultan da bai tsaya jin sauran bayanan ba yayi gudu ya wuce dakin da akace ankai gawan wannan matashin. Hankalinsa atashe ya buɗe farin kyallen da aka rufe masa jikinsa dashi, jinin daya ɓata masa fuska shiya hana Sultan iya tantancewa ko dan uwansa ne, jikinsa har ɓari yake ya kalli agogon da akace Hajja ce tabashi, tabbas kuwa agogonne gashi ajikin agogonma an inscribing sunan A Mainoma. Wasu zafafan hawaye ne suka gangaro daga fuskarsa dan shima ya riga ya sallama cewa Amin ne wannan akwance, gaba ɗaya sun riɗe dan haka basu gane cewa skin colour ɗin gawannan dake kwance daban yake dana Amin, duk da Amin yanada duhu amma duhun wannan yafi nashi sosai. Ankai Ameera dakin hutu, tana kwance kamar gawa amma can kwakwalwarta yana hasko mata wannan hatsarin, tana unconscious amma tana ƙoƙarin kiran Ya Amin, tana cewa "dan Allah karka tafi kabarni, wazai yi wasa da ɗanka. Kadawo dan Allah, wlh bazan iya rayuwa babu kai ba. Nayafemaka duk abinda kayi mun, I'm sorry 😭". Nurse dake gyara mata drip ɗin hannunta ta kalleta tana ayyana irin son da Ameera ke yiwa mijinnata, Allah sarki baiwar Allah. Gashi tana haifan ɗansu shi kuma uban yaron yana barin duniya🥹. Hotoro, Kano. Yana cikin bacci yaji hayaniyan abokinsa Mukhtar yana salati. Da sauri ya miƙe yana sharce zufan fuskarsa saboda wani mafarkin mara kyan gani dayayi wai ya mutu, ga Ameera can da jaririnsu sunata kuka. Kallon Mukhtar yayi yace "ya lafiya kuwa"? Cikeda tashin hankali Mukhtar yace "Amin, Sanusi yayi hatsari da motarka kuma banida tabbacin yanada rai yanzu haka" da sauri ya miƙe tsaye yace "WHAT? Sanusi yayi hatsari fa kace. Garin yaya, shida yafita da mota zaije agyara, inna lillahi wa inna ilaihi raji'uun" ya ƙarasa maganan yana saka takalminsa wayarsa ya ɗauka yacewa Mukhtar "taho mutafi yanzu" fita sukayi shida Mukhtar zuwa accident scene ɗin, anan ake sanar dasu ai an kaisu asibiti. Da sauri Mukhtar ya juya machine dinsa jinchenge suka wuce S Mainoma's Hospital. Tunda suka sauka a asibitin dan uwannasa yaji ƙirjinsa na bugu. Wata attendant ce ta kaisu ɗakin da aka sa gawan kafin family ɗinsa su zo. Daidai suna shiga Sultan kuma ya sawo kai zai fita. Ja baya yayi yana kallon Amin dake tsaye abakin ƙofa, Amin ma shi yake kallo yaga idanunsa sunyi jaaa, da sauri Sultan yajawo hannun Amin ya rungumeshi sosai ajikinsa yana shafa kansa yana bubbuga bayansa, shima Amin ɗin rungume ɗan uwansa yayi sosai, Allah sarki dan uwa rabin jiki. Sun daɗe ahaka kafin yasakeshi yace "Alhamdulillah, we all thought we lost you. Alhamdulillah. Ina kashiga Amin duk kasa hankalinmu yatashi." Murmushi Amin yayi yace "wannan dake kwance abokina ne, dashi da Mukhtar sune kawai abokina na ƙwarai, ina gidansu tun shekaran jiya saboda naɗan saki sukunin abinda ke damuna. Shine ɗazu yafita da mota ta zai kaita wurin gyara. Ashe dai tafiyar kenan" ya ƙarasa hawaye na gangarowa daga idanunsa. Mukhtar ma sai kuka kamar ƙananan yara, Allah sarki Sanusi Allah ya jikanka. Saida suka fito daga ɗakin gawan sannan Sultan ya kaishi ɓangaren yara na SCBU (special care baby unit) inda aka sa baby a incubator. Wani blue riga da hula irinna asibiti aka bashi yasa sannan suka shiga. Can na hango wani gado na yara mai kyau, ga wani ɗan ƙaramin oxygen tank dake gefen gadon. Kan gadon na hango jariri ɗan tswit dashi amsa mai pampers Karami babu komai ajikinsa. Agaban gadon suka tsaya shida Amin yanuna masa babyn yace " ga ɗanka nan, Finally kazama Baba" mamaki fal afuskarsa yake kallon Sultan yace "Ameera ce ta haifeshi"? Gyaɗa kai yayi yana masa murmushi. Hannunsa har rawa yake ya kai hannunsa dake sanye da handglove ya taɓa yaron ahankali, motsi yayi saikuma yakoma bacci. Wani irin farin ciki ne ya mamaye Amin, Allah sarki duk da bata hanyar aure aka haifeshi ba amma tabbas wannan yaron na musamman ne, soyayyarsa lokaci ɗaya ta ɗarsu azuciyarsa. Kana kallon babyn kaga babansa, saidai shi yafishi haske ya dauko hasken mamansa. Suna fitowa Amin yacewa ɗan uwansa akaishi ɗakin da aka kwantar da Ameera. Su Hajja da Innati dasu Mamy duk sun zo asibitin, kowa da kalan gunjin kukansa, ana kukan rashin Amin,dan tuni Hajja ta baza labari cewa an kawo gawan Amin nan asibitin Sultan. Da sallama suka shigo Dakin, Sultan ne agaba sai Amin abayansa. Idon su Hajja akan Amin yafara sauka, duk suka miƙe suna sallallami. Hajja ta ƙaraso gabansa da sauri, ta riƙe gefe da gefen fuskarsa tana kallonsa hawaye na gangarowa a idanunta, bayan ta tabbatar cewa shiɗinne ta rungumeshi tana yiwa Allah godiya. Su Mamy da Ammi har Innati duk suka miƙe suna sukayi kansa suka rungumeshi gaba ɗaya. Wannan hayaniyan shiya sanya Ameera ta farka agigice ta saki kuka mai ƙarfi tana kiran sunan Amin. Wannan shiya jawo hankalinsu zuwa kanta. Kafin su motsa har Amin yakai bakin gadonta ya zauna agefenta ya kamo hannunta yana kiran sunanta. Kamar amafarki taji muryarsa ta daki dodon kunninta, da ƙyar taƙarasa buɗe idanunta ta saukeshi akansa. Kamar gizo gizo haka take gani, hannun nasa ta damƙe da kyau tana cewa "Yaya Amin kaine? Dan Allah ba mafarki nakeyi ba?" Gyada mata kai yayi shima yana hawaye, tabbas Allah ya dasa masa ƙaunar yarinyar nan mai karfi azuciyarsa🥹, hannun nasa ta riƙe da kyau tace "Alhamdulillah Alhamdulillah ya Allah" da ƙyar ta miƙa hannu ta kamo hannunsa ya rungumeta, duk wannan abinda ake yi su Hajja suna tsaye galala suna kallon ikon Allah, ko dai sun mance iyayensu na ɗaki ne. Sumui sumui Hajja dasu Mamy duk suka fita aɗakin harda Sultan aka wuce dakin jarirai, sukuma iyayen aka barsu su gana da junansu 😂 🌷🌷🌷🌷🌷 Gidan Amarya da Ango Har yammah yayi ban ji motsin kowa a gidan ba, sai ɗazu da rana da aka kawo mun abinci wai shine yasa akawo. Oho nidai babu abinda yadameni, zama nayi na ɓararraje abinci iya son raina. Bayan Sallan maghrib naji na gaji da zaman daki tunda babu kowa a gidan nace bari in sauko in ɗan zaga cikin ginin. Saukowa nayi naga ko ina agyare tas tas, wurin wannan water fountain ɗin na tafi, har kujera na nemo na zauna inata kallon kifaye , araina nace ahap, ai ni kawai nasamu gurin hira tunda na kula nikaɗai ce agidan. Har aka kira sallan isha'i sannan na haura sama ɗakina nayi Sallah. Nikam nagaji da zama haka babu kayan sawa, gashi banida waya dazan kira gida ince akawomin nawa dana bari agida. Ina cikin wannan tunanin ne naji an murɗa hannun kofar an shigo. Har zan fara bombomi, naganshi tsaye cikin riga da wando na suit amma babu jacket din ajikinsa, ya naɗe hannun rigan zuwa saman elbow, boturan rigan kuma guda uku bai haɗa su ba, kasa ɗauke idona nayi daga kansa, kallon dantsen hannunsa nayi na haɗiye wani yawu makwat, wannan ko dan dambe albarka. Yadda take kallonsa gaba ɗaya tama mance cewa towel ne ajikinta, shima tundaga kasa yake kallon ƙafafunta kar zuwa kirjinta, ahankali yafara takowa da ledodin hannunsa har zuwa gabanta. Da sauri ta kauda ido tana hararan gefe, murmushi mai sauti yayi ya sunkuyo daidai kunninta yace "i missed you baby" ya ƙarasa maganan yana chuckling kamar karamin yaro. Juyowa tayi ta harareshi ta matsa baya. Dakanshi ya dinga fitar da kayakin ɗaya sayo masu yawa, saida ya jera matasu cikin closet ɗinta sannan ya fito da wani kayan bacci ahannunsa. Tana zaune saman stool ɗin dressing mirror, ta ɗora ƙafa ɗaya kan ɗaya tana karkadashi. Murmushi ya ƙarayi yagirgiza kai, Anee rigima. Bansan lokacin daya fito ba sai kawai jin hannunsa nayi kan igiyan towel ɗina Yana ƙoƙarin kuncewa. Kan bantan Uba🙀, aiko bai isa ba, da sauri na riko hannunsa ina zuba masa harara. Hakan baisa ya fasa abinda yake shirin yi ba. A hankali yakama hannunta ya saukar dashi ƙasa sannan ya cigaba da zare igiyan towel din, tanajin ya zare igiyan ta miƙe da sauri ta bankaɗeshi ta koma can nesa dashi ta riko towel din da kyau kar ya zame. Takowa yafara yana zuwa kusa da ita ta kwasa aguje zuwa gadonta, hayewa tayi saman gadon ta jawo duvet ta rufe kanta ta kanainaye ko ina kamar ɗan kwado. Abun har dariya yabawa MJ, hannu yasa yafara kunce maɓallen rigansa har ya ciresu gaba ɗaya, shima ya haye saman gadon. Hannu yasa yafara jan duvet din, itakuma tasa hannu itama ta riƙe gam tana magana cikeda masifa acikin bargon tace "kaga Malam ka fice mun aɗaki, yau iskancin kuma yatashi yau so kake kayi mun zindir, ai baka isa ba, muga ni da kai wazai ci galaba akan waninsa"Ahaka fa shi wasa ma yake yi, da yanaso ne dayasa hannu sau ɗaya kawai zai cire bargonnan ajikinta tsaf, amma tunda ta daring dinsa aiko zai cire shi yaga abinda zata yi. Jin yayi shiru bai motsa ba Aneesa har ta fara ajiyar zuciya, duk tunaninta ya sauka akan gadonne, batayi aune ba kawai saiji tayi anyi sama da bargon. Wani irin ihu tasaka ta mike arazane tana sakin ashar. Tsaye yake da bargon ahannunsa yana yi mata dariyan mugunta, abinda poor Aneesa bata sani ba shine bargon da MJ ya kwaɓe ajikinta harda towel ɗinta ya haɗa, amma masifa ya rufe mata ido. Tsayayyen breast dinta ya kafawa ido yakasa ja da idanunsa awurin, dama haka yarinyar nan take, Ya Ilahi. Nayi bombomin nayi zagin amma naga mutum yana tsaye kamar dutse naga ya kafawa wuri ɗaya ido. A hankali nabi inda idanun nasa ke kallo, abinda nagani shiyasanyani sakin ihu mai ƙaraji na sauko daga saman gadon da gudu sai kansa nayi na faɗa jikinsa ina boye abinda yake kallo ajikina sosai ajikinsa tsabar ruɗanin dana shiga, na sa hannu na matse kirjina sosai da jikinsa, anawa foolish tunanin wai tunda bathroom yayi nesa da zan shige kawai na faɗa nasa jikin dan na samu kariya ashe babban kuskure na tafka. Kunya naji ya mamayeni na kasa koda motsi ne, naked breast dina da kirjinsa suka haɗe atake wani irin yanayi ya sauko mun wadda tun da nake aduniyan Allah ban taɓa shiga irinta ba. Daskarewa yayi ya kasa motsi, shikenan tagama dashi. Yadda ta matse kirjinnata da nashi shiya sanyashi jin mugun kasala ya saukan masa, ahankali ya ɗora hannunsa saman Ass dinta ya damƙesu da kyau, numfashi yake saukewa ahankali yana ƙara mayar da ita jikinsa. Jin hannunsa saman mazaunaina yasa naƙara yin lakwas bakina yayi mun nauyi dazanyi wani masifa. Ƙafafuna naji sun fara rawa, da ƙyar da kuma taimakon Allah nafara kiciniyar raba jikina danashi amma mutuminnan tsabar rashin imani ya ƙara matseni sosai bayaso ya sakeni. Hannu yasa ya ɗagota jikinsa ƙafafunta suna zagaye a bayansa yafara takawa ahankali zuwa gadonta. Idonta a runtse luff, ta gama sarewa da mutuminnan, lamarinsa tsoro yake bata. Gashi daga peck yakoma har tsiraicinta yake gani Ya Allah 🥹 Innocent beautiful face ɗinta yake kallo, wani abu na ƙara jawoshi zuwa wurinta,ahankali ya kwanta saman jikinta. Yar ƙara ta sake jin uban nauyin daya sakar mata, tana iya jiyo numfashinsa dake sauka saman fuskarta da sauri sauri, shiko gogan sai wani danne yarinyar mutane yake, pink lips ɗinta yake kallo da rinannun idanunsa, da mugun slow ya haɗe bakinsa da nata yafara sucking ahankali. Ga hannunsa dayake yi mata tafiyan tsutsa ajikinta, sai ga takwarar Innati tayi makwas ba bakin surutu da tsiwa😂 Saida yasha son ransa sannan ya cire bakinsa yana ƙare mata kallo, idonta alumshe kamar ɗazu ga danshin yawunsa akan lips ɗinta. Boobs ɗinta yake ƙarewa kallo, n**ples dinta sun wani fito zuru zuru suna tsone masa ido. Hannu yakai kan guda ɗaya yana shafawa tareda lailaya mata shi, ajiyar zuciya tayi tana ƙara kankameshi da kyau. Murmushi yayi, yagano first point of weakness ɗinta. Cikin mayen sha'awa dake fuzgarta harta ɗora hannunta saman gashinsa tana yamutsawa tareda ƙara bankaro masa kirjin da kyau (Takwarar Hajja kin badamu🙆). Ya ɗau lokaci mai tsawo yana jagwalgwala ta yadda yakamata kafin yaji yaɗan samu sukuni, bayaso yayi the main the main tun yanzu🙈, dama kuma yanzu ma dan ba'a hayyacinta take ba da yasha zagi da Allah ya isa 🤣🤣. Jin jikinta ya saki numfashinta kuma na sauka ahankali yasashi dagowa ya kalleta, har bacci ya ɗauketa hani'an. She looks so damn gorgeous when sleeping. Kiss ya manna mata agoshi yace "I love You Baby Girl" sannan ya sauko daga saman gadon ya tattaro wandonsa da bai san lokacin daya bar jikinsa ba da kuma rigansa ya haɗa wuri ɗaya, gyara mata kwanciya yayi ya dauko duvet aƙasa ya rufe mata jiki bayan ya ranƙwafo ya manna mata kisa a boobs 🙈 sannan ya kashe mata wuta ya fice aɗakin. 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 76_80 Warning ⚠️ 🔞 Contains Explicit and matured words. Please do read at your own risk. Remember to be warned is to be for armmed !!!! Not edited ❌ 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 No haka naji wani dummmm da ƙarfi ya daki kunnena, agigice na tashi daga kan gadona ina wuntsilowa ƙasa. Ashe dai ba mafarki nake ba, ƙaran bindiga ne ke tashi tako ina pass pass har reflection ɗin hakan na nunawa awindow saboda dare. Take jikina yafara rawa narasa ina zan shiga in ɓuya. Sai yanzu ma na kalli jikina ashe babu komai, abubuwan daya faru some hours ago yafara dawo min tiryan tiryan, rarrafe nafara ina yi ina jin zuciyata na bugu kamar zai ɓallo kirjina, har nakai bakin ƙofar closet ɗina na shiga, miƙewa nayi nafara neman kayan sawa, tsabar ruɗewa ban san lokacin dana buge jewelry box da aka aje saman canter ba yafaɗi akasa warwas ta fashe, ƙafana yafara rawa hawaye tuni yafara gangarowa ina yi ina ambaton sunan Allah, su waye wannan kuma dazasu hana mutane bacci a tsakiyan darennan. Wani wando da rigan sanyi set na ɗauka na sa, dake rigan mai hulace na maƙala hula saman kaina. Tsayuwa nayi ina tunanin mafuta, tabbas harbinnan acikin gidannan akeyinta, kuma kamar ma ƙaruwa takeyi, toh a ina zan ɓoye, ban gama tunani ba naji an bankaɗe kofar ɗakina anshigo, cikina ya ɗuri ruwa ƙafafuna suka gaza ɗaukan nauyina, inaji kamar za'a shigo closet din nayi saurin kashe wutan na koma bayan ƙofa na ɓuya. Mutumin ya shigo bansan ko wanene ba amma ina ganin reflection dinsa saboda wutan toilet akunne yake, bayansa na kalla amma na kasa ganewa ko wanene. Ƙasa ƙasa naji kamar mutumin na kiran "Aneesa" tsoro ne ya ƙara shiga har hanjin cikina, addu'a kam babu wadda banyi ba saidai wadda ban sani ba. Flashlight naga an kunna dauuu mai hasken gaske an haska mun idona dashi har saidai na rufe idon gamm. Mutumin bai kashe wutan ba kuma bai kauda shi daga idona ba bai kuma cemun komai ba, haka muka tsaya nama kasa yin komai na ƙara runtse idona gamm inajin yadda zuciyata ke tsananta bugu. Kashe tocin naji yayi, sai tsit kamar ya fice. Har na saki ajiyar zuciya sai kuma naji anyi wuff anyi sama dani, wutsil wutsil mafarayi da ƙafa ina bubbuga bayan mutumin amma bai tsaya ba, haske ne ya kara gaure mun idanu, sai alokacin na lura da cewa falon ƙasa muke. Abinda nagani shine ya ruɗar da duniya ta, shida sojojinsa guda uku suna rusune a tsakiyan faalo an ɗaure musu hannu ta baya. Wani fitsari naji ya daki marata, Idona tsam akansa ina kallon shi, shima Ni yake kallo idonsa sun rine zuwa abun tsoro. Mutanin danaga sunyi kawanya afalon ban gane ko ɗaya acikin su ba, suna sanye da bakaken kaya sun rufe fuskokinsu kamar armed robber ko assassins zan kirasu, amma dai su ɗin abun tsorone. Mutumin daya ɗaukoni na juya na kalla, shima yana sanye da kaya irin nasu, ban gane shi ba, rabin fuskarsa a rufe take, toh amma ya akayi yasan sunana ɗazu naji yana kirana. Kallona na komar izuwa kan Ya MJ dake rusune shima dai da alama bai san wanene a tsayen ba. Cikin wata irin kausashshiyar murya daban taɓa jinta daga wurinsa ba naji yace " Who the hell are you guys, kusu wanene. Mekuke nema damu. Har wani iko kukeda har kuka iya shiga gidannan kukawowa sojojina farmaki" daga gefensa ɗaya daga cikin wannan armed robbers ɗin yace "soon zaka sani, kar ka damu. Idan muka gama da abinda yakawomu basai mun bayyana maka mu wanene ba, ranan tashin ƙiyama zaka ganmu, amma yanzu kam daganan kafara shirin yiwa duniya bye bye,abinda idonka zai gane maka yanzu zaka gwammace da mala'ikan mutuwa zai ɗauki ranka kawai ayanzu" yana gama faɗin haka mutuminnan dake bayana ya finciki gashin kaina ya matso dani gab da shi ya rungume. Ihu na sake kamar za'a yankani, hawaye shaaaa ina jin zafi rikon dayayi mun. Kamar zaki haka MJ ya tada jijiyoyin wuyarsa idanunsa azazzare yace "heyyyyyyyyy, karka kuskura ka taɓa mun matata. Zanyi pata pata da naman jininka, release her noww" wani shu'umin dariya mutumin yayi ya ƙara damƙeta dakyau yace "haba mlm, me akayi ko? You want me to release her? Hhhhhhhh" yayi dariya sannan yace "zan releasing dinta bayan na releasing abakinta🙀", rassss naji zuciyata ta buga, hawayen dake Zarya a idanuna suka ninku. Ganin hawaye a idanun abar ƙaunarsa hakan ya haddasa masa jin ƙuna azuciyarshi, idan sukayi gigin taɓa masa mata sai sunga worst side of him. Sojojinsa dake gefensa sai wani huci suke yi kamar suyi bomb, tabbas a wannan lokacin idan da za'a hurgo musu ɗaya daga cikin mutaninnan da kaca kaca zasuyi da namominsu. Ga shi har yanzu kafca akeyi awaje tsakanin armed robbers ɗin da sojojin dake waje. Jefar dani yayi saman doguwar sofan falon har kaina ya bugu da katakon shi. Ƙara na saka ina fashewa da kuka, mutuminnan yasa ɗaya daga cikin mutanensa suka toshe mun baki da handkerchief mai warin tsami kamar an share hammata dashi. Ga amai dake tasomin, ga azaban da ƙeyana keyi saboda buguwar danayi, rigar jikina ya kama da dukkan ƙarfinsa ya keta saman wuyan dan rigar akwai kauri sosai kamar sweater. Yanzu kam kuka wiwi na fashe dashi, Ameera ce ta faɗo mun azuciya, yanzu Allah kaɗai yasan tashin hankalin data shiga a lokacin da su Amin sukayi mata aika aikannan Ganin an yaga mata riga, da gaske dai raping ɗinta sukeso suyi agabansa. Sojojinsa suka duƙar da kai kasa suna jin haushin kansu. Ogansu na wannan halin amma basuda yadda zasuyi su taimaka masa. Armed robbers dake tsaye akansu ganin kamar suna shirin yin wani abu suka saita bakin bindigarsu da kyau da kyau daidai keyansu. MUJAHID iya wannan lokacin ya gwammace ya rasa ransa akan ajefa rayuwar masoyiyarsa cikin haɗari. Dariyan mugunta wannan mutumin yayi da muryarsa mara daɗin ji, hayewa yayi saman ruwan cikina yakamo hannuna duka biyu ya ɗaura saman kaina ya haɗe su wuri ɗaya, ina kuka ina rokonsa amma yadda kasan sheɗan haka yaki barina. Juyawa yayi ya kalli Ya MJ yace "look well, ka kalli yadda zamu fatattaki palace ɗin matarka. Na tabbatar maka daga yau inka kalli wurin sai kaji kamar ka yanyankata saboda tsana. Hhhhhh" yakarasa yana kai hannunsa saman kirjinta da babu bra sai rigan sanyi, bai kaiga tabawa ba yaji an buga masa wani abu kaman ƙarfe a ƙeya. Ihu yasa yana kama keyannasa ya mirgina gefen Aneesa da tuni ta sume. MJ ne tsaye da bindigan ɗaya daga cikin mutanin dake tsaye akansu ɗazu da bindiga, baiyi wani tunani ba yajuya gindin bindigar yafara bugun wannan azzalumin mutumin aduk inda yasamu. Abun sai yazama change of position, da farko armed robbers dinne suka dominating ɗinsu, yanzu kuma sojojinne suka kewaye falon kamar sun sauko daga sama, toh yaushe ma har suka shigo falon haka suka ɗaukesu abazata. Saida yayi masa tilis ya make sure ya targaɗa kowane gaɓa na jikinsa sannan yasa shi a tsakiyansa yana tsaye akansa yafara kiciniyar cire masa faceask dake fuskarsa. Duk da yasha bugu amma yake ƙoƙarin kare face mask ɗinsa, sojan MJ dake gefensa ya kama masa hannun mutumin har yayi nasaran cire masa face mask ɗin. Baiyi mamakin ganin wadda yagani ba, dama yasan a kowani rana yana tareda haɗari, toh amma meyasa basu attacking ɗinsa tun yaushe ba sai yanzu dayayi Aure? Azafafe ya kaima mutumin mugun naushi ya ɗago collar ɗin rigarsa yace " Ministan kuɗi ne ya aikoku, basaina matsa kun faɗa mun ba. Ohhh, You guys are doomed. Da naso nabi komai ahankali amma yanzu tunda kuka shiga sabgar iyalina sai na baku mamaki. You dare touch my wife and go scot-free? I'll make your lifes a living hell I promise you" jifa yayi dashi wa sojojinsa, sukuma kaman karnuka haka suka rufu masa baka jin komai sai gib gib gib yadda kasan ana dakan sakwara a turmi🤣 Sungume matarsa yayi ahannu yana ƙare mata kallo har ya haura sama. Ɗakinsa yakaita ya kwantar saman katafaren gadonsa na alfarma, yaja bargo ya rufe mata jiki. Kallon agogo yayi yaga minti kaɗan za'a kira sallah. Bayi ya wuce yayi alwala sannan ya fito yayi shirin Masallaci har lokacin bata farfaɗo ba, ruwan dake side drawer ɗinsa ya ɗauka ya zuba kaɗan ahannunsa ya yayyafa mata. Saida taja numfashi mai tsayi sannan ta sauke, ahankali ta buɗe idanunta ta saukeshi akansa, tana ganinsa a tsaye ta miƙe da kyau ta gyara zamanta tana kallonsa harda murza idanunta dan ta ɗauka ko mafarki takeyi. Zama yayi agefenta ya kai hannunsa zai taɓata ta buge masa shi, sai kuma tasa kuka wiwi tace " duk laifinka ne, ba don ka aureni ta hanyar dole ba da yanzu ina gidan masoyina. Wlh da sunyi mun fyaɗe har in koma ga Allah bazan taɓa yafe maka ba. Yiiiii" ta ɓare baki kaman jaririya tana kuka. Haushi iya haushi kam MJ yaji, yana jin daɗin ya kuɓutar da ita daga hannun mugayennan, amma shine ta buɗe baki tana kiransa sunaye. Ita badon son dayake masa ba ta isa ta buɗe baki takirashi dan Iska bai gurje mata baki da ƙasa ba? Zuciyansa na tuƙuƙi ya daka mata tsawa yace "shuttt tf upp. Naƙara jin kukan ki saina miki dukan tsiya saboda kiyi kukan da hujja. Kina matata kike faɗa mun cewa da ban aureki ba da kina gidan wani. Thank heavens for the love I have for you, da sai kin gwammace kida da rawa. Mara kunya kawai" itama aharzuke ta tashi tana fuskantarsa tsawonta daidai nashi ido cikin ido tace " to ka rabu dani mana, antaba yin wani abu dole ne. Nace maka bana sonka bana sonka basai ka ƙyaleni ba. Kuma bazan taɓa daina son Ya Isma'il ba har numfashina yabar doron.." bata ƙarasa ba ya ɗauketa da wani irin mari har ta koma ta kwanta luff saman gado kamar lawashi" ya fuskanci idan ya zauna yabi na yarinyar nan saidai tariƙa ƙara masa hawan jini akan wadda yakeda shi tun da da, dan haka kawai ya bar mata ɗakin gaba ɗaya ya wuce masallaci. Kafin yafita saida yasa aka gyara ko ina tsaf, Allah yasa babu wani sojan da aka rasa saidai wanda akajima ciwo. Saida nayi kukana iya son raina naga babu mai rarrashina na miƙe na shiga toilet nayi wankan tsarki nayi wankan sannan nayi alwala na fito. Sai yanzu ma na lura ashe ba ɗakina name ba, wannan Dakin ya ci uban nawa a haɗuwa da girma da komai ma. Ban tsaya kalle kalle ba bataci ɗakina nayi Sallah. Ina idarwa na kwanta saman sallaya nacigaba da jera kukana har waƙan "so so na Umar M Shariff" nayi saboda jinake kamar heartbreak nake ciki😂. Baccin da aka hanamun da tsakiyan dare shina biya yanzu. Na ɗauki lokaci mai tsayi ina baccina kafin na farka. Wanka nayi na shirya cikin gown irin mai tattara a cikinnan dai kasansa kuma abaje yake, ta saman rigan kuma show me your shoulder ne, sai hulan kayan na feshe jikina da turare na sanya flat shoe na fito falo. Ko ina tsaf tsaf kamar ba falon da aka wargaza saikace filin yaƙi ba. Hanyan kitchen nayi, ina shiga na tsaya ina ƙarema ko ina kallo. Ina irin kitchen ɗin turawa da zakaga kamar bai kamata ayi abinci aciki ba, hasalima yayi Kamada wani wurin shakatawa ne da zaka zauna kaita kallo yana saka nishaɗi, to wannan kitchen ɗin haka yake. Abubuwan cikinsa na tabbata babu ko ɗaya da aka siyo a Nigeria, Ac har biyu a cikin kitchen ɗin. Nama rasa ta ina zan fara tunda ba gane kan gidan nayi ba. Wani ƙofa nagani ta gefe, shiga nayi inda naci karo da food pantry mai ɗaukeda nau'ikan abinci kala kala babu wadda babu, saida nagama santina sannan na ɗebo iya wadda zan dafawa cikina, dan ba'ayi mutumin da zan ɓata hannuna wajen girka masa abinci ba🙄 Tukunya mai kyau na ɗora saman wuta. Sharp sharp nafara prepping kayan miya kafin ruwan yayi zafi na parboiling macaroni twist ɗina. Bayan na gama shirya abincina ko ina ya kaure da ƙamshi mai daɗin gaske. Jollof ne macaroni dayaji ice fish dasu carrots da sauransu sai plantain frittata da kuma banana smoothie nayi, akan tray na shiryashi ma fito zuwa dinning dake can gefen falo. Saida na aje saman dinning ɗin na tuna ban dauko ruwa ba, sharp sharp na koma kitchen na ɗauko goran ruwa na fito, ina farinciki yau Finally zanci abincin dana girka dakaina. Raina yayi baƙi kirin lokaci ɗaya annurinn fuskata ya bace har bansan lokacin dana furta "kan bura uba🙀" wai duk lokacin dana ɓata ina girki a kitchen dan kawai inci abinci mai kyau da lafiya shine mutuminnan ya haike saman kujera yana afkawa cikinsa abincina?baimasan ina bayansa ba, aharzuke na ƙarasa wurin dinning ɗin nayi sama da plate ɗina kirjina na sama da ƙasa saboda haushi. Ban maso inyi masa magana kawai najuya da taguwar abincin dake cikin plate zuwa kitchen, ina shiga na rufe kofa bammm na zauna saman Island ina danasanin kai abincin falo. Gashi ya rage mun aukinta😡. Tunda ta wuce kitchen yakasa kyafta ido, wai me yarinyan nan take nufi dashi ne. Gaskiya yakamata ayita ta ƙare kawai, Allah ya kaisu anjima bari ya dawo gida da yamma sai ta yabawa aya zakinta. Rigan suit dinsa ya ɗauka saman dinning da jakansa ya wuce waje. 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Ba'a yaɗa aihuwan Ameera a family ba aboda sunsan cewa magana kawai za'a fitar marasa amfani. Alhamdulillah jikin mai jego da sauƙi yanzu ba laifi. Tunda Amin yadawo jiya wanka kawai ya kaishi gida amma throughout yana nan a asibiti tareda masoyiyarsa. Su Abby ma dasuka zo zo dubata,ganin irin lob da ake zubawa wadda babu wanda yayi tsammaninsa kawai aka fita aka barsu. Abby ya riga ya yanke shawarar aranan sunan yaron za'a Daura auren iyayen. Alhamdulillah jikin baby ma ana samun cigaba, daga juya zuwa yau a cire masa oxygen amma kuma still yana cikin ƙwalba duk da yanada ɗan girmansa baza'a kirashi bakwaini irin sosai dinnan ba. Mamy da Innati sune suke zuwa dubashi time to time, Ameera sam taki zuwa, sun ɗauka kunya takeji amma itafa haka kawai taji bawani son ganinshi takeyi ba( ke Ameera zakiso uban ɗa kice baki damu da ɗan ba🙄 meya miki, iyye nace meya miki🙄). Tunda Goggo tashigo garin Kano tace itada komawa Adamawa. Afadinta wai ai surkuwarta mai kuɗi ce dan haka itada talauci sunyi hannun riga. Da yamma ta sauka a gidan Jenar, da ƙyar aka barta ta shiga, dan ma lokacin Amin na gida bai koma asibiti ba, shine yasa sojojin suka barta ta shiga. Baba Larai ne kawai agida, duk mutanin suna can wurin mai jego. Sai wani isa da gadara Goggo keyi a gidan Hajja tana buɗe hammata ita ga surkuwar Innati (cab, amma hali bazai taɓa canza wa ba wannan tsohuwar🙄). Haka tasa Baba Larai ta jera mata nau'ikan abinci akan dinning, daga ta tsakura wannan sai ta caccaka wancan. Bayan ta gama tace mata wai takaita Dakin innati tunda itace take gadara da. Baba Larai kuwa bini bini take mata abinda ta umurta tunda surkuwar ƴarinyar gidance. Wanka Goggo tayi ta male male saman gadon Innati dayasha gyara ga shegen laushi kamar auduga, gefe kuma ga Ac. Haba tuni Goggo tahau mota zuwa Adamawa, sai jan munshari take kamar saniya "khauuuuuu khauuuu kurrrr" inta ɗago saita aje 🤣🤣. Su Innati basu tashi dawowa gida ba sai ƙarfe takwas na dare, sun baro Mamy ne da Amin a asibitin. Batasan da zuwan Goggo ba sai da tashiga ɗaki kawai taga mutum akan gado har yanzu bacci takeyi, da farko taso tayi ihun aljana amma data kalle gefenta can ƙofan bayi taga Ghana must go ɗin Goggo wadda ya gama kyamushewa. Mamaki ya kamata, meya kawo Goggo garin Kano, batazo bikin Aneesa ba sai bayan auren take zuwa. Kodai har yanzu tana tunanin cewa Innati na matsayin matar ɗanta ne shiyasa ta tako ƙafarta har Kano tazo gidansu har wani bacci take mata agado,ina ruwan ba'a saba ba. Murmushi tayi kawai ta girgiza kai tawuce bayi dan yin wanka. Harta fito ta shirya cikin kayan baccinta, tukunna lokacin Goggo ta farka. Ko salati babu tasaki wani dogon miƙa tana girgiza kamar mai farfadiya. Kallon Innati tayi dake gaban dressing mirror tana taje dogon gashinta dake zube har ƙugunta wadda yasha gyara yana sheƙi da ƙamshi ba kamar lokacin datake gidan Zaidun ba. Ikon Allah Goggo ta tsaya kallo, ashe dama haka matar ɗannata keda kyau bata sani ba. Ta shagala da kallonta har Innati ta gama ta juyo tace "Goggo sannu da zuwa" firgigit ta dawo daga kallon tsananin kyau tayi murmushin yaƙe tace "yawwa Hajiya Hussaina" (ikon Allah, inkanada kuɗi tsoho ma har ƙasa zai durkusa ya gaidaka😂). Galala Innati ta tsaya kallon Goggo da wani kininibi, yaushe ta zama Hajiya uhmm. Bata nuna mata komai ba kamar ma batasan me ita da ɗanta suke shiryawa ba. Barin ɗakin tayi mata bayan tasa akawo mata abinci da duk wani abinda take buqata, ɗakin Hajja take. Hajja tayi mamakin ganin Innati adakinta wai kuma da niyyar kwana. Da Innati tayi mata bayani, gyara kwanciya kawai tayi tace. "Allah ya kyauta". 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Sai ƙarfe tara yadawo bayan ya gama duk wani aikinsa a waje. Yau shiri na musamman yayiwa yarinyar nan, Hausawa sunce da zafi zafi ake lanƙwasa ƙarfe, gara tun yanzu yakoyamata lesson tasan cewa yanzu aƙarkashinsa take tadaina rena masa wayo. Da sallama abakinsa ya shigo gidan, bai tadda kowa afalon ba kamar kullum, sauri yayi ya haura sama zuwa ɗakinsa. Wanka yayi ya fito dagashi sai towel ɗaure aƙugu, ga gashin kansa dake zube kan kafaɗarsa sai ɗigan ruwa yake. Kirjinsa dame sumul babu ko gashi looks so sexy 🙈 abs ɗinsa sun fito ɓaro baro ya haɗu da vline ɗinsa haka ruwa ke gangarawa yana bin line ɗin yana shiga towel🙈. Gaban dressing mirror ya tsaya, hand dryer ɗinsa ya jona a wuta ya drying kansa ya shafa mayuka kamar na mace, feshe jikinsa yayi da turaruka masu ƙamshin gaske da kama jiki. Minti bubble gum ya jefa cikin bakinsa yana taunawa ahankali, closet ɗinsa ya shiga minti kaɗan ya fito da kayan bacci ahannunsa. Riga ne dogo wadda ya wuce masa guiwansa kalar honey colour irin mai igiyar afefennan da aljuhu agefen hagu da dama. Bayan ya saka ya feshe jikinsa da turare kuma ya sanya bedroom slipper ya kwaso wayoyinsa ya fito aɗakin bayan ya kashe wuta. Aneesa's POV Fitowata kenan daga wanka, ina zaune saman stool ɗin gaban dressing mirror ina share gashin kaina dana gama wankewa. Towel ɗina iya mazaunaina ya tsaya, ahakama dan najashi kasa kaɗan kusan rabin ƙirjina na waje. Bayan na gama shafe shafe na miƙe zan ɗauki kayana akan gado, dama tuni na riga na fitar dasu. Wani irin mummunan faduwar gaba naji ganin mutum zaune akan gado idonsa ƙar akaina. Saurin danne tsorona nayi na matse fuska, bance masa komai ba na ɗauki kayana dake gafensa zan wuce najin kamo hannuna, afusace na juyo zanyi masifa kamar yadda na saba naci karo da farfaɗan ƙirjinsa. Ɗagowa nayi ina kallonsa can sama amma tsabar rashin tsoro irin nawa na dake nace "ka sake mun hannu inje in sa kaya" ko gizau baiyi ba, ƙwace hannu na nayi ina gallara masa harara. Watau ma maza da basuda kunya, kan uba. Ka wanke mun mari da safe yanzu kazo kana kashe mun ido tsabar rainin hankali. Abinda ya ƙara mun baƙin ciki shine dariyan danaga yanayi mun, watau Ni ya maida mahaukaciya kenan. Ina ƙoƙarin ƙwace hannuna yayi saurin sa hannunsa ya zagaye ƙuguna dashi ya matso dani gab dashi sosai muna mannuwa da juna. Makwat na haɗiye yawu, bansan mene ne a idanunsa ba, kamar wasu sparkles ne da ban taɓa ganin irinsu ba, kodai saboda ban taɓa kallon idanunsa bane. Daidai kunnina ya rada mun wai "You look so damn hot baby" afusace na tari numfashinsa nace " nabi hot da gudu ba wando😂 Dallah Ni mlm ka sakeni inje in sa kaya" wani dariyan ya kumayi a shaƙiyance wadda yasa dimples dinsa lotsewa har ciki, kiciniyar kwatan kaina nafarayi inaji towel ɗina na ƙoƙarin bani kunya. Shi kuma kamar da niyya yasa hannu akan mazaunaina ya fizgo towel ɗin ta kasa, nashiga uku🙆. Wannan karon dariya mai sauti yayi yace "yau za'a raba gardama. I'm daring you tonight, ki ƙwace kanki. In har kikayi nasara namiki alƙawarin zan miki duk abinda kike so yau ɗinnan ba sai gobe ba" yana faɗin haka naji yayi sama dani ya aje kan gado, be kaiga haurawa ba nayi saurin sauka na jawo towel ɗina nayi na ƙofa. Har zan buɗe baki ƙit kit an rufe, juyowa nayi naga wani ɗan ƙaramin remote ahannunsa ya riƙe yana mun wannan shu'umin murmushin dana tsana. Kuka ne kawai banyi ba, amma zuciyata tuni ta gama tsinkawa. Yau kome zai faru I'll never give in kamar jiya dayaci galaba akaina. Ina ganin yayo kaina gadan gadan nasha kwana aguje nayi na closet ɗina, fincikoni yayi da ƙarfin gaske ya ɗaga sama, wannan karon kam fuskarsa babu wasa. Bazan ce yana cikin ɓacin rai ba, ina irin fuskar da mutum keyi idan zai yi mugunta ɗinnan, to shi yayi. Da ƙarfi ya jefani saman gado, towel ɗina ya Kuma kuncewa. Da nace bazan ƙara kuka agabanshi ba amma dana ga bala'in dayafi na ƙarfina, tuni na fashe da kuka wiwi ina rokonsa. Murmushin mugunta yayi yaɗata tube rigan jikinsa, runtse ido nayi na tattaro duvet ina kare kirjina dashi. Haurowa yayi ya jawo ƙafata na koma straight, shammata na yayi da faffadan ƙirjinsa gafara sakar mun kiss kamar mayunwacin zaki tako ina da bakinsa me iya kaiwa. Azafafe na kai masa yaƙushi a jikinsa, amma kamar karfi nake ƙara masa. MJ ya ɗau wuta tuni, komai azafafe yake mata saikace baisan first timer bace. Abubuwan dake rikitashi shiya damƙe guda ɗaya, na biyun kuma ya kai masa chafka yana tsotsa cikin fitar hayyaci. Ga hannunsa dake yawo a sauran bangarorin jikinsa, bai damu da kukanta ba kuma bai damu dayayi foreplay da ita ba, all he wants is to just do it. Shi kansa bai san lokacin daya bincike wandonsa gefe ba ya rufesu da duvet, cinyoyinta ya raba gida biyu yafara karanta addu'a. Ina ji yasa hannu ya raba cinyoyina ya karanta addu'a, hankalina ya ƙara tashiwa, wannan addu'an ko bacci nake idan aka karantota nasan na menene saboda ana yawan yi mana bitanta a islamiyya, "inna lillahi wa inna ilaihi raji'uun" shine kalmar daya fito abakina a lokacin danaji kamar an soka mun mashi aƙasa na, kamar mahaukaci dake tseren gudu haka yake kiɗinsa da rawansa. Ihu na saki wadda na tabbata sojojin gidannan Gaba ɗaya sunjushi tunda ko ina tsit yake. MJ ya shiga duniyar da ya mance rabonsa da shigar ta, aiki kawai yake ba kama hannun yaro, bai damu da ƴar mutane dake ihu tana neman agaji ba, bayaji baya gani kawai yake bugunta yadda kasan ba ƙaramar yarinya ba. Shi kansa ihun yake zubawa, lallai su Hajja sunyi kokari, me suka ɗurawa ƴarinyar nan haka. Shi inba karya zai yi ba dasai yace ko Neehal batayi masa jwain haka ba. Ihu yake yamance cewa basu kaɗai bane a gidan. Daya gaji da style ɗaya, ya juya yarinya yacigaba da aiki ko tausayawa ba. Saidai yadauki tsawon lokaci sannan ya saketa ya mirgina gefe ya kwanta yana maida numfashi yadda kasan yayi tseren gudu da wani. Itako Aneesa tuni tamance awace duniya take. Ta daisan babu kowa a duniyar face ita kaɗai, duhu ya mamaye ko ina bata ganin komai. Gashi tanajin zafi amma takasa motsa koda yatsarta ne🥹🥹😭. Haka shima MJ bacci ya ɗaukeshi agefenta bayan yajawota sosai ya rungume kamar jaririya. The next morning.... 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah✍️ PG 81_85 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Kiran sallah ne ya farkar dashi, da salati abakinnasa ya buɗe idanunsa wadda ke ɗauke da bacci. Yau wani irin bacci na musamman yayi mai daɗin gaske. Tana kwance akan hannunsa guda ɗaya ta cusa furkarta daidai ƙiriinsa tagefe har yanzu bacci take amma bata daina ajiyar zuciya ba. Ya shagala da kallonta sosai, wai shi can baya dama abinda yayi sunansa aure? Cab amma ancuceshi, zaqin Aneesa is incomparable, itace ainahin definition ɗin jan miya. Neehal garau garau ce kawai (toh dama zaka haɗa gyaran Nigeria dana India ne🙄). Laƙace hancinta yayi yaja kumatunta ahankali yace "rigimammiya na" ahankali yajata akan hannunsa ya mike ya buɗe duvet zai sauko daga kan gado, idanunsa ne ya sauka akan abu wadda kalansa yayi daban da colour ɗin bedsheet. Hannunsa yakai gurin wani button dake maƙale agefen gado ya kunna haske, mummunar bugawa kirjinsa yayi ganin jini caba caba ya ɓata gado ya ɓata musu jikinsu. Arude ya juya wurin baiwar Allah yana ɗan bubbuga kumatunta yana kiran sunanta amma shiru. Hankali atashe ya wuce toilet da sauri ya watsa ruwa sharp sharp ya fito da towel ɗaure aƙugunsa bayan ya haɗa ruwa mai zafi a bathtub. Yaye duvet ɗin yayi ya sungumeta kiiii zuwa toilet, ahankali ya ajeta cikin ruwan zafin, wuffff kuwa ta buɗe ido kamar mai aljannu, azababben ihu ta sake ta ƙankame dantsen hannunsa ta fara ƙoƙarin tashi acikin ruwan, baiyi amfani da force ya dannata a ruwan ba, amma bai bai bari ta tashi ba. Kamar zai yi kuka irin ihun azaban dayaji tana yi, sosai yake jin abun har cikin zuciyarsa. Saida ya gasata na minti biyar haka kafin ya tsiyaye ruwan wadda duk ya koma kalar jaa, wani ruwan ya kuma haɗawa ya mayar da ita ciki, wannan karon ma kasa kukan tayi, sai hawaye kawai. Aneesa ba baki takasa budewa tayi masa magana. Tariga ta tsorata dashi matuqa, tayarda babu wani sauran imani atattare dashi, zuciyarsa abushe take ƙamas kamar na fir'auna. Bayan ya gama shida kansa yayi mata wanka harda na tsarki. Yanata kula da yadda taki kallonsa ko kaɗan, gashi takasa buɗe baki tace masa uffan itadai nata ido mai hawaye . Ahannu ya ɗauketa kamar jaririya suka fito daga toilet ɗin. Ajeta yayi kan sofa ya yaye bargo da bedsheet dasuka ɓata ya kai washing machine sannan ya dawo ya canza wani kafin ya maidata. Dogon jallabiyarsa ya zura mata ya ɗauko hijabi ya sanya mata, shima ya shirya yashimfiɗa sallaya yajasu, harga Allah bazata iya tsayuwa ba dan haka azaune tayi nata Sallan. Koda suka idar ya juya ya kalleta tayi saurin ja da ido gefe tana yamutsa fuska. Tsabar neman magana saiya miƙe ya kwanta saman cinyarta yana ƙara kallon fuskarta. Ita dai batace masa komai ba, to me zata ce masa. Ai ita yanzu sunanta sorry, tazama second hand babu wani takama da rashin kunyar dazatayi masa. Wayarsa dake gafensa ya ɗauka ya kira doctor ɗinsa akan yazo ya duba masa Madam. Doctor kuwa kamar yasan abinda ya faru, tundaga asibiti ya haɗa magunguna ya zuba ajakansa, yasan MJ ba bari zai yi ya duba abun ba😂. Sai da ƙarfe 6:30 AM yayi kafin doctor ya iso. Cire mata jallabiyar yayi ya canza mata zuwa T-shirt da zanin kayanta wadda tazo dashi. Shigowa doctorn yayi MJ yayi masa bayanin cewa bata jin daɗi ne. Pain killer injection ya fitar ya kaɗa yasa MJ ya riqe mata hannu zai yi mata alluran. Duk wannan shawagin da akeyi Aneesa na kan gado gum batace komai ba, jin tsinin allura afatar hannunta yasata sakin kuka tana ƙoƙarin ƙwace hannunta, kallonta doctor yayi yana mamakin irin wannan raki nata. Ita data iya enduring pain ɗin first s*x meye Kuma allura. MJ da jiyake inama zai cire zafin ya mayar jikinsa ko zata samu hutu. Magungunan doctor yabashi yayi masa bayanin yadda zai bata shi sannan yayi masa sallama yatafi bayan yayi masa bayanin bata buqatar ɗinki kawai yarika yi mata hot water sit bath akai akai hakan zai taimaka mata wurin warkewa da sauri. Ajiyar zuciya kawai take saukewa, inda tasan ba iya duka lamarin MJ ya tsaya ba da ina ita ina yi masa rashin kunya, ai daga yau ko uhmm bazai sake hadata dashi ba, she has learnt her lesson. Fitowa MJ yayi farfadan gidansa inda sojojinsa ke kai komo, ga mamakinsa duk wadda ya haɗa ido dashi sai yayi saurin kauda kai ƙasa kamar mara gaskiya, idan ya juya kuma sai yaga suna ƙuskus saikace sun zama mata. Shi bai ma kawowa ransa cewa sunji wani abu ba, umurni yabawasu kan cewa duk su tafi yabasu hutu na kwana biyu, iya mai gadi kawai da driver za'a bari amma duk sauran Sutafi saiya neme su. Yana komawa ciki ya shiga kitchen, apron ya daura ajikinsa da babu riga sai dogon wandon jeans. Ashe dama MJ ya iya abinci🙀, gani nayi ya fidda indomien China wadda ake kira ramen sai kwai guda biyu. Ruwa ya ɗora saman gas, yafara yanka su abarba da Apple ya aje gefe guda. Bayan ruwansa ya tausa ya zuba indomien aciki ya zuba seasoning ya rufe. Ko ina na kitchen ɗin ya kaure da ƙamshi mai daɗi, bai jima ba ya gama komai ya zubo indomien a plate yayi shi ruwa ruwa ne sai faman turiri yake. Karamin mug ya ɗauka ya haɗa tea aciki, gefe kuma ga fruit salad dayayi shima duk ya jera saman tray sannan ya kunce apron din jikinsa ya sungume plate ɗin zuwa ɗaki. Har yanzu bacci take, kana kallon fuskarta kasan taji maza. Ina irin table da ake ajewa marasa lafiya akan gado a asibiti, wadda turawa ke kira da breakfast in bed. Shi yayi mata, ahankali yafara tashinta. Arazane ta buɗe ido tana neman direwa daga kan gadon, wani zafin dataji aƙasanta shiya sanyata nutsuwa tana cije laɓɓan baki, kallon abinci tayi saman gado sai turiri yake, haushin abincin ma take. Aikin banza agama cutarka azo ana tarairayaka. To shin wai shi ɗin baiji zafi bane sai ita kaɗai? Hararansa tayi ƙasa ƙasa takoma ta manne da gado tana matsar ƙwalla duk da yaƙi fitowa😂. Murmushi yayi ya zauna agefenta yakamo hannunta ahankali yake murzawa cikin cool voice yace "sweetheart kiyi haquri, nasan ban kyauta miki jiya ba. Nima bansan meya faru nayi hakan ba, I'm sorry please" ko ci kanka bata ce masa ba, ya ƙara magana ta shareshi bai daddara ba ya kumayi ta shareshi, narai narai da ido yayi kaman zai yi kuka yace "baby pls now. Is that what we're gonna do now, silent treatment? Dan Allah kiyi haquri talk to me plss" hawaye na taruwa a idonta baki na rawa tace "nabarka da Allah" daga haka bata ƙara ce masa komai ba. Girgiza kai yayi, ya taɓowa kansa tsuliyan dodo shi Mujahid😂 Lallabata yafarayi akan ta daure taci abinci, amma tasha mur tayi kamar bada ita yake yi ba. Gwadata yayi ta hanyar cewa idan bataci ba zai maimaita abunnan na jiya da daddare, kodan haka yana tunanin zata ci abincin amma shegen taurin kai irin na Aneesa ko kallonsa bata yiba. Abun ya fara damunsa, yarinya mai shegen tsiwa da rashin kunya amma yau itace bakinta yayi gum saikace mai ciwon hakori, lallai ashe duk mace mara kunya dan bata shiga hannun daidai da ita bane🙈. Durƙusawa yayi har ƙasa ya kamo hannunta yana shafawa yace "dan Allah Neesa kiyi mun koma menene amma kar ki bar mun kanki da yunwa. Kiyi haquri kiyi wa Allah badon halina ba ki daure kici abinci " amaimakon tayi masa magana ma sai gyara kwanciya tayi ta juya masa ƙeya. Hannu yakai ya taɓata ta buge masa hannu taja bargo ta rufe ido kaman mai bacci alhalin ba baccin takeyi ba. Duk juyin duniyannan MJ yayi dan ya shawo kanta amma tamaidashi banza. Haka ya haqura ransa na ƙuna ya dauki trayn abincinsa yafita daga ɗakin. Tanajin ya fita kawai taji wani kuka ya taso mata, saida tayi kukanta son ranta sannan tayi bacci. Safa da marwa yake acikin ɗakinsa yana neman mafitan abinda zai yi. Wani abu yace masa ya gwada searching a net me zaiyi ya sauko da ita daga fushin datake. Computer ɗinsa ya ɗauko ya zauna abakin gado yana searching, an bashi options dayawa. Duk ciki babu wanda yayi masa. Jefar da system ɗin yayi ya kama kansa da hannu biyu, gashi ba isasshen lafiya ne da ita ba, idan bataci abinci ba to ya zai yi. Wayarsa dake gafensa ne ya fara ƙara, ɗagawa yayi yana kallon sunan daya fito saman wayar. Mamy ce ke kiransa, da sauri ya ɗaga saboda tun kwana nawa yana kiransa amma bata dagawa, gaida ita yayi amma ta shareshi ta hanyar faɗin "kabawa takwarar Hajja waya, inaso nayi magana da ita. Ba kai nakira ba" cire wayan yayi yana kallonsa, har yanzu fushi sukeyi dashi kenan ikon Allah. Asanyaye yace "Mamy bacci take, batajin daɗi" wani mummunan bugu zuciyar Mamy yayi, itadai iya saninta Aneesa ba son MJ takeba ba balle ace har ta sake da zaiyi mata wani abu, Allah yasa ba dole yayi mata ba. Cikeda fushi Mamy ta daka masa tsawa "Allah Mujahid ka fita Idona, ka tabbata idan wani ya sameta mu da kai ne agidannan. Ka kula mana da yarinyar mu, karka cutar da ita, kadaina ganin Hajja ta goya maka baya, wlh wani abu ya sameta mu kanmu bazamu kai Hajja zafi ba inhar akan takwararta ne. Aikin banza kawai, idan ta tashi ina so nayi magana da ita" kit ta kashe wayarta bata jira cewarsa ba. Wani iska mai zafi ya fesar, Ya Ilahi, kenan shi ba'a damu da shi ba. Ba'a damu da abinda zai sameshi ba duk wannan fushin dasuke nuna masa. Uhmmm, aje wayan yayi ya mike ya fita aɗakin. Yana shiga ɗakinta ya tarar ta farka tana ƙoƙarin tashi akan gado, kamar superman yayi saurin tareta yana ganin zata fado ƙasa, kamar ɗaxu yanzu ma haka, babu abinda tace masa. Miƙewa tayi cikin aro jarumta tafara ɗingisawa tana ware kafafu kamar wacce akayiwa kaciya, tana tafiya tana cije lebe bataso ya gano cewa har yanzu tana buqatan kulawarsa. Kowa yayi ta kansa kawai. Idan ya gaji da rashin maganarta gareshi sai ya maida ita gida wurin mahaifiyarta. Yana zaune anan har ta shige toilet. Da farko yayi tunanin binta ko zai tayata gasa kanta, amma dayayi tunanin cewa karyaje ya ƙara tabo wani abun kawai ya ƙyaleta. Acan bayi kuwa, saida ta kara gasa kanta sosai, tanayi tana hawaye, ji take kamar ta fasa ihu idan ruwan zafin ya taɓa wurin amma bataso ya shigo bayin,dan ganinsa ma kawai kamar zafi yake karamata. Takai kusan awa ɗaya abayin sannan tayi wanka da alwala ta fito. Yana nan zaune bai tafi ba, yi tayi kamar bata ganshi ba ta wuce gaban dressing mirror ta ɗau hand dryer ta jona tafara busar da kanta. Sai ido yake binta dashi, gaskiya yarinyar nan zata sa masa ciwon zuciya, wannan kyau har ina. Inda zata sauko suyi zamansu cikin soyayya, dako babu wadda zai kaishi jin daɗin haka. Duk da yunwa dake addabar hanjin cikinta amma bata bari yagano ba. Shiko bawan Allah yabi ya damu. Da daddare bayan Sallan isha'i ta lallaba ta sauko downstairs dan yunwan datakeji. Sharp sharp tayi ɗanwake da ƙwai biyu sai ruwa agora tafito tawuce ɗaki. Ko lura dashi batayiba yana zaune afalo yana aiki, shi kuwa yaga shiganta shiyasa ya dawo falo ya zauna duk tunaninsa a dinning zataci abincin amma sai yaga tawuce ɗaki. Miƙewa yayi ya bi bayanta, akan stool ɗin dressing mirror yasameta tanacin abincinta cikin kwanciyar hankali. Murmushi yayi ya rufe mata kofa kar ganinsa yasa taji abincin ya fita mata arai. Kano... Daga Hajja har Innati da sauran mutanin gidan kallon Goggo kawai suke, sai wani isa da gadara take da ma'aikatan gidan kai kace itace ma me gidan Gaba ɗaya, idan tasa ayi mata wani abu in suka ce ai bahaka ake yi a gidan ba sai tafara masifa tana cewa ko sunsan ita wacece agidan. Itacefa surukar Innati, suko intayi musu barazana da wannan sai suyi mata abinda takeso. In kuma wurin cin abinci, haka ta zauna a kujerar da Hajja take zama, kawaici kawai yasa Hajja batayi mata magana ba. Jira kawai take ranan da Allah zai kawo Abba gidan yazo yace yanaso Innati ta koma gidansa, alokacinne zaninta zai kunce musu ta zazzage musu abinda ta daɗe tana tarawa. Da daddare ma haka, tayi ƙane ƙane agadon Innati, kamar jiya haka yau ma Innati takuma kwana aɗakin Hajja saboda munsharin Goggo ko saniya albarka😂. Duk da zaman Hajja a gidan, batasan cewa Ameera ta aihu ba, asalima ko tambayarta batayiba. Ta dai san wunin yau su Innati da sauran mutanin sun fita basu daɗe a gida ba. Washe gari aka sallamosu Ameera daga asibiti, yaro yayi girman da za'a iya barin su su dawo su cigaba da kula dashi agida. Motoci biyu sukayi aka dawo gida. Yaron na hannun mahaifinsa suka fito daga motar. Aɗayan motarsu Hajja Ameera ta zauna, itama ba laifi taji sauki sosai, saidai tana buqatan wanka ne mai kyau dan ba samu takeyi a asibiti ba. Tunda Goggo ta leƙa daga sama ta hango duk sun fito daga motoci, ga kuma jariri a hannun wani ɗan saurayi kyayyawa, taɓe baki tayi. Sai alokacin ma ta tuna da Ameera wacce ke takowa ahankali, tana riƙeda hannun Mamy har suka shiga side ɗinsu Raihanah gaba ɗayansu. Son jin ƙwaƙwaf irinna Goggo yasata fitowa daga sashin Hajja tayi nasu Mamy. Alokacin kuma suna zaune afalo, anbawa Ameera jaririn ta shayar dashi, sai a lokacin zai fara shan nono direct dan a asibiti cup and spoon ake bashi ruwan madara. Ameera na riƙeda ɗanta yana zuƙan nono ahankali sai yatsina fuska take jin uban zafin da maman nata keyi mata, itafa badon an tilasta ta ba bazata shayar dashi ba. Ko sallama babu Goggo ta ƙusa kai cikin falon, mummunar gani tayi ta saki salati batareda tasani ba. Dafe ƙirji tayi tana xaro ido waje tace "menake gani haka, Ameera kece ke shayar da yaro? Yaushe har kikayi aure bamu sani shine har kin aihu. Kodai .... Inna lillahi wa inna ilaihi raji'uun " tafaɗa tana tafa hannu, kowa na falon hankalinsa ya dawo kan Goggo daketa faman zuba ita kaɗai. Badon komai yasa aka kawo Ameera part ɗin Mamy ba sai dan gujewa hantara irin nata, ashe dai sun gudune basu tsira ba. Tuni Ameera ta zare bakin nononta abakin yaron, shi kuwa innocent soul ya ɓare baki yana tswala ihu. Amin ya karɓeshi yasa akafada yana jijjigashi. Hajja ranta yayi baƙi ƙirin, wannan matar fa idan bawani ya taka mata burki ba sai ta nemi jawo musu kata'i. Zata miƙe Innati tayi saurin kamo hannunta ta girgiza mata kai. Itako Goggo ta kallesu tace "Hussaina bar hanata,ƙyaleta ta faɗa mun abinda kunnena keson ji. Ince dai ba iskancin nata taje tayi takawo muku ɗan shege ba" wuff Amin ya karbe ta hanyar faɗin "nidai ɗana ba ɗan shege bane, nine ubansa kuma ako ina ina alfahari da hakan. Karki kuma ce masa ɗan shege sunansa Aadil", kasa cewa komai Goggo tayi ganin jikanta na maida mata magana ba kunya. Murmushi Mamy da Ammi sukayi, lallai Amin zai zama uba mai kare ɗansa ako ina,kuma agaban koma wanene. Allah kawai ya kiyaye gaba amma ba'a fatan hakan ya ƙara faruwa koda kuwa ba'a kan Amin bane. Wannan amsar da Amin yabawa Goggo shiya bawa Kowa satisfaction. Itako Ameera ƙin bawa yaron nono tayi tana kallonsa ahannun Amin yana tsala ihu. Sum sum Goggo tajuya tafita amma bawai donta bar zancen kenan ba, tabbas sai tasan yadda akayi yarinyar nan tasamu ciki har ta aihu. Da kyar Ameera ta yarda ta karɓi yaron ta maida masa mama abaki, da sauri ya cafka har saida ta saki ihu, minti kaɗan yayi bacci aka kwantar dashi, itakuma Mamy ta haɗa mata ruwan wanka mai sauƙin zafi aka yi mata wanka dashi. Port Harcout Navy Base. Yau sojoji sukaje airport tarban yarinyar Naval Commander wacce tagama training ɗinta a ɓangaren likitancin sojoji a ƙasar US. Danƙararrun motoci ne aka shirya domin tafiyar, suna isa airport suka jera layi both sides ana jiran saukowarta daga jirgin, Ya Isma'il na hango agaba shine yake riƙe da flower wadda za'a bata idan ta sauko. Yayi matuqar kyau cikin kakin sojoji, ƙaramin bindiga na gefen aljihunsa, yasha mur babu fara'a a tattare dashi, gashi yayi rama wadda idan kasan shi to tabbas sai kasan cewa ya rame kuma yana cikin damuwa. Saida kowa ya gama saukowa suna tsaye suna jira. Ƙafafunta dake sanye da takalmin mai tsini irin mai igiyoyinnan ta sanya awaje kafin ta fito. Tsayuwa tayi can saman benen jirgin tana karewa jama'an airport ɗin kallo. Sanye take cikin Simple material brown colour tayi rolling da veil ɗinsa, Ga handbag dinta na Bottega veneta shikuma Black colour, sai spec data makala a idanunta masu duhun haske, tsinin hancinta zar dashi kamar itace ta zana abunta. Ahankali tafara taka matakalan jirgin tana saukowa cikeda class, har ta sauko wurin sojojin inda sukuma suka standing at at ease suka saluting dinta. Ya Isma'il dake riƙeda flower yaɗanyi murmushin yaƙe ya miƙa mata flowern sannan cikin cool soothening voice dinsa yace "you're welcome dearest Dr Habiba" saida wutan kanta ya ɗauke ɗif jin wannan zazzaƙar murya daga kyakkyawan Matashi mai jida jini ajika. Kusan seconds talatin ta ɗauka tana kallonsa ba kyaftawa sannan tayi saurin dawowa hayyacinta ta karɓi flower tana murmushi tace" thank you" ganin duk wannan washe bakin datake Ya Isma'il bai damu da itaba yasa itama ta matse fuskarta tayi gaba suka bita abaya. Wani G wagon baƙa aka tanada dominta, itada driver sai Ya Isma'il na gaba agefen mai zaman banza, kunninsa saƙale da Bluetooth yana kallon waje har suka fara tafiya. Itako Habiba sai kallonsa take tana adkiring irin kyawunsa. Gaskiya ta fola, Allah Allah take ta koma gida tasamu Dad ɗinta tayi masa magana. Suna isowa tangamemen gidan Babannata akayi parking sojoji suka buɗe mata kofa ta fito. Mun ɗinta da yayanta Salahuddeen suna tsaye abakin ƙofa sai washe haqora suke. Da gudu Habiba ta sauka daga motar ta wuce wurin mamanta ta rungumeta da kyau tana zuba mata shagwaba. Lakace hancinta Salahuddeen yayi yace "yarinyar mum andawo kenan bamuda sukuni" turo baki tayi ta sake maman nata ta juyo tana baza ido ko zata hango crush dinta. Can ta ganshi yana tafiya shida sauran Juniors ɗinsa zasu shiga mota. Da gudu tabi bayansu har su mum sun ɗauka wani abune. Daidai zai shiga mota yaji ta kamo hannun rigar kakinsa, juyowa yayi dan ganin wanene ya kama masa riga, kallonta yayi da mamaki yace "what's the problem" ɗan murmushi tayi tace "amm dama am just wanted to thank you for the flowers" da mamaki yake kallonta, bai wani son dogon magana dan haka kawai ya gyaɗa kai, ya juya zai shiga mota yaji ta ƙara kamo masa hannun rigar, ɓacin raine yanzu ya bayyana a fuskarsa, juyawa yayi ya kalleta, ganin tana murmushi yace what again. Sosa ƙeya tayi tace "can I please have your number. Kawai dan mudan riƙa gaisawa. Kaga zan fara aiki a asibitinku na sojoji ne, at least idan na saba da daya daga cikinku zaka riƙa nunamin wasu abubuwan" girgiza kai yayi yace "bana aiki aɓangaren asibiti, amma inada aboki acan zan haɗaki dashi" bubbuga kafa tafarayi tana masa shagwaba sai kace wani saurayinta, cikin kissa tace "a'a niai kai nakeso ka nunamin ba wani ba. In kuma bazaka bani ba ai shikenan" juniors dinsa ya juya ya kalla yaga suna yi masa dariya, matse fuska yayi yafara kiran numbern ba tsayawa. Allah yayiwa Habiba kaifin kwaƙwalwa, duk da bata riƙeda wayanta a lokacin amma har ta iya haddace numbern a lokacin dayake kiranshi, yana gamawa ya shiga motarsa suka wuce, itakuma tawuce gida da gudu inda su mum ɗinta ke tsaye, ko takansu batabiba tacigaba da kiran numbern tana gudu har ta shiga ɗakinta inda aka aje mata handbag tabude ta ciro wayarta ta dialling numbern. Tana jin ya shiga ta daka tsalle kamar zata fadi ƙasa, shi kuwa on the other side yaga baƙuwar lamba ce ke kiransa amma ya ɗauka, tanajin an dauka ta saki murmushi bata ce komai ba, "Hello, who's there" taji ya faɗa cikin sanyin murya, da sauri ta kashe wayar ta saving numbern da "Bae to be❤️" (lallaine zaƙaƙura😂) tana cigaba da murmushi, mikewa tayi ta shiga toilet. Abuja.. Yau kwana uku kenan kamar kullum tunda abunnan ya shiga tsakaninsu har yau Aneesa batayiwa MJ magana. Bawan Allah yashiga damuwa matuƙa, to menene zai yi mata kuma wadda zaisa ta yafe mishi, yayi iya ƙoƙarinsa Allah ma shaida ne. Da wanne zaiji, da fushin iyayensa ko kuma da fushinta. Itakuwa duk tabi tasawa ranta damuwa, cikin kwanaki uku nan tayi wani uban rama, ga wani horon yunwa data ɗorawa kanta, sai dare take cin wani abu light ta kwanta tayita kukan zuci tana tunane tunane. Ita yanzu hankalinta kawai ya karkata izuwa gidane, so take takoma wurin mahaifiyarta da ƴan uwanta, izuwa yanzu jikinta ya warke sarai bata jin zafi kamar da, dan kullum saitayi sir bath. Ganinsa kadai yana sanya mata faɗuwar gaba, kullum idan yazo sai yayita kokarin kanta da hira amma itakam saidai ta zuba masa na mujiya babu bakin magana, dashi har abun ya fara bashi tsoro dan gani yake kodai ta kurmance ne. Shekaran jiya ya kira Hajja kodan zata yarda tayi mata magana yaji menene ke damunta, amma ɗaya bata wayar kin karɓa tayi. Yau kuwa bai je ko ina ba, yana gida throughout. Ya making mind ɗinsa yau dole saitayi masa magana, haka kawai bazai zauna da yarinya tanada damuwa taki faɗa masa ba, salon azo wani abu yasameta ace ai laifinsa ne. Da daddare bayan ya dawo daga masallaci direct dakinta ya wuce baije nasa ɗakin ba, da sallama abakinsa yashiga. Tana tsaye kan sallaya tana sallah, zama yayi saman gado ya zuba mata ido yana kallon yadda take Sallan cikin nutsuwa babu wani kuskure ga karatu datakeyi abayyane saboda sallan isha'i ne, zazzaƙar muryarta yake sauraro irinna masu musabaqa zaddaɗi. Bayan ta idar ta mike ta naɗe sallayar tawuceshi ko gaidashi batayiba. Bin bayanta yayi, kamo hannunta yayi ya jiyar da ita suna fuskantar juna ido cikin ido. Babu wasa afuskarsa amma damuwa na nan yace "what's wrong with you for the sake of Allah. Kimin magana mana nasan ko menene ke damunki. Sokike ki halaka kanki? Baki fa dawani dayafini ayanzu. If you don't share your problems with me who else will you do that with" hawaye na taruwa a idanunta amma bakinnan gum takiyin magana, aharzuke yakama kafadunta ya shiga jijjigata yana maimaita tambayarsa, kuka ta fashe dashi tace "Ni ka ƙyaleni, you're nobody for me to share my problems with, kafita harkana kawai. Ai dama kulawan na karyane, idan kanaso kaganni cikin walwala ka maidani gida kawai Ni bazan zauna dakai ba" tsayawa yayi yana kallonta, tsanan datayi masa yakai har haka? Sake mata kafaɗa yayi asanyaye yace "is that what you want"? da sauri ta gyaɗa kai kamar zata ɓallata, huci ya fesar yace "alright then. Allah yakaimu gobe zan maida ke Kano insha Allah", wani hawayen farincikine ya zubo mata, tayi saurin sharewa tawuce tabarshi a tsaye awurin yakasa motsawa. Shikam soyayya batayi masa rana ba, he loves wholeheartedly amma at the end of the day kowacce da kalar tata, kamar zaiyi kuka haka ya juya ya kalleta, ta haye saman gado ta ja bargonta rufe jikinta dashi. Ya jima yana kallon ta kafin yayi hanyar ƙofa ya kashe mata wuta ya fita aɗakin. 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 Reemah ✍️ PG 86_90 🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Kamar yadda ya faɗa washe gari da sassafe ya sa ta shirya, abun har mamaki yake bashi yadda ta sake wasai sai faman nan da nan take tana shirya kayanta cikin ƴar travelling bag. Ƙarfe takwas suka tafi airport. Ga mamakinta saitaga yasa sojansa ne ya yi mata duk wani processes. Shi kuma suna zaune har lokacin da jirgi zai tashi, duk tunaninta tare zasu tafi amma saitaga ya miƙa mata traveling bag dinta yakama goshinta yayi kissing yace mata "take care. Allah ya kaiku lafiya" yana faɗin haka yayiwa wannan sojan signal yazo su tafi. Har ta fara tafiya sai ta juya ta kalleshi yadda idanunsa suka kada kamar zai yi kuka. Da sauri ta juya tabi bayan wannan sojan ko ɗar bataji azuciyarta ba, ita kawai sotake taganta agida yanzu. Bai tafi ba saida yaga tashin jirgin su, ransa na ƙuna haka ya shiga mota office ɗinsa suka wuce bai koma gida ba. Ko da ya tafi office ɗin kasa concentrating yayi, bini nuni tunaninta zai faɗo masa, Allah kaɗai yasan yadda yake jin yarinyar azuciyarta, he's damn in love with her. Har ma'aikatan wurin saidai suka gane cewa the chairman is not his self today, dan meetings guda biyu important ones yasa akayi cancelling ɗinsu duka. Da wuri ya koma gida tun kafin lokacin yashi yayi. Ƙarfe goma suka iso garin Kano. Taji mamakin irin guard ɗin daya tanada mata, tunda ta sauko daga jirgi guda biyu suke biye da ita. Da suka fito daga airport din kuma motoci biyu aka kawo ɗaya na sojoji ɗaya nata. Ranta ƙal, Allah Allah take ta iso gida. Suna shiga gida akayi parking bata jira abuɗe mata mota ba ta buɗe da kanta ta fito da gudu tayi part ɗin Hajja. Da sallama abakinta ta shigo, tsayawa tayi cak ganin Goggo akan cushion ta kalmasa ƙafa ɗaya akan ɗaya tana ƙurban pineapple juice. Juyowa Goggo tayi ta kalleta tundaga sama har ƙasa, asanyaye ta ƙarasa shigowa falon ta durƙusa har ƙasa ta gaida kakannata. Yatsina fuska tayi ta amsa mata, sannan tace " ikon Allah, yanzu auren kafin yakai sati ɗaya shine har kin dawo. Inbce dai ba wani iskanci kikaje kikayi ba aka koro ki, dan nadan hali" wannan maganar na Goggo ba ƙaramin baƙanta ma Aneesa rai yayi ba. Sosai taji abun a zuciyarta duk da tanada gaskiyan ta. Hajja ce ta sauko daga upstairs sanye da haɗadden atamfa blue da ratsin white ta ɗaura dankwalinsu style ɗin da. Kallon Aneesa tayi wacce ke durkushe agefen Goggo takasa dagowa, tabbas akwai abinda Goggo tayi mata wadda yasa ta kasa tashi awurin ta durƙusa. Allah yasa Mujahid ya kirata yace mata zai yi tafiya ta wata ɗaya shiyasa ya aikota gida kar zaman kaɗaici ya dameta. Murjushi tayi ta ƙaraso cikin falon tace "a'a takwara har kin iso, aikuwa ɗazu mai gidanki ya kirani ya faɗa min kin zuwa. Sannu da zuwa taso mana kin rusuna awurin kamar mai neman gafara" sai yanzu Aneesa ta dago ta kalli Hajja tayi murmushin yaƙe ta mike ko kallon Goggo batayi ba, wucewa tayi wurin Hajja ta rungumeta sosai tanajin wani sanyi azuciyarta, gaskiya aure da wadda bakaso bala'i ne. Saida Hajja ta tsargu da yadda Aneesan ta rungumeta saikace tayi shekara bata ganta ba. Goggo sai jifanta take da mummunan kallo, watau ma akwai munafirci anan, itada ta raineta tunda aka haife ta amma bata saba da ita kamar yadda ta saba da Hajja ba. Hannun ta Hajja ta kama suka wuce sama zuwa ɗakinta, suna shiga saiga Innati tafito daga toilet, da gudu ta faɗa jikinta tana sakin kuka kamar wacce akayiwa mutuwa. Sosai Hajja da Innati suka fahimci akwai wani abu dake damun ƴartasu, ga kuma yadda ta rame kamar tayi ciwo na shekara. Zaunar da ita Innati tayi akan gadonta, suka zauna agefenta Hajja ta kamo hannunta tace "takwara menene, kunyi faɗa da ƴaƴanki ne? Yanaga kin rame mun haka" cikin sheshsheka tace "Hajja, ba komai kawai nayi kewarku ne" duk da basu yarda da abinda ta faɗa ba amma basu so su takura mata shiyasa basu matsa da tambaya ba. Innati kam kwata kwata bata ga komai a zamansu da MJ ba, ta yarda da yaron kuma taga tsantsan son Aneesan a idanunsa bazai taɓa cutar da ita ba. Saida suka rarrasheta sosai sannan Innati tasa tayi wanka ta huta. Wanka tayi ta shirya cikin riga da wando iya guiwa ta faka gashinta da ƙaramar ribbon ta nemi gado ta kwanta tana ajiyar zuciya. Minti kaɗan bacci mai nauyi yayi awon gaba da ita ga Ac yana hura iska ahankali. Sai ƙarfe Uku na rana ta farka, bayan tayi sallah Mamy ta haɗo mata abinci mai rai da lafiya. Sai nan nan suke yi da ita, kodan ganin ramar datayi yasa suka damu, suna ganin kamar akwai abinda ke faruwa tsakanin mata da mijin. Ran Mamy idan yayi dubu to ya ɓaci, saida taja masa kunne sosai amma bai ji ba. Toma wai menene dalilinsa na aiki Aneesan gida cikin ƙasa da sati ɗaya. MUJAHID Agida sai juyi yake akan gado yakasa samun sukuni. He misses her so badly, gashi baida lambar wayarta. Wayarsa ya ɗauka ya kira Hajja lokacin suna tareda Aneesa da Innati agefen Mamy wurin Ameera. Jaririn na hannun Aneesa tanayi masa wasa, ji take inama yaronta ne musamman yadda taga ƴar uwartata take shayar dashi gwanin sha'awa (ware anan, keda kika gujewa mijinki taya zakiyi ciki🙄). Miƙa mata wayar Hajja tayi wai gashi za'ayi magana da ita, bama tasan wai shine ba saida tasa akunne, shiru baice komai ba sai ajiyar zuciya dayake saukewa ahankali. "Hello, Assalamu Alaikum" tafaɗa tana gyara wayar akunninta, kallonta Hajja tayi tace "tashi kije ɗakin Turai kiyi wayar sannan ki dawo" da Aadil ahannunta tafita da wayar saƙale akunninta. Tana shiga ɗakin Mamy ta nemi wuri ta zauna itama batace masa komai ba, suna nan ahaka har mintina biyu suna jin saukar numfashin junansu. Shiya fara katse shirun yace "Babyyy" yadda yaja sunan saida taji wani yarrrr ajikinta. Ummm kawai tace bataƙara magana ba, murmushi yayi wadda yafi ciwo zafi yace "kin isa gida lafiya" nan ma saida ta ɗauki kusan sakan talatin sannan tace Lafiya. Chuckling Aadil yayi wadda yajawo hankalin MJ yace "akwai yaro a wurinne"? Ummm tace, ya ƙara jefo mata tambaya "who's baby" gaba ɗaya ta ƙagu ya kashe wayar, jinta take atakure, guntun tsaki taja wadda shi kansa saida yaji, tace "babyn Ameera ne" da mamaki ya maimaita sunanta yace "Masha Allah, kice ashe na zama Uncle, ki shafa mun kansa zan kirasu na gaidasu" uhmmm kawai tace, daga yadda take amsa masa shiya riga ya gane cewa ta gaji da wayan, at least yaji muryarta, wannan ma kaɗai ya isheshi baccin dare cikin sukuni, Allah ya nuna masa ranan dazata fara sonshi. "Baby love kiyi haquri duk abinda nayi miki, ki yafemun. I'm not gonna force you kidawo gidana, na baki dama kiyi zamanki har lokacin dakikaga You want to come back. I just want you to know that I love you so much. Allah ya cigaba da kasancewa tareda ke ako ina my love. Sai an jima" bai jira abinda zata ce ba yakashe wayar yanaji kamar yayi kuka. Rungume pillow yayi yana kallon side lamp din gadonsa yana tunani har bacci ya ɗaukeshi. Ta jima da wayar ahannunta kafin ta mike ta fice aɗakin ko ɗar batajiba da maganganun daya faɗa mata. Ita in anata ne ma daga yau karya ƙara kiranta. Washe gari sunan Aadil aranan su Abby suka daura auren Ameera da Amin batareda wani taro sosai ba. Daga Limami sai Abby sai abokin Abby wadda shine yayiwa Amin waliyyi Abby Kuma yayiwa Ameera. Ko Abba ba'a faɗa masa ba gudun karya bijiro da wani kabli da ba'adi. Kuma anyi auren asirrance ne saboda anunawa Goggo aida aurensu suka haifi Aadil ba shege bane shi ɗin. Agurguje Please. Yau satinta ɗaya da dawowa gida, kuma tun ranan daya kirata sukayi magana bai ƙara nemanta ba. Itace kullum amanne da jariri tana goye dashi ko kuma tayita yawo tsakar gida dashi tanayi masa wasa. Cikin satin har ta murmure kamar ba itace tayi rama ba. Su Sultan da Amin suna jin nauyin yiwa iyayensu magana ne, amma tabbas sun gane cewa akwai wani abu tsakanin Aneesa da ƴaƴansu, it's so unusual na MJ ya maida matarsa wurin iyayensa dan kawai zai yi tafiya, lokacin dasuke tareda Neehal ko tafiyan sati ɗaya zaiyi seya tafi da ita balle kuma a ƙaryarsa da basu sani ba wai tafiyan wata ɗaya. Raihanah da Mustapha ma kimin bin kwakkwafinsu da son shigewa Aneesa sun kasa gano komai. Innnati tayi tayi da ita ta faɗa mata menene damuwar amma taƙi. Haka duk sukayi shiru suka zuba mata ido. Intayi tsami zasuji Port Harcout. Yana kwance akan gadonsa dagashi sai shorts ya kwanta arigingine yana kallon saman ceiling ɗin dakinsa. Aneesa ce ta faɗo masa, Allah sarki yasan tuni Mujahid ya daɗe da ratsa duniyar ta,kenan yanzu ta zama tasa fid dunya wal Akhira. Yana cikin wannan tunanin yaji ringing din wayarsa, wani dogon tsaki yaja ya ɗauki wayar yana kallon baƙuwar number dake addabansa da kira kowani daren Allah yau sati ɗaya kenan. Kuma ba'a tashi kiransa sai war haka alokacin dayake tsaka da tunanin masoyiyarsa, kuma bai taɓa ɗagawa ba. Yau wani abu azuciyarsa yace masa "Isma'il kawai ka ɗauka, bakasan ko wani Alkhairi ne ke binka ba" wayar ya katse mutumin dake kiransa bai daddara ba aka ƙara kira. Ɗagawa yayi ya ƙara akunne, yanajin yadda ta sauki wani wawan ajiyar zuciya cikin angelic voice ɗinta tace "Assalamu Alaikum Ya Isma'il" damm yaji azuciyarsa, ya akayi wannan mai lambar tasan yadda masoyiyarta ke kiransa, saida ya ƙara duba wayar da kyau ya tabbata ba numbern Aneesa bane. Maida wayar kunnina yayi ya juya ɗayan gefen gadonsa ya kwanta da kyau yace "Wa'alaikis Salam. Pls who's on the line"? Habiba on the other side ta kwanta ta rungume teddy dinta aƙirji har wani lumshe ido takeyi cikin shagwaba wadda ita kanta batasan tayi ba tace "Ya Isma'il shine na jera sati ɗaya ina kiranka amma kaƙi ka ɗaga ko? Uhmmm uhmmm" ikon Allah, sai yanzu ma ya tuna cewa yabawa wata lambarsa, kai gsky amma yarinyar nan akwai kaifin basira, da sauri da ya faɗa mata numbern saboda kar ta ma kama har ta kirashi ashe dai da bai tsira ba. Cikin sigar tuhuma yace "ya akayi kika san sunana" murmushi tayi, muryarsa kaɗai is so mesmerising, ahankali tace"a name tag din dake makale a saman kakinka. I chose to call you Yaya saboda nadan ka girmemun nesa ba kusa ba, You deserve that much of respect from me" girgiza kai Isma'il yayi in affirmation, she's kinda smart. Bai wani so yaja conversation din yayi nisa shiyasa kawai yace ok, daga haka bai sake magana ba. Itama kuma ta rasa mezata ce masa tunda kusan maganan gaba ɗaya itakeyinta. Da dai taga haifa niyyar cewa komai kawai tayi masa sallama sannan ta kashe wayar. Ta fuskanci cewa shi ba mutum bane mai yawan magana, dan haka duk yadda zata yi ta shige masa sai tayi hakan, dan wannan catch din dis special bazata bari Black American ɗinnan ya kuɓuce mata ba, koda kuwa yanada mata (balle ma baida shi). Shi kuwa Isma'il yanata mamakin irin ƙwarin kai na Habiba, yanzu dama mata suna iya kiran mazajen da basu sani ba da daddarennan. Lallai kuwa, girman Turai yayi tasiri akanta sosai da alama. Allah ya kyauta. To mene ma nata na kiransa, me take buqata a wurinsa barda wani shagwaɓarta, lallai kuwa . Abuja Fitowarsa kenan daga wani meeting da Vice President akan wasu kuɗaɗe da ake tunanin anyi safararsu izuwa Niger ta hanya mara kyau kuma dasa hannun wani Babba ne. Jacket din suit dinsa ya rataya a shoulder ɗinsa because he's so exhausted. Yana shiga office ɗinsa ya zauna akan sofa ya jingina kansa da jikin cushion ɗin, yau sati ɗaya tunda yayi magana da ita har yau bai ƙara jin muryarta ba. Yayi haka ne saboda yaga ko zata nemeshi da kanta amma shiru, kenan dai ta tabbata yarinyar nan bata jinsa aranta ko kaɗan. Ajiyar zuciya ya sauke,ya maida idanunsa ya lumshe. Ga wani yunwar dake addabarsa kamar me, kullum cikin shan Black coffee yake da biscuit. Babu wani abun da ke masa daɗi, Allah kaɗai yasan wani irin so yakewa wannan baiwar Allahn,🥹. Yasan tabbas idan gida sukasan cewa akwai matsala tsakaninsu to za'a ɗauki tsatssauran mataki, hala ma ace ya saketa kawai tunda na sonshi take ba. Addu'a yake Allah yasa ma yanzu haka tanada ciki saboda koda maganar ta taso cikin ya kashe shi. Shi yasa ma yaƙi tafiya da ita, yasan dole za'a fuskanci wani abu tsakaninsu so Gara kawai ya zauna yayita rarrashin kansa har lokacin dataji tanasonsa kuma tana da niyyar zama dashi. Amin fa ya zaƙe, kullum zarya yake a hanyar part din Mamy, idan yazo kuma ahanashi ganin amaryarsa, badan komai sukayi hakan ba saidan gyarata dasuke ƙara yi. Ga Aadil da ya ƙara wayo kamar ba bakwaini ba. Duk wani hidimarsa ta koma hannun Aneesa, yaron tun kafin ya kai arba'in har ya gane hannunta, idan yasha nono awurin mamansa, zai fara ƙananan rikici tana ɗaukansa zai yi shiru, abun har mamaki yake bawa mutane. Sai kace yasan akwai alaka tsakaninsu. Itako idan ba'a anyi maganar MJ ba, mancewa take da wai tanada miji. Tsakani da Allah komai sake tattare dashi tayi gafe ne dashi ta watsar. Yau weekend duk suna gida babu inda suka tafi. Wuraren ƙarfe sha ɗaya ɗaya daga cikin sojojin ya shigo ya sanar dasu cewa sunada baƙo. Da sauri suka kimtsa kansu, Aneesa da Ameera suka wuce ɗakin Innati. Inda Goggo ta haƙimce saman sofa kamar kullum, jarababbiyar tsohuwar har wani jiki ta haɗa tayi fresh. Hijabi Innati ta sanya ta zauna suna hira jefa jefa da Hajja inda Goggo ta zuba musu ido kawai. Sallama sukaji abakin kofa gaba dayansu hankalinsu yakoma can, Abba ne tsaye abakin Kofar yasha wankan babban riga irinna talakoki mai sauƙin kudi. Sai washe baki yake, murmushin yaƙe Hajja tayi tace "a'a mutan Adamawa, sannu da zuwa ƙaraso mana" Goggo kuwa kamar zata yi bindiga, Meya kawo Abba gidan kuma, badai yazo tafiya da ita bane. Cab ɗin jan jan , tana ganin kuɗi da jin daɗi shine zata yarda tabishi. Shiko Abba hankalinsa nakan Innati wadda tun shigowarsu ta haɗa hirar sama dana ƙasa ko annuri babu afuskarta. Ƙarasowa yayi ya zauna, ya gaida Hajja ya juya wurin Goggo tace "sannu da hutu Goggo ta, kinata shan na Kano gashi har wani jiki kika ƙara" harara Goggo ta zabga masa tamaida kanta tv tana kallo, girgiza kai Hajja tayi, ba uwan ba da ɗan ba. Masu aiki ne tasa sukawomasa abin motsa baki. Ko kunya babu haka ya baje Babban rigarsa yana kwasan girki, kai kace agidansa yake. Saida yaji yayi ƙat sannan ya ɗago ya kalli Innati yace "sannu Hussaina, ina ƴan matanki. Ameera, na nima ban ganta ba" adaidai lokacin kuwa Ameera ta sauko da Aadil goye abayanta saboda Aneesa ta shiga wanka shi kuma sai rikici yake. Riƙe haɓa Abba yayi yana kallon ta, yaushe akayi aihuwa a gidan bai sani ba, kuma lokacin bikin Aneesa baimaganta da ciki ba balle ace, sai kuma ya tuna ai tunda yaganta da wani xabgegen hijabi taketa yawo. Tunda ta hango mahaifinta taji ƙirjinta yayi waji wawan bugu, amma data tuna cewa yanzu tana aure da uban ɗan ne, ko mai zai faɗa ya faɗa. Ƙarasowa tayi ta rusuna ta gaida shi, still bakinsa yakasa rufuwa gana kallon kyakkyawan jaririn dake bayanta shige sak yana Kamada Amin dan ya shaida fuskar Amin sosai. Goggo ce ta katse shirun ta hanyar faɗin "Zaidu kaga jikanka, bakasan ƴarka ta aihu ba"? Da sauri Abba ya juyo kansa kamar zai ɓallata yace "mene, yaron Ameera fa kikace. Yaushe tayi aure shine har zata aihu ban sani ba"? Tsoro ya bayyana afuskar Ameera ƙarara, Hajja ce tayi saurin saka baki amaganan tace "kai bakasan abinda yasamu ƴar taka bane kafin mahaifiyarta ta bar gidanka? To wannan ɗan shine sakamakon abinda ya faru" kasa cewa komai Abba yayi, kan Uba. Yaran zamani, daga fyaɗe so ɗaya shine har tayi ciki? Ikon Allah. To ai baida abun cewa tunda yasan ya akayi hakan yafaru. Shashe maganar yayi tunda ba abinda yakawoshi ba kenan. Allah ya kyauta. Kallon Hajja yayi ya ɗan sosa ƙeya yace "Hajiya, dama nazone saboda na maida iyalina gida da kuma mahaifiyata. Shine nace ko zan haɗu da Jenar muyi magana dashi" hankalin Innati nakan TV ne, amma tunda taji maganganun Abba batasan lokacin data juya ta zuba masa uwar harara tanaji ranta na ƙuna. Tabbas ko sama da ƙasa zasu haɗe ne babu abinda zaisa takoma gidan Zaidu saidai gawarta. Murmushi mai Kamada tsiya Hajja tayi tace masa "Allah sarki, ai bansan haka abun yake ba amma Nadeen kam tuni tanada wani a ƙasa yanzu haka. Ai bamuji daga gare ka ba harta ƙarasa iddarta dan haka kuwa kaga babu aure tsakaninku" Abba bai san lokacin daya mike ya zuba wata uwar ashar yace "da aurena akan Hussaina, wlh akwai aurena akanta shine zata bawa wani dama ..." Bai ƙarasa ba kuwa itama Hajja ta harzuƙa tamike dama wannan ranan take jira kuma gashi Allah ya kawo shi, aharzuke tace "karka raina mana wayo mana, kai bakasan abinda ake cewa kunya ba? Ina kallon mahaifiyarka tazo ta zaune mun agida tanayin duk abinda taga dama, bance mata komai ba saboda kawaicina duk da kuwa abinda tayiwa ƴata. Shine kaima kazo dan bakada ta ido zaka wani ce akwai aurenka akanta. To nabi auren da gudu ba patari, aikin banza kawai. Duk rashin ilimin ka na addini Yakamata ace kasan idan mace ta gama idda baka nemeta ba to sai ka biya sabon sadaki hakan kuma zai kasance ne kawai idan ita tana ra'ayinka" bakin Abba da Goggo ya mace babu bakin magana. Rarrafawa yafarayi da guiwa kamar ƙaramin yaro har wurin innati ya haɗa hannunsa wuri ɗaya yace "dan Allah ɗan girmansa Hussaina badon halina ba kiyi haquri ki dawo gidana. Wlh nayi nadama akan abinda nayi miki" murmushi Innati tayi tace "ashe dai in Kanada rai baka gama kallo ba, ai kuwa Zaidu nida kai har abada saidai gawana " wannan amsar ya girgiza duniyar Goggo, idanfa auren Abba da Innati ya mutu, kenan dole ta koma gida Adamawa, kai habawa. Cikeda fushi Hajja ta kira sojoji daga waje akan su zo suyi waje da Abba da Goggo, dama tana neman chance ne dazata kore ta daga gidan duk wannan isa da batsewa datake. Aikuwa sojojin suna shigowa basuyi wata wata ba suka sungumi Goggo ahannu basu direta akoina ba sai wajen gate ɗin Mansion ɗin, Abba kuma akayi masa koran ƙare yanata zage zage cewa suyi hattara, akwai aurensa akan Innati shidai ya mayar da ita. Raihanah da Aneesa suna hira aɗaki Ameera ta shigo da gudu tana zuba musu labarin abinda ya faru, suko mezasuyi idan ba dariya ba. Finally Allah ya kawo ƙarshen zaman Goggo a gidan. Raihanah ce ta jefowa Aneesa tambaya wadda yasaood ɗinta canzawa atake, cewa tayi"Amaryan Ya MJ, ke kam rabonki da wayada mijinki tun yaushe. Yayi tafiya amma irin zakaɗin kirannan danaga amarya da ango sunayi kekam banga kinayi ba"? Bata iya cewa komai ba, kawai ta kwanta ta juya musu baya. Tabbas Raihanah da Ameera yanzu kam sun gane cewa akwai babban matsala tsakanin Aneesa da MJ. Itakuwa, abinda yafaru tsakaninsu shine ya faɗo mata, faɗuwar gaba ne ya ziyarceta, meyasa kullum ake damunta da tambaya akan mutumin da taki jininsa haba mana. Tsaki yaja ta gyara kwanciya, tanaji Raihanah da Ameera suna jifanta da maganganu amma tayi ƙyam kamar bacci takeyi. Fast forward ⏩ Yau ta cika wata ɗaya cif a gidan. Abby ya dawo daga tafiya ya ganta a gidan, yayi mamaki, ɗaya yiwa Hajja magana sai tace ai MJ yayi tafiya nan da ƴan kwanaki ma tana sa ran zai dawo. Abby bai iya cewa komai ba kawai ya share maganan, to me zai ce, ai Hajja ce ta goya masa baya, so duk abinda zai faɗa yanzu saidai taga laifinsa amma bana MJ ba. Ya shirya cikin ƙananan kaya, Black jeans da white T-shirt sai pcap black color ga wani dakakkiyar Snickers dayasa white colour na Nike. Ƙaramar trolley ne ahannunsa, ya ƙara haske dashi, amma ya zabge sosai ba wasa, idanunsa sun fito da kyau ga hanci kamar zai faɗo. Daddaɗan ƙamshi yake fitarwa mai sanyi, dark shade spec ya sanya yana fitowa guards ɗinsa suka karɓi jakan zuwa mota. Minti ashirin ya kaisu airport daga inda gidansa yake. Ba bata lokaci jirginzu ya ɗaga zuwa sararin samaniya. Ƙarfe huɗun rana suka iso Kano saboda jirgin rana suka bi. Motocinsa dake waje suka jera kansu yana fitowa aka buɗe masa ya shiga sai MAINOMA Mansion. Tun Ya Isma'il baya kula Habiba, amma there's something special about the girl. Duk yadda yakeso ya avoiding dinta kamar wani charm tayi amfani dashi wurin jawo hankalinsa gare ta. Sai gashi shida yayi kusan sati nawa baya dariya, idan suka zauna tafara bashi labari zai ta dariya yana tafa hannu. Before you know, har tayi nasaran jawo hankalinsa gare ta. Idan bata kirashi ba shine zai fara kiranta. Har Mum ɗinta da Commander sun sheda hakan. Kullum Ya Isma'il idan babu aiki sosai gidan yake wuni suyita hira shida mutuniyarsa. Yau shida Habiba suka shirya zuwa Kano, zai zo ya nuna musu agida cewa yasamu mata ya haqura da Aneesa tunda yayansa yayi masa overtaking. Ƙarfe huɗu suma suka diro cikin garin Kano. Habiba baki ya kasa rufuwa, yau za'a haɗu da inlaws. Motocinsu ya faka agaban gate sukayi horn aka buɗe musu gate suka shiga. Bakinta ya kasa rufuwa ganin wannan uban gidan kamar ba'a Nigeria ba. Duk kuɗin babanta, wannan kam yaci ubansa. Suna zaune afalo suka dinga jin dirowan motoci suna shiga gidan. Mamy tasa Raihanah take ta duba su wanene. Aneesa ma zaune aƙasan ƙafarta tana turara mata gashi. Da gudu Raihanah tadawo tana cewa " Mamy lwh Ya MJ nesa Ya Isma'il suka dawo, basu fito ba amma motocinsu ne suka jera kansu awaje" wuffff gaban ta ya faɗi, Ya Isma'il ya dawo? Kuma da MJ innalillahi wa inna ilaihi raji'uun. Mamy tace "Isma'il yadawo, Alhamdulillah, shine zasu diro babu ko sanarwa". Da sauri ta ɗau ɗankwalinta ta ɗora saman kai suka miƙe gaba ɗaya sukayi ƙofan falon. Fitowarsa kenan daga motar, mamaki yakamashi ganin Isma'il shima ya fito, ga wata budurwa agefensa suna takoma inda yake tsaye. Har suka ƙaraso yana kallon ɗan uwannasa, addu'ar sa kawai Allah yasa ya daina fushi dashi, ga mamakinsa suna ƙarasowa Isma'il ya rungumashi, murmushi yayi shima ya zagaya hannunsa abayansa suka rungume juna, Habiba ta rusuna har ƙasa tana gaidashi, Isma'il ya introducing ɗinta as his wife to be. Murjushi MJ yayi kawai ya kamo hannunsa suna tafiya, Habiba kuma tana bayansu. Fitowa su Mamy sukayi suka tsaya a bakin entrance, idanunsa ne ya sauka akanta, tana tsaye ta kama ɗankwalinta da hannu biyu tana kallonsu Isma'il da baquwarsa. Sosai taji wani abu ya daki zuciyarta, wacece wannan Ya Isma'il ya zo da ita. Raihanah da gudu ta wuce wurin yayyinta ta rungume MJ tana washe baki. Isma'il ya ƙaraso wurinsu Mamy ya kalli Aneesa na abinda baifi sakan uku ba yajada fuskarsa ya maida wurin Mamy, Habiba ta rungume Mamy tana gaida ita. Kamar tasa hannu tajawota zuwa ƙasa haka Aneesa taji. Yanzu dama soyayyar da Ya Isma'il yake mata duk wasa ne, gashinan yaushe yaushe har ya samo wata🥹 Tana tunani batasan lokacin da MJ ya ƙaraso wurinsu na itada Mamy, da gudu Aneesa takoma ciki tanaji kamr kuka zatayi. Da mamaki duk suka juyo suna kallon ta, Mamy ta girgiza kai, yasan ba komai yana hakan ba sai ganin Habiba datayi tareda Isma'il. To ya zatayi, ai aikin gama yariga ya gama. Mood ɗin MJ ya canza, yanzu duk wannan satittikan daya bata har yanzu batajin komai akansa? Gashi nan ta nuna kirikiri cewa son Isma'il na nan a zuciyarta. Itako Raihanah taji daɗin ganin Habiba, ko babu komai yasan yanzu Ya Isma'il yayi mata nisa dolene ta haqura ta koma wurin MJ. Amma inba Aneesa ba, tsakani da Allah babu wadda zai kalli MJ yajuya Kai yace sai Isma'il idan ba itaba. Tasamu ma yana so ta shiyasa yake lallaɓata. Tare suka shigo ciki, Mamy ta haura sama zuwa ɗakinta. Anan ta tadda Aneesa kwance akan gado ta kifa kanta tana kuka, amma jin an buɗe ƙofa yasa tayi shiru tana sauke ajiyar zuciya. Ƙarasowa Mamy tayi ta zauna kusada ita takira sunanta. Miƙewa tayi tana share hawayen fuskarta ta kalli Mamy, " haba takwarar Hajja, wannan kukan na menene. Nifa ina matsayin uwa ce agareki ba suruka ba. Matsayi ɗaya na ɗaukeki da su Raihanah, tun ba yau ba na riga na fuskanci akwai abinda ke tsakaninku da Mujahid. Meyasa mukeso ku ɗorawa kanku abinda Allah bai ɗora muku ba. Kuyiwa kanku faɗa ku riƙe juna tunda Allah yariga ya haɗaku. Haba. Yanzu ke kukan dakikeyi name, indai akan Isma'il ne to da dai kinsawa kanki ruwan sanyi. Shi dama namiji wuyan abun shine ku rabu, kuna rabuwa wlh koda safe ne kibashi nan da zuwa yamma zai samo wata. Ki yi haquri kisawa kanki ruwan sanyi. Ina baki shawara ku riƙe mijinki da amana. Da ina fushi da Mujahid, amma yanzu duk na yafe musu, su ɗin nawane babu yadda na iya dasu. Mujahid yana sonki, Ni na tabbatar miki da haka. Karki bari son Isma'il ya yaudareki har ya sa kibari Mujahid ya rabu dake, zakiyi two zero idan haka ya faru, danshi Isma'il kobai samu wata ba, ba lallai ya aureki ba tunda ɗan uwansa ya rigaki saninki. Kiyi haquri kinji"? Hawaye na gangarowa a idanunta ta gyaɗa kai. Murmushi Mamy tayi ta shafa kanta sannan tace "taso ki kimtsa kanki kizo muje mu shiga kitchen a ɗora abinci a wuta kinji" fitowa Mamy tayi ta barta tana tunani, tabbas babu ƙarya cikin maganan Mamy. Azamaninnan wacce suruka ce zata zaunar dakai tayi maka magana heart to heart haka. Saukowa tayi daga gadon ta gyara fuskarta sannan tafito. A kitchen tasamu su Mamy sunata aiki itaba Raihanah da sauran masu aiki. Sa masu hannu tayi sunayi suna hira, hadadden abinci akayi. Mamy ce ta girka pounded yam da miyan egusi dayasha nama,kifi, da kayan ciki, sai tayi coconut fried rice. Aneesa kuma tayi meatpie da tortila wraps sai strawberry smoothie. Masu aiki kuma suka karasa sauran. A babban dinning hall ɗin gidan gaba ɗaya za'ayi dinning dan haka masu aiki suka dinga jera abinci suna fitarwa a tray zuwa hall din. Bayan Sallan maghrib ta fito daga part ɗin Mamy zataje tayi wanka a apart ɗin Hajja. Tana sallama tasamu babu kowa afalon sai ƙaran Ac dake tashi. Da sauri ta haura sama taje ta watsa ruwa ta fito. Ana Sallahn isha'i dan haka ta tada Sallah tafara. Bayan ta idar ta shirya cikin kayan bacci wando da riga mai dogon hannu irin mai tsantsin nanne yadin kayan. Feshe jikinta tayi da turare ta ɗora hijabi akai tafito. Alokacin data shigo dinning hall ɗin kowa ya riga ya hallara kusan ita kaɗai ake sai MJ da babu shi awurin. Kallon Habiba tayi wadda ta zauna kusada Ya Isma'il sai washe mata haqora take, ko sakan uku batayi da kallonta ba taja da ido. Kujeru biyu kawai suka rage, dan haka taja ɗaya ta zauna. Takun mutum sukaji abayansu gaba ɗaya suka juya suna kallonshi, normal shirin daya sabayi ne, wando three quarter sai rigansa armless wadda ya fidda damatsensa da kyau. Farar fatarsa sai wani glowing take under the light, kujeran dake kusada Aneesa yaja ya zauna. Tunda ƙamshin turarensa ya bugi hancinta ta rasa duk wani sukuni nata. Turarensa is God damn so Good. Ta ƙame wuri ɗaya ta kasa motsi. Kallonsu Isma'il yayi yaɗanyi murmushi, yanzu da shi da ita kenan. Kawar da tunanin yayi a zuciyarsa ya maida kansa kan kulolin dake gabansu. Raihanah da Aneesa da Ameera sune suka miƙe suka fara serving MJ mutanin wurin. Plate dake gaban MJ ta ɗauka tana so ta tambayeshi mezaici amma ta kasa, tana rikeda plate ahannu ta zubawa kula ido. Murmushi Ammi tayi tace "takwarar Hajja, zuba masa fried rice din da coleslaw, shiyafi so" ɗago Kai MJ yayi ya kalleta, au dama magana takeso tayi amma takasa, to meyasa, kunyarsa takeji ko menene. Serving ɗinsa tayi ta aje gabansa, ganin ta ɗauki wani plate zata debi abinci yayi saurin kama hannunta yace wace " leave it, zauna muci wannan tare yayi mun yawa" kowa ya juya yana kallonshi, ko ya mance akwai mutane a nan ne. Itakuwa tasha jinin jikinta, jarpa ai saidai tafasa cin abincinnan. Ina ita ina sharing plate dashi agaban iyaye da yayyi. Bai ƙara ce mata komai ba ya maida kansa plate ɗin, wani spoon daban ya ɗauka yasa a cikin plate ɗin gabannasa yakama hannunta ta zauna tana wiƙi wiƙi da ido. Kowa ya gama cin abinci amma Aneesa ta kasa yin koda spoon ɗaya ne, ganin haka yasa MJ tashiwa ya ƙara abincin dake plate ɗin tunda ya fara ci. Saida ya serving komai a karamar tray sannan yacewa iyayensa " Hajja nagaji, zamu tafi ɗaki acan zataci abincin saimu kwanta" dammmmm ƙirjinta ya buga. Babu wadda ya hanashi, saima sallama dasukayi musu. Hannunsa ɗaya na riƙeda tray ɗayan hannun kuma ya kamo hannunta suka wuce upstairs zuwa ɗakinsa. Aneesa jitake kamar ta fashe da kuka. Suna shiga falon ta ƙwace hannunta hawaye na taruwa a idanunta. Gaba tayi tabarshi a tsaye da plate ahannunsa. Zama tayi saman cushion tana turo baki. Murmushi yayi ya ƙaraso gabanta ya aje abincin saman center table ya juya wurinta ya kamo hannunta yace " Sweetheart fushi har yanzu"? Juya kai gefe tayi tana ƙara turo bakin gaba. Kiss ya manna mata ahannu , da sauri ta ƙwace hannunta saboda wani yarrrr dataji ajikinta. Hijab ɗinta yaja ya cire, gashin kanta yabiyo hijabin ya rufe mata fuska. Ƙamshin da gashin ya fitar shine yasashi lumshe idonsa. Hannu yasa ya kwashe gashin ya maida shi gefen fuskarta yace "babyna, dan Allah kici abinci ko hankalina zai kwanta. Plssss" for the first time, takasa yi masa musu. Abincin ya ɗauka ya sa akan cinyarsa ta sauko ƙasa suna facing juna. A hankali yake ɗibawa yakai bakinta, kamar bazata buɗe ba amma ta fara budewa yana sa mata. Duk yau yayi mata wani kwarjini takasa haɗa ido dashi. Ba laifi taci abincin sosai tasha juice. Sauran data bari ya ƙarasa ya shanye smoothie ɗin da snacks gaba ɗaya. Tattara plates din yayi yakai kitchen aƙasa, lokacin su Mamy suna falo suna hira. Wuce su yayi ya koma ɗaki. Yayi mamakin ganin har ta fara bacci akan carpet. Hannu yasa yaɗagata cak zuwa ɗaki. Kwantar da ita yayi ya gyara mata kwanciya. Toilet ya shiga yayi alwala ya fito yayi Sallan witr yaɗan karanta Qur'an sannan ya miƙe zuwa gado. Kwanciya yayi ya karanta addu'a ya shafa mata ajikinta shima yashafa anasa. Jawota yayi jikinsa, itakuwa shatu gyara kwanciya tayi kan ƙirjinsa ta zagaya hannu ta cikinsa ta ɗora ƙafa akan cinyoyinsa tacigaba dajan burki tana ajewa. Daɗi kamar ya kashe MJ, yau zai yi baccin daya daɗe baiyi irinsa ba. 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 REEMAH ✍️ PG 91_95 Not edited ❌ Bacci mai daɗi suke yi su biyun yadda suka kanainaye junansu kamar wani zai ƙwace ɗaya ahannun ɗaya. Gashin Aneesa duk ya barbaje ya rufe wa MJ fuska. Wayarsa dake kan side drawer ne yafara ƙara alarm din ƙarfe biyar yafara bugawa. Itace tafara farkawa tana ƙyat ƙyat da ido. Jin kanta tayi asaman wani abu mai laushi ga fadi, ahankali ta gyara sumanta ta kalli fuskarsa wadda har yanzu bacci yake cikin sukuni. Ji tayi kamar karta tashi saboda daddaɗan perf dinsa ga kuma kirjinnasa da laushi. Tana jin ya fara motsin farkawa tayi saurin rufe idanunta tanajin wani iri, wai mutuminnan shi bai da zuciya ne? Yanzu duk irin wulaƙancin data dinga shimfida masa shine baiyi zuciya ba, gata kane kane saman kirjinsa. Buɗe idonsa yayi ya zuba matasu yana ƙarewa beautiful face ɗinta kallo, she looks so innocent while sleeping, amma idan ta farka to sunanta ƙaramar lioness. Hannu yasa ya kashe alarm din, sannan ahankali yafara shafa bayanta yana matsewa da ƙirjinsa, jin tayi ajiyar zuciya yasashi gane cewa ba bacci take yi ba. Bakinsa yakai daidai kunninta ya hura mata iska ahankali yace "i know you're awake" ƙara runtse idonta tayi da kyau, murmushi yayi mai sauti ya manna mata kiss a forehead dinta yace "get up, lokacin Sallah yayi" ahankali ta buɗe idonta ta zuba masa, wani yarrrr haka yaji, idanun look so sexy dasuka ƙanƙance kamar tana jin bacci. Tashi tayi tana miƙa, ido ya zubawa boobs ɗinta yadda sukayi wani sama suna pointing gabas, har ta sauke hannunta bai cire idonsa ba, kallonshi tayi taga abinda yake kallo da sauri ta ɓankare kirjinta baya tana turo baki kamar yadda ta saba. Murmushi yayi ya sauko daga kan gadon, miƙa mata hannu yayi ba musu ta sa hannunta cikin nashi, saukar da ita yayi tasa bedroom slippers dinta suka wuce toilet, tana gaba Yana binta abaya har suka shiga. Sabon brush guda biyu ya ciro a drawer yasa musu toothpaste ya miƙa mata, tsayawa tayi agaban makeken mirron toilet ɗin tana sa ruwa a brush din ta, shi kuwa abayanta ya tsaya shima yasa ruwan. Ɗagowa tayi suka haɗa ido da sauri ta sauke tana mamakin kanta, lallai fadan Mamy yayi tasiri akanta, ita bama tayi tunanin zata sauko ƙasa da wuri haka ba, sai kuma ta tuna da wannan mai fuska kamar ɗanyen tumatur (Habiba) guntun tsaki taja, tacigaba da goge bakinta. Hannu yasa guda ɗaya ya sakalo ta cikinta ya kara hada bayanta da gabansa da kyau, yadda take girgiza datakeyin brush ɗin ba ƙaramin daɗin abun yakeji ba. ALLAH kaɗai yasan daɗin dayake ciki da loml dinsa ta sauko ta daina fushi dashi. Yanzu iya abinda yarage masa shine ta furta masa " I LOVE YOU" da kuwa babu mai kaisa jin dadi. Tare suka gama brush ɗin sukayi alwala sannan yasata agaba suka fito. Sallaya ya shimfida ne musu ya tada Sallan raka'atanil fajr sukayi tare. Bayan sun idar kuma ya jasu Sallan asuba. Suna idarwa suka zauna yin azkhar tare, har musaffa sukayi na Qur'an, inda shi idan ya karanta sofha ɗaya itama saita karanta ɗaya, inda akwai gyara kuma saiya gyara mata. Suna idarwa yaga ta miƙe ta cire hijabi zata fita. Da sauri ya kamo hannunta yace "ina zuwa kuma" batareda ta kalleshi ba tace "zamu fara aikin breakfast ne" ɗaukanta yayi cak yayi hanyar gado da ita yace "ni dai a'a, ai sun san mijinki ya dawo Kuma yana buqatar hutu" direta yayi saman gadon shima ya biyota. Kashe wutan ɗakin yayi gaba ɗaya lokacin gari har yaɗan fara haske, blanket ya jawo musu ya rufe musu jiki, yadda ya ƙanƙameta saikaci za'a saceta. Hannunsa male male saman boobs dinta yana yamutsawa ahaka har bacci ya ɗaukesu. Shiru shiru har ƙarfe takwas kowa ya hallara a dinning za'ayi breakfast amma su MJ shiru. Har sun fara cin abinci Hajja tace "yau naga ikon Allah, ai wani abun ana bari kodan kunya, Mujahid ya gama lalata mun ɗiya. Har ƙarfe takwas uban me ake yi aɗaki basu fito ba. Kai jama'a, Allah ya shirya yaran zamani" babu wadda ya tanka mata, Abby ya girgiza kai kawai, Hajja dai batada dama, ko gaban waye sai ta zuba magana iya son ranta. Su Raihanah da Mustapha suka kalli juna suka yi murmushi suna ayyana abubuwa aransu musamman Raihanah. Amin kuwa sai faman tokare ƙafan Ameera yake ta ƙarkashin dinning Kuma tas a idon Ammi, fork dake hannunta ta ƙwala masa aƙeya, har saida ya sosa yana sakin ƙara. Murmushi Ameera tayi tacigaba da cin abinci ta. Aadil na can hannun Habiba ta rikeshi itama tana cin abinci, inka ganta sai ka rantse ƴar gidan ce. Ta saba da su cikin wuni ɗaya, dake babanta abokin Abby ne sai shima ya dauki abun as normal. Isma'il kuwa, duk yadda yaso ya fidda abun aransa yakasa, gashi dai yanzu yanason Habiba amma yakasa cire Aneesa azuciyarsa, ko jiya daya ganta saida yaji wani ɗar azuciyarsa, ta ƙara kyau da haske, annurin aure tas akan ajikinta ya bayyana. Kawar da tunanin yayi yacigaba da tsakar chips ɗinsa. Sai ƙarfe tara suka farka, shiya fara yin wanka sannan itama ta shiga. Dake babu kayanta aɗakin saita maida na jikinta kawai ta fito kitchen dan nema musu abinda zasuci. Karo taci da mutum daidai zata shiga kitchen, Isma'il ne riƙeda kofi ahannunsa, kallonta yayi itama tana kallonsa kawai tayi ta kawar dakai gefe, ta gefensa ta wuce ta shiga kitchen ɗin, sharp sharp ta dafa ruwan shayi ta zuba a flask sannan ta yi mayo egg sandwich ta ɗora saman tray ta fito. Har ta haura bata hadu da kowa ba. Da sallama abakinta ta shiga, zaune tasameshi yana aiki a system ɗinsa, aje trayn tayi saman center table. Aje system ɗinsa yayi ya sauko ƙasa ya tanƙwashe kafafu yasa itama ta zauna kamar jiya suna facing junansu. Sandwich ɗin ya serving a plate, ya haɗa tea a glass cup ɗaya. Shida kansa yake bata, intaci shima saiya ci gwanin sha'awa. Yau kam ta cire kunya ta narki sandwich ɗin da kyau. Bayan sun gama ci kuma, shida kansa ya kwashe plate ɗin yasata agaba suka fito, ake plate ɗin yayi a kitchen duka wuce party ɗin Hajja. Anan suka samu anata hira, kusan kowa na falon. Habiba ce keta faman basu labarai suna kyakyatawa. Yau da sauƙi, Aneesa bata wani ɓata rai dataga Habiba ba. Saima zama dasukayi suna ta hira abunsu. Hajja ta kalli MJ tace " Babana, yaushe zaka koma gida da matarka. Banason yawan zuwa hutunnan dakake musamman yanzu dakakeda mata. Isma'il yace gobe zasu koma sai in andawo shirye shiryen aurensa, kai ma kawai ku tattara gobe kowa ya koma wurin aikinsa " Aneesa jitayi kamar ta nitse aƙasa, yanzu mutane da gidansu shine za'a na koransu wai sukoma can wata uwa duniya. Raihanah ta saci kallon MJ, sai taga kamar shi abun ma daɗi yayi masa, ta maida idonta kan Aneesa taga yadda ta haɗe giran sama da ƙasa. Haka sukaci gaba da hira har lokacin Sallan zuhr. Washe gari, Isma'il da Habiba suka shirya komawa Port Harcout, inda Mamy da Ammi suka yi mata sha tara na arziki. Sai ƙarfe tara suka kama hanya. Aneesa tana sane da MJ ya dinga haɗa kayansa, itakuwa ko akwatin ma bata fitar ba, har ya gama taga ya ɗau wayarsa yayi danne danne ya aje. Minti kaɗan sai aka kwankwasa kofar falonsa, budewa yayi saiga Raihanah da kayan Aneesa ahannu kamar zatayi gudun hijira. Tunda ta haɗa ido da Aneesa wadda ta cika tayi famm ai bata sake kallonta ba, karɓan kayan yayi ya rufo kofa. Miƙewa tayi ta fashe da kukan shagwaba harda bubbuga kafa aƙasa. Murmushi yayi ko kulata baiyi ba saida ya gama haɗa kayan tas cikin wani akwati, sannan ya juyo zuwa gare ta, har yanzu kukan takeyi da hawaye caba caba. Abun har ya bashi tsoro, ba dai har yanzu tana kan bakanta bane na cewa saidai ya rabu da ita. Takowa yayi inda take ya jawota jikinsa ya runguma da kyau, lamo tayi tana kan kukan ahankali. Shafa gashinta yayi yace " bakiso ki tafine "? Girgiza kai tayi tana ajiyar zuciya tace " Ni dai kawai kawai kasa aƙwaso maka kayana. Kuma harda bra ɗina aciki fa" saikuma ta ƙara fashewa da kuka, ikon Allah. Yanzu dama saboda bra ɗinta dake cikin kayan shine yasata kuka. Kamar zai yi dariya saiya riƙe karya jawowa kansa wani abun daban. Saida ya ɓata lokaci wurin rarrashinta sannan ta yi shiru tanata faman turo baki gaba. Shiryawa sukayi, tana ganin ya ɗauki turare zai fesa tayi saurin hanashi tana toshe hanci, da mamaki ya tambayeta Meya faru, sai cewa tayi "wlh wannan turarennaka warin kashi yake mun" mamaki yahanashi magana sai kawai uhmmmm yace ya aje turaren ya fasa sawa. Bayan sun kammala shiri suka fito saƙale da hannun juna. Afarfadan gida suka samu mutanin gida basu koma ciki ba dan su Isma'il basu daɗe da wucewa ba. Sallama sukayi dasu, amma kafin su tafi saida Aneesa tayi kuka Hajja da Ammi sukayi aikin rarrashi, Innati kuwa jitake kamar ta kwakkwaɗeta, yarinya sai son shagwaɓan tsiya yadda kasan itace last born. Aadil na hannun babansa yana ta faman zazzare ido yana tsotsan hannunsa, karɓansa Aneesa tayi tanaji inana abata shi Sutafi tare. Kamar yaron yagane, shima tunda ya shiga hannunta yaƙi komawa hannun babansa. Ameera ce ta karɓeshi tana rarrashinsa kafin yayi shiru. Batareda ɓata lokaci ba suka shiga mota sai airport, suna isowa minti kaɗan jirgin su ya ɗaga zuwa birnin tarayya. Wani babban gida Abby ya siyawa Amin acan Hotoro, anata gyare-gyare komai saida akasa sabo dal. Can gida kuma gyara Ameera take sha as per sabuwar Amarya, lefe kuwa tuni Mamy ta gama haɗawa dozen ɗaya. Aranan da Aadil ya cika arba'in aranan suka paka zuwa sabon gidansu. Gidane haɗadde ɗan dede four bedroom bungalow. Daren ranan Amin ya antayo da ledodi guda biyu. Sallan nafila sukayi tare suka ƙara godewa Allah, gasassun kaji ne irin gashi mai romo romonnan da exotic mai sanyi ya fitar yayi serving ɗinsu. Aadil da tuni yayi bacci bayan mamansa tayi masa wanka ta shiryashi cikin kayan baccinsa yana cradle. Aranan saida Amin ya kashe ranan garin Kano gaba ɗayansu bai bar ko ɗaya ba. ALLAH yasa babu mai gadi balle wani bayansu a gidan, zabga ihu yadingayi yana kiran sunan Mamy da Ammi kai harda sunan Aneesa saida ya kira, tunda yake sex da mata awake bai taɓa jin irin ƙololuwan daɗi irinna yau ba (bambancin haram da halal kenan), Ameera tasha wuya iya wuya amma haka ta daure dan ta faranta masa, shi da kansa yayi mata wanka suka tsarkake jikinsu sannan suka kwanta, Aadil kuwa tunda ya farka saboda ihun da ubansa keyi haka ya koma baccin wahala tunda yaga babu sarki sai Allah bayan ya gama shan kukansa. Su Isma'il suna komawa Port Harcout a satin su Abby suka tafi dashi da abokansa dan neman auren Habiba, ƴan gidan sunyi murna kaman me. Ansa biki nan da wata biyu, inda za'a haɗasu da Sultan da budurwarsa Ummu Sulaim. Habiba baki ya kasa rufuwa, tuni labari ya zaga ƙawayenta, sai faman nuna musu hoton angonnata takeyi sukuma suna ƙyasawa. Tunda suka dawo Abuja babu abinda ya taɓa shiga tsakaninsu na auratayya, saidai babu damuwa tana kula dashi yadda ya kamata. Amma abun mamakin shine, bai isa yasa turare taki ba, ko turaren wutan datake sawa aɗakinta da gidan gaba ɗaya ta daina sawa wai warin kashi yake mata. Aneesa takai point ɗin da idan tayi abinci saidai tafito can wurin ɗakin maigadi tazauna taci, cewa take bata iya cin abinci acikin gidanta yanayi mata wari zatayi amai. Abun harya fara damun MJ, wani irin hanci ne da ita, kowa hancinsa normal amma ita kamar ta aljannu ne da ita, komai mai ƙamshi tace ita wari yake yi mata. Gashi har yau kalmar nan ta "I LOVE YOU" takasa furta masa. Wani plan ya haɗa dan ya gwadata. Yau weekend Dan haka yana gida throughout. Tana zaune tana kallo ya shigo bayan ya dawo daga masallaci sallan azahar. Abakin ƙofa ya tsaya ya buɗe mata hannu alamar tazo, miƙewa tayi babu musu tafara takowa zuwa wurinsa, amma kafin ta kai sai jin mutum tayi aƙasa timmm ya faɗi babu alamar motsi atattare dashi. Ihu ta saki tana ƙwalawa sojojin gidan kira, da gudu suka shigo suna ganin Ogansu aƙasa sukayi saurin sungumeshi zuwa cushion. Ɗaya daga cikinsu ya kira doctor yayi masa bayani. Tana zaune tana kuka ta riƙe hannunsa kamar zata ɓallashi tana jijjigashi amma bai tashi ba. Doctor ya iso ya zauna kusada shi inda yajuwa Aneesa baya bata ganin fuskar MJ. A hankali MJ ya buɗe idanunsa ya kalli doctor ya kashe masa ido ɗaya, sojojinsa dake tsaye suna kallon wannan drama sukayi ƙoƙarin matse dariyansu, juyawa sukayi suka fita a falon yarage daga Aneesa sai Doctor da MJ. Juyowa doctor yayi ya kalli Aneesa yace "Madam, rabon da ki cewa mijinki i love you tun yaushe"? xaro ido waje tayi ta dafe ƙirji tace "i love you Kuma, Meya haɗa ciwonsa da i love you Doctor " ɗan ɓata rai doctor yayi yace "haba ai Dole ciwonsa ya tashi. Mutum nada ciwon hawan jini dayake buqatar ana ce masa i love you akai akai shine kika ƙyaleshi har tsawon lokacinnan baki ce masa ba"? 🙆 Hawaye na gangarowa a idanunta innocently ta matso kusada shi ta kamo hannunsa ahankali ta buɗe baki tace "Ya MJ katashi, wlh ina sonka sosai sosai. I love you, I love you I love you I love you " ta dinga maimaitawa kamar karatu, murmushi Doctor yayi, lallai ya yarda da wani malami yace mata wawaye ne, gashi da ƙarya kaɗan aka tono abinda ke zuciyarta. MJ kuwa Allah ne kawai yasoshi bai tonawa kansa asiri ba saboda daɗin daya mamayeshi. Kamar mai ciwon gaske a hankali ya fara motsi da hannunsa dake riƙe cikin nata, buɗe idonsa yayi ya ƙara lumshewa ya buɗe su tas akanta, rungumeshi tayi tana sakin kuka, da gudu doctor ya ɗau akwatin aikinsa yabar falon yana dariya. Shi kuwa MJ daɗi iya daɗi, hannu yasa ya zagaye bayanta yana bubbuga wa ahankali. Da ƙyar ya samu tayi shiru awurin har Bacci ya ɗauketa ahaka. Kwantar da ita yayi a ɗaki shima ya kwanta kusada ita ya jawota jikinsa shima yayi baccin. Tunda suka dawo gida Goggo take fushi da Abba. Gashi babu abinci agidan kina misƙala zarratin. Duk kuɗaɗen da Abby yabawa Abba tas ya cinye su a kayan marmari shida Goggo. Goggo duk sai tabi ta kwaɓe a sati guda, wannan jikin datayi lokacin tana gidan Innati duk ya zube tas, takoma yadda take ada. Abba kuwa babu aikin fari balle na baƙi, tabbas yanzu kam ya yarda cewa haqqin matarsa na bibiyansa. Ana nan ana nan wani rana wani mutum mai suna Alhaji Bobo yazo gidan da safen Allah lokacin suna karin kumallo da garin kwaki a tsakar gida. Jin sallamarsa yasa Abba miƙewa da gudu ya shiga ɗaki yana cewa Goggo tace masa baya gida. Wasu zaratan maza ne suka shigo su uku cikin zafin nama suka fara tarwatsa tukwanen dake tsakar gidan suna ball dasu, salati Goggo tayi ta miƙe tana neman taimako wai ƴan fashi sun shigo masu gida. Alhaji Bobo yashigo Rai aɓace yace "Malama kiyi mana shiru, kuma kicewa macucin ɗanki ya fito waje, idan kuwa ba hakaba sainasa anyi raga raga da sauran haƙoran dake bakinki. Cikeda tsoro Goggo ta ƙwala ihu tace "Zaidu kafito, kanaji kana gani za'a hallaka mamanka amma kana ɓoye aɗaki ɗannan" ɗaya daga cikin samarin ne suka shiga ɗakin da Goggo ke kallo azafafe ya hurgo Abba waje. Rikeshi sukayi su biyu Alhaji Bobo ya kids masa mari akumatu yace "Zaidu ina takardun filaye na dana baka saƙo ka kaiwa gidan sanata? Ko ka fitar mun dasu koka sa ran zamanka acikin gidannan ya ƙare" fitsari na neman ƙwacewa Abba a wando ya yi saurin matse ƙafa yace " Alhaji kayi haquri, kaɗan bani lokaci. Wlh wani ɗan ƙwangila na saida mawa, amma inajin ya shigo gari zan je na yi ƙoƙarin amso maka takardunka " tsawa ya daka masa yace "kar ka maidani wawa Zaidu. Daga gidan ɗan kwangilan nake kafin nazo nan. Tuni angama gine gine a filaye na, ka siyar masa da filayena a matsayin naka bayan kasa a canza sunana zuwa naka. Kai omale ku kira masu bull dozer dinnan ayi daga raga da gidannan kar komai ya tsira. Sunaji suna gani masu bull dozer suka zo, aka fatattakesu waje, cikin abinda baifi minti arba'in ba aka yi ƙasa da gidansu Goggo. Mutanin anguwa sun fito sun tsatssaya suna kallon wannan ikon Allah. Goggo kuwa sai birgima take akan yashin gidan tana kuka har zaninta ya kwance saura patarinta tsamamme da baya samun wanki. Mai garine ya tausaya musu yace su zauna agidansa zuwa gobe sai suka ma hanya zuwa koma inane zasu. Washe gari Abba yace su shirya sukoma Kano zuwa gidan Baba Auwalu. Hmmm Ranan Monday itada kanta ta shiryashi cikin three pieces suit mai kyau, amma duk wankannan kememe taki yasa turare, sai faman manne mata yake (su MJ ansami abun da akeso), da ƙyar ta ɓanɓareshi ajikinta ya tafi aiki. Ahaka ma bai wani jima ba yadawo gida. Yanayin yadda taganshi sai ya tuno mata da lokacin first night ɗinsu. Yadawone idanunsa wani iri. Tana kula dashi kamar tsoro yake ya tambayeta kar tace a'a, itakuwa data gane taje tayi wanka ta shirya cikin bumshot da half vest irin mai botura agabansa ko bra batasa ba ta ɗora hijab akai. Aɗakinsa ta sameshi ya fito daga toilet dagashi sai gajeren wando. Kallonta yayi idanunsa aƙanƙance ya marairaice fuska ya buɗe mata hannunsa. Da gudu ta cire hijabi ɗinta ta ƙarado gareshi, kusan suman tsaye yayi a lokacin data cire hijabi, yadda boobs ɗinta ke up and down shine ya kashe masa tunani. Baiyi sune ba sai ji kawai yayi ta haɗe bakinsu wuri ɗaya azafafe take bashi hot kisses. Dama kuwa jira yake shima ya kama kanta da kyau ya karkace yana maida mata martani. Komai zafi zafi sukeyinshi, tunaninsu da kayansu duk yabar jikinsu batareda sun saki ba, irin foreplay ɗin dasukayi har Aneesa ta mance irin azabar daya gana mata a lokacin farko. Lokacin data dawo hayyacinta kuwa tuni MJ yayi nisa a duniyar ta bayan yayi addu'a, babu wani maraba da lokacin farkonacan sai dai wannan karon tayi iya ƙoƙarinta wurin ganin batayi masa magiya ba, hakan kuwa itama ya taimaka mata, dan inda batayi haka ba, zai yi amfani da force ayanda yake bayaji baya gani. Zunduma ihu yake son ransa itakuwa kamar gawasau hawaye da kukan zuci, bai tashi sarara mata ba saida ya gwada duk wata style daya sani akanta. Irin ambaliyar dayayi mata kuma, ita kanta tasan cewa ya daɗe yana haquri da rashinta akusadashi. Mirginawa gefe yayi yana maida numfashi, saida yaji ƙarfi sosai ajikinsa sannan ya mike ya wuce toilet ya haɗa ruwan zafi a tub, dawowa yayi ya sungumeta zuwa toilet din. Sosai ya gasata kuma wannan karon batayi masa irin kiciniyar datayi wancan lokacin ba. Wanka sukayi ya fito da ita ahannu sai faman zuba masa shagwaɓa take yana biye mata. Ahaka rayuwa taci gaba da tafiya, cikin tsantsan soyayyar juna da kulawa. Basu kara zuwa Kano ba sai lokacin cikinsu Isma'il. Anyi taro sosai nagani nafada, kuma an ɗaura aure lafiya an kaiwa kowa amaryarsa inda Isma'il shi zai koma can Port Harcout da amaryarsa amma zasuna zuwa gida akai akai. Ummu sulaim din Doctor Sultan kuma anan Kano gidansu yake. Kowa yana ji da matarsa suna kashe love yadda Yakamata. Aadil yayi wayo inda yanzu zama yake yi, ga Amin daya zama maƙale mata awurin Ameera. Ya koma makarantarsa itama ta koma Tata. Haka da safe zasu shirya sai su kawo Aadil gida wurin Ammi, sai ya kaita makaranta daganan shima ya wuce tasa makarantar. Kowa saida ya sheda nutsuwar Amin. Hatta VC ɗinsu dayayi masa wulaƙanci duk yanzu an shirya yazama obedient. Yanzu haka yana final year ɗinsa, Ameera Kuma tana SS 3 kenan zasu rubuta WAEC. Tun bayan bikin su Isma'il dasuka dawo gida ya lura da yawan ƙananan ciwo datakeyi akai akai. Har yasa baya zuwa aiki shi kadai saidai suke tare, ita aikinta bacci kawai a office dinsa. Idan yayi baƙi kuma saidai abuɗe musu wani office daban saboda kar adameta. Da yamma kuma kafin sukoma gida to ƙa'ida ne suke cold stone asiya ice cream kala kala. Abun mamaki kafin washe gari tas ta shanye su. Bai taɓa lura da cewa tunda tadawo gidansa ko sau ɗaya bata taɓa yin period ba tunda shi kullum cikin shan zuma yake. Ga wani kyau data ƙara tayi fresh Masha Allah. Kusan wata biyar kenan da dawowarta Abuja. Tana zaune tana shan ice cream yadda ta saba, ta buɗe saman rigarta tabar ciki awaje, saukowa yake daga kan bene. Tundaga nesa ya hango yadda cikinta ya taso yayi kummm dashi, har yana cin tuntubi ya ƙaraso wurinta da gudu ya durƙusa aƙasa yasa hannu akan cikin, kamar jiraa cikin yake taji wani shafi pain adaidai inda hannunsa ya taɓa kamar an buga mata abu awurin har saida ta saki ƙara. Kallon ta MJ yayi yace "sweetheart rabon da kiga period ɗinki tun yaushe "? Sai yanzu ma ta tuna da wani abu wai shi period, kan uba. Aikuwa ta nace tun yaushe tayi period, badai wani cuta ne da ita ba. Rau rau tayi da ido zatayi kuka da sauri MJ ya hanata, yasan halin sarai idan tafara kuka to wani aikine daban rarrashinta. Kwantar mata da hankali yayi ya ce anjima zai siyo mata pt ta gwada. Bai jima ba kuwa ya fita yaje yasiyo yakawo, amma acan pharmacy aka ce masa yabari sai gobe da sassafe fitsarin farko saita gwada dashi. Da asussuba ya tashe ta tana cikin baccinta mai daɗi ga namomin kaza agabanta tana yagawa, kuka tasa mishi wai yayi mata bukulu yasa naman kazan ya gudu. Aneesa akwai abun dariya. Dakansa yayi mata gwajin, tare suka tsaya sun kafe pt da ido suna jiran ganin sakamako. Positive ya nuna musu wani irin ihu sukayi su biyun a toilet, da sauri ya ɗagata sama yana murna. Itama haka, Finally zata haifi babyn kanta kuma da mutumin da take tsananin sonsa fiye da kowa. Har hawayen farinciki yayi yana murna. After three months. Tana ture zungumemen cikinta akitchen tana aiki a hankali, ƙafafunta duka biyu sun kumbura suntum. Ga wani budewa data ƙarayi kamar wata mama, hips dinnan bajam kenan, boobs kam ba'a magana. Breakfast tray ɗinsa ta riƙe ahannu zata fitar falo, tanasa ƙafa wajen kitchen taji ƙafan ya riƙe gam yaƙi motsawa. Cikinta da bayanta ya riƙe, sake trayn tayi aƙasa tana dafa bango wai wash wash take tana cize leɓe. Saukowarsa kenan yaji ƙaran zubewan abu aƙasa, da sauri ya karaso wurinta inda yaga tana murƙususu. Cikin fitar hayyaci ya sungumeta sai waje yana ihun abuɗe musu gate da sauri. Sun iso asibiti babu bata lokaci aka kaita labour room Allah yakawo mata cikin sauƙi, shiganta da aihuwarta duk baikai minti goma ba. Tsaleliyar budurwa ta haifo kyakyyawa mai Kamada Mujahid. Nurses sun gyara ta da babyn, tana bacci aka kawo wa MJ ɗiyarsa. Har hawaye take a lokacin daya riƙe little princess ɗinsa ahannu, sai yanzu ya yarda blood is thicker than water. Kwata kwata baiyi irin connection dinnan ba alokacin da Neehal ta haifo Akeer duk da yaso yaron kaman me. But this little Angel right here is different, jinta yake har cikin jininsa. Rubguneta yayi tsam akirjinsa yana sumbatar goshinta. Labarin aihuwa ya kai wasu Hajja har Kano cikin minti kaɗan. Duk aka fara shiri za'a zo ganin baby. Jirgi guda na Abby sukayi aka jibgosu a birnin tarayya. Aneesa sai buɗe idonta tayi taga Innatinta azaune akusada ita. Saida tabi kowannensu da kallo ta dawo kan Innati saita fashe da kuka tana neman yafiyar mahaifiyarta tana cewa ashe haka aihuwa yake, dan Allah ta yafe mata. Shafa kanta Innati tayi tace mata Allah yayi mata albarka. Babyn wacce ke hannun MJ ya kafe matarsa da ido ya miƙowa Innati ta ajewa Aneesa saman kirjinta. Wani irin soyayyar yarinyar take ji har cikin ƙashin bargon huhun naman jikinta 😂. Kwanasu ɗaya a asibiti aka sallamosu gida. Last page dropping tomorrow inshallah 🥹🥹 🌷 RAYUWAR ANEESA 🌷 REEMAH ✍️ PG 96_100 Last page. Wannan page ɗin sadaukarwa ne ga Mom Sani Ashanty Eeshert Maijama'a Zeinab Noor ɗin Zeinab😂 Khadijat Musa Maryam Sa'adatu Aliyu Musa Aisha Abdullahi Maimahaman Kagana Mmn Minal Queen Halery Hadiza Alkali Mrs Abdulkarim Dama sauran Fans din RAYUWAR ANEESA wadda ban ambato sunansu ba. Ina godiya sosai da sosai akan goyon baya da kuka bani wurin kammala wannan littafin lafiya. Sharhinku, addu'o'inku da kuma ƙaunar da kuka nuna mun supersedes all🥺. Ina alfahari da ku ako ina. Ina sonku fisabilillah 🙏. Allah yabar zumunci, yahaɗa mu cikin aminci a Darussalam. Nagode Nagode Nagode sosai sosai🙏♥️. I love y'all 🥹🥹🫰 🌷🌷🌷🌷🌷🌷🌷 Ranan suna Baby girl taci sunan Haseena. Baban jego yayi ƙoƙari sosai, babu wadda ya rasa ci yarasa sha, ga sovenirs iri iri sai hamdala. Aneesa kam ba'a magana, tayi fes fes, wanka kala kala photographers har sun gaji da ɗaukan hotuna. Washe garin taro basu suka farka daga baccin gajiya ba sai wuraren sha ɗaya. Dake anan Abuja akayi sunan, dan haka Ammi ce ta zauna da Aneesa take yi mata wankan jego. Su Mamy da su Hajja aranan suna jirgin su ya ɗaga da daddare. Aneesa na cikin bacci taji Haseena ta tswala ihu inyaaaa, a firgice ta farka ashe wai wanka Ammi keyi mata, ina irin ɗaga yaro da ake yi sama ayita jijjigashi, da gudu MJ ya shigo Ɗakin har yana cin tuntubi, ganin anjuya masa kan yarinya ƙasa Ammi ta riƙe kafafunta ana jijjigata yayi saurin shigowa ya karɓi yarinyarsa ya rataya a kafaɗa. Haɓa Ammi ta riƙe tana kallonsa tace "yau naga ikon Allah. Mujahid meye haka, ka bani yarinya na shiryata banson iskanci" ƙara matse yarinyar yayi aƙirjinsa ya ɗau towel ɗinta ya rufeta yace "haba Ammi, ƴar yarinyar nan ake juya mata kai ƙasa, in jini ya dawo kanta kuma fa" Aneesa na zaune akan gado ta riƙe kumatu tana kallon draman Ammi da ɗanta, shi kuwa ya haqiqance baza'a ƙara yiwa ƴar sa haka ba. Ran Ammi ya ɓaci ta miƙe ta haɗa bawon wankan da komai ta fitar dashi aɗakin tana ta zalzale masifa amma MJ na tsaye ƙyam ya rungume ƴarsa sai zabgawa Aneesa harara yake kai kace itace tayiwa ƴarinyar haka. Turo baki gaba tayi tace "to Yaya ni sai faman hararata kakeyi saikace ni nayi maka laifi" haɗe fuska yayi yace " yanzu tsakani da Allah, yarinyar nan guda nawa take, kina kallo ake jefa mun ƴa asama saikace paper" miƙewa tayi ta gyara riganta ta shiga toilet dan watsa ruwa, tana jinsa yanata faman masifa yana sakin tsaki time to time. Har tayi wanka ta fito, tasameshi yana damben sa wa baby pampers, dariya ya kamata sosai ganin yadda yajuya gaba baya ya wani ci serious irin shi ya iya dinnan. Itako bby sai hurga ƙafa takeyi asama ta kasa zama wuri ɗaya sai kuka take. Daya gaji ya miƙe yana haɗa fuska ya kalli Aneesa yace "gatanan ai, tun abinda Ammi tayi mata yasa ta kasa yin shiru, ni kizo kibawa yarinya nono ko zata yi shiru" murmushi tayi ta ƙaraso ta ɗauki Haseena tasata saman cinyarta ta buɗe towel din ta tafara shayar da yarinyar. Yana tsaye yana kallonsu cikeda burgewa, har yarinyar tafara bacci sannan tacireta ta ƙarasa mata shirin. Yau Abby yayi baƙi daga Adamawa, Governor ne da kansa yazo ziyara, dake shida Abby classmates ne a secondary school, His Excellency Muhammad Waziri. A babban falon Abby wadda ba kullum ake budewa ba sai idan anyi baƙi na musamman, anan aka buɗe aka gyara tsaf tsaf aka barbade da turare. Tunda safe da Abby ya faɗawa su Innati zai yi baki, itada su Mamy suka shiga kitchen sunata shirya abinci kala kala. Da misalin ƙarfe ɗayan rana suka iso gidan, motoci ne har motoci, gana sojoji gana bodyguards zai Kuma na shi Babban baƙon dakansa. Baza'a kira shi da dattijo ba saboda yanada sauran ƙarfi ajikinsa, kuma kana kallon sa kaga ma'abocin daga ƙarfe hala tun yana yarintarsa. Fari ne amma ba cancan ba, Fulanin asali kyakyyawa, ga tsayi. Abby na tsaye abakin ƙofan motansa yana jiran fitowar abokinsa. Ana buɗe masa motan ya fito suka rungume juna da Abby suna bubbuga bayan juna, Abby yace "sannu da zuwa baban tuzurai. Kaide Moha ALLAH ya nuna min ranan aurenka. Gani nan harda jikoki amma kai ko inyaaaa babu, dan Allah kafada mun yadda kake rayuwar babu mace atare da kai" murmushi His Excellency yayi ya shafa ƙeyarsa ƙasa ƙasa yace "lemon tsami da azumi sune suke taimako na" dariya Abby yayi suka tafa hannu kaman wasu samari. Ƙarasowa sukayi cikin falon suna wasa da dariya. Masu aiki ne suka fara aikin jero kayan motsa baki, ga kuloli na abinci kala kala. A plate ɗaya akayi serving ɗinsu, suna ci suna warwaso yadda dai classmates keyi lokacin nan na secondary school. Bayan sunci sukaje sukayi sallah sannan suka dawo. Abby yace bari yaje ya kirasu Hajja da sauran mutanin gida su zo agaisa. Afalon Hajja yasamesu dukkansu suna hira. Innati taci wankan abaya ne beige colour wadda ya karbi fatar jikinta dayayi lugui. Kiransu Abby yayi akan suzo agaisa da His Excellency, ɗankwalin abayarta ta yafa akai, jelan gashinta na yawo a bayanta, Hajja da Mamy na gaba itama ta biyo bayansu. Da sallama abakinsu suka shiga falon, Yana gishingide da cushion, Yana ganin Hajja ya miƙe da sauri ya sauko ƙasa ya rusuna cikin ladabi ya gaida ita. Mamy ma ta gaida shi, sai yanzu ya kalli Innati dake gefen Mamy, aransa yace "Masha Allah tabarakallah, what a beauty" yadda Abby yaga abokinnasa ya kafawa ƴar uwarsa ido yayi murmushi kawai. Itako Innati ranta fes ta gaida shi, basu jima ba suka fita afalon yarage Abby da abokinsa. Ɗan sosa ƙeya His Excellency yayi yace "Abdul, wannan mai maroon abayar ƙanwar Hajja ce, naga suna bala'in kama"( note shi bai san cewa Abdul nada ƙanwa ba) girgiza kai Abby yayi ya ciza Apple ɗinsa yace "kai Malam ƙanwata ce fa, wadda muka shekara muna nema" haɓa His Excellency ya riƙe yace "haba, kai Masha Allah, wallahi ta fika kyau nesa ba kusa ba" harara Abby yayi masa yace "Malam abini ahankali, ni ne nan waliyyinta, tunda suka shigo falonnan na harbo jirginka. Ayi mun ladabi ko nabawa wani, kasan zan aika" shafa ƙeyarsa yayi wadda babu ko alaman furfura yace "haba wa, Ni na isa. Ai kai Yanzu Yaya zan riƙa ce ma. Allah yaja zamaninka yayanmu, Allah yabar mana kai yayanmu, kai Yaya Allah yayi maka me Nice 🙂 " wani wawan dariya Abby yayi yace "shegen miya, da baka dawo hanya ba'ai, yanzu dai kace nine nafi kyau idan ba haka ba, cire aranka kawai" da sauri His Excellency yace "habawa, ina taga kyawunka ai kai ƙarshe ne yaya, kambulusi" azuciyarsa yace "Allah ko rabin kyawunta baka gani ba"😂. Kafin arufe shafinnan saida Abby ya amince zai yiwa Innati magana akan abokinnasa. Idan aurennan ya tabbata sai yafi kowa jin daɗi, saboda Muhammad mutum ne har mutum, alokacin duk cikin ajinsu babu mai kokarin shi, kuma yanada hankali ga sanin Yakamata. Bayan tafiyar His Excellency, Abby yayiwa Innati magana da daddare, kunya ya kamata, wai maza basuda ta ido, shikenan daga ganin mutum sau ɗaya sai kace kafaɗa sonshi. Bawai dan kuɗinsa ko kyawunsa ba, a'a, tana fargaban ta ƙara jefa kanta a wani rayuwar kunci na aure, gara tayita zama da mahaifiyarta tana kula da ita har su rabu lafiya, tayi renon jikokinta. Saida Hajja tasa baki amaganan sannan Innati ta sallamawa ranta kawai ta yarda kuma tayi addu'ar Allah yasa shine mafi alkhairi. A daren ranan Abby ya kira His Excellency ya sanar dashi abinda ake ciki. Farin ciki kamar zai kashe bawan Allah, Abby bai ɓoye masa komai ba na cewa Innati ta taɓa aure harda yara, kuma yace yaji ya yarda zai aureta ahakan. Cikin satin aka sa ranar aurensu nan da wata ɗaya curr. Kamar bikin farko, haka Hajja ta dinga jigilan kuɗade tasa masu gyara sukazo aka fara yiwa Innati. Duk yadda tayi da Hajja amma tsohuwar taki tace "a'a Nadeen, aurenki na farko banyi abinda ya dace ba, aurenki na biyu wallahi sai na kai maqura" haka dai ta haqura ta ƙyaleta. Gidan amare da angwaye ba'a cewa komai, kowa yana zaune da matarsa lafiya. Habiba na can tana renon matashin cikinta, itakam tagode babu wani laulayi mai zafi saidai yawan Bacci. Ba kamar Ummu sulaim ɗin Sultan ba, baiwar Allah duk tabi ta rame saboda wahalar da cikin ke bata, dake cikinta bai kai na Habiba a watanni ba. Mazajen kam an dage kowa na kula da matarsa daidai gwargwado, Ya Isma'il soyayya iya soyayya babu kama hannun yaro, yadda yakeji da matarsa bazama kace yataɓa soyayya da wata mace kafin ta ba. Amin da Ameera sai yadda Allah yayi kawai. Daga ita harshi an rasa wanene gwara awurin soyayya. Suna kulada juna yadda ya dace. Aadil yana wata bakwai akayi masa ciki, aranan da Ameera tagane cewa cikine da ita, tayi ƙaramar hauka. Ita atataf saidai azubar da cikin, bata shirya ɗaukanwa Aadil ƙani ko ƙanwa ba. Cewa take yaron bazai yi lafiya ba, shi kuwa Amin shima ya nace yana son abunsa babu abinda za'ayi. Da ƙyar yasamu ta haqura, kuma tacigaba da shayar da Aadil ɗin. Yanzu haka tana hundred level kenan a buk inda Amin ma yake, tana karantar Biochemistry. Cikinta yanzu yana wata huɗu kenan harya fara tasowa. Ƴan mata har kishi suke da ita, ga haɗadden motar da Amin ke kawowa school idan ya faka agaban faculty dinta zai fito ya buɗe mata ƙofa sannan ya karbi jakanta,bazai fito ba sai ya tabbata yakaita lecture theatre ɗinsu. Da yamma idan ya riga ya tashi haka zai jira harta gama ya ɗaukota suwuce gidan Mamy su ɗauko Aadil sannan su wuce gida. Rayuwa kullum sai ƙara tsanani takewa Abba da Goggo, sunje Kano amma haka baba Auwalu yashafa tozali a idonsa yaci musu mutunci kamar ba ɗan uwansa da mahaifiyarsa ba. Koran kare yayi musu yace babu inda zasu zauna agidansa. Haka sunaji suna gani suka koma Adamawa, yanzu a wani ƙwangon gida suke zama. Duk sun zama abun tausayi, shi Abba wani kwararraben wheelbarrow yasamu yana turawa a kasuwa, idan mutum yayi siyayya kuma kayan sunyi masa yawa, Abba zai karɓa ya sa a wheelbarrow dinsa ya tura har inda mutumin zai shiga adaidaita sahu. Itakuma Goggo gishiri take saidawa, idan tasiya packet guda ɗaya saiyayi kaman sati ɗaya Kafin ya ƙare. Tayiwa Baba Auwalu tsinuwa yafi bakin kwando, ta mance cewa abinda kayiwa ɗan wani sai ɗanka yayi maka kokuma ayiwa ɗanka. Gashi yanzu rayuwa ta juya, Innati na cikin daula su kuma suna cikin ƙunci. Allah kenan, Ya Allah aduk halin damuke ciki kar ka sa muyiwa na ƙasa damu mugunta, kar mu cutar kuma kar acutar damu da ƴaƴanmu🙏 Ana bikin Innati saura kwana goma Su Aneesa sukayi arba'in. Aranan duk suka tattara daga ita har Ammi zasu dawo Kano sai bayan biki, zuciyan mazane kawai yasa Mujahid baiyi kuka ba. Ammi ce ta tsaya masa awuya lallai saidai su taho gida da Aneesa, babu yadda ya iya haka ya yarda. Yanzu haka yana zaune da Haseena ahannu yana kallon yadda Aneesa ke kai komo tana shirya musu kayansu a akwati. Saida tagama tajuyo ta kalleshi taga wani irin mayataccen kallon dayake binta dashi. Kashe masa ido ɗaya tayi tayi murmushi tace "Ya MJ menene" haɗa fuska yayi yace "sai yaushene zan cancanci acanza mun wannan tsamammen sunan na Ya MJ, ko sau ɗaya baki taɓa kirana da wani pet name mai daɗi ba, yanzu kikayi wasa sai na hana ku wannan tafiyan sai ana gobe bikin mutafi tare" dariya tayi, tasan ƙaramin aikinsa ne kuwa yanzu ya hanata tafiyan. Matsowa kusada shi tayi ta karɓi Haseena ta aje saman gado tayi kujera da cinyarsa, hannu tasa ta saƙalo ƙeyarsa da kyau suna kallon juna. Kiss tamanna masa agoshi tace "haba Baby Boy, abun bai kai haka bafa. I'm sorry bazan ƙara ba kaji"? Ashagwaɓe yace "to Ni dai baby, Allah nayi kewarki, tun yaushe banji ɗumin matata ba, duk Ammi tabi ta takura mana. Yanzu kuma ina murna kinyi arba'in zan samu na rage zafi kawai za'a taso da wani kabli da ba'adi " sauri tayi ta haɗe bakinsu wuri Daya, kamar jira yake yafara bata hot kiss har wani karkace wuya yake yana kama gefen kanta da kyau, cikin fitar hayyaci ya buge zip ɗinta ƙasa ya sauke riganta, boobs dinta dake acike yakaiwa damƙa yana matsasu yadda yakamata. Ba'ajin komai sai sautin numfashinsu dake fita sauri sauri, tabbas idan mutum ya tsaya abakin kofa tas zaiji. Kansa yacusa atsakanin boobs dinnata yana basu kisses, tunda ta aihu baiji duminsu ba sai yau. Hook ɗin bra ɗinta yasa hannu ya ɓalle, sai gasu muraran abayyane, kamar jariri haka ya sa bakinsa aguda ɗaya yafara bata good sucking ahankali. Cije leɓe tayi bataso tayi ihu amma tabbas badan Ammi ba irin ihun dazata saki sai gidan ya amsa. Kullum complain take cewa idan Haseena tana shan nono zafi yake mata, amma meyasa da MJ yasa bakinsa akai wani irin daɗi taji har ƙwaƙwalwata, ƙara damƙe kansa tayi da kyau tana banƙaro masa kirjin. Shi kuwa an dage sai zuƙowa yake yana lumshe ido, cire masa baki tayi awannan ta mayar masa da ɗayan, har wani riƙe masa shi tayi irin yadda uwa ke riƙewa yaronta idan tana shayar dashi. Ganin bazai iya jurewa ba akasalance ya miƙe da ita ajikinsa ya wuce wurin ƙofa yasa key sannan ya dawo dakin. Su kansu idan aka tambaye su ya akayi kayansu yabar jikinsu har rantsuwa zasuyi suce basu saniba. Ɗaukanta yayi suka shiga toilet dan karma ajisu, sun mulmula juna yadda ya kamata saidai basuyi penetration ba. Sun kai kusan awa a toilet suna juya kansu sannan sukayi wanka tare suka fito. Har wani murmushin jin daɗi yake, dakansa ya shiryata cikin leshi doguwar riga mai fadin wuya. Tana riƙeda da Haseena shikuma yaja akwatin suka fito. Afalo suka sami Ammi tana zaman jiransu. Fitowa sukayi suka shiga mota sai airport, basu jima ba jirginsu ya ɗaga. Haka MJ ya dawo gida da dimbin kewar iyalinsa. Bawani event akayi da bikinba. Iya walima kawai akayi. Saida ana gobe ɗaurin aure kafin su MJ, da Isma'il suka diro agari. Gida ya cika maƙil da jama'a. Ameera da Aneesa suna makale da mamansu, wai yau sune mahaifiyarsu zata ƙara aure Allah sarki. Har tausayin mahaifinsu ya kamasu. ALLAH kaɗai yasan a wani hali yake ciki. Koma menene ai mahaifinsu ne, kuma sun daɗe da yafe masa abinda yayi musu shida mahaifiyarsa. Washe gari juma'a, dubban jama'a suka sheda ɗaurin auren Nadeen Isa Mainoma da angonta Governor Muhammad Waziri of Adamawa state. Bikin ɗaya girgiza Media, babu wadda ya taɓa tunanin Governor ɗin Adamawa baida mata sai yau da labari ya dinga yawo akan cewa farkon aurensa kenan. Yakasa rufe baki, sai baza babban rigansa yake yana gaida jama'a. Can gida ma ancika dam. Matan Governors na arewacin Nigeria ɗaɗɗaya ne kawai basu halarci bikin ba. Kowa yaga Mamy sai ya kyasa, Allah sarki daga matar Zaidu yanzu ta koma matan Governor wato First Lady ɗin Adamawa Yola. Su Aneesa da su Ameera da sauran matan yaran gidan Jenar anko sukayi na wani tsadadden cutton lace black mai adon duwatsu, baby Haseena da Aadil suma sunsha kwalliya cikin kayan yara na kanti masu kyau sai zuba ƙamshi suke. Bayan mazajen sun dawo daga ɗaurin aure, duk suka fito harda Hajja da Innati Amarya tasha kyau cikin leshi ga alkyabba an ɗaura mata asama, banda matar Governor yanzu matar Yarima ce, dan angonnata shine babban yaron Sarkin Adamawa kuma dagashi ba ƙari. Atsakiya suka sata ga His Excellency agefenta sai sauran yaran gidan Jenar gaba ɗaya da matansu, ga Hajja gasu Mamy ga kuma Abby. Amin na riƙeda Aadil, MJ Kuma yana riƙeda Haseena, kowa ya tsaya kusada matarsa akayi babban round na group picture. Kyawun hoton ba'a magana. Jama'a duk sun tsaya suma da wayoyinsu suna daukan hoton wannan ahali mai cikeda kamala da kuma farin ciki. Angama taro lafiya lau, duk an watse saura mutane kadanne wadda suma gobe ko jini duk zasu koma gidajensu. Aranan Innati adakin Hajja ta kwana, sun jima suna hira kafin suka kwanta Innati tasa kanta asaman ƙirjin mamanta tanaji kamar karta tafi. Washe gari da sassafe aka fara shirin kai Amarya. His Excellency na garin Kano bai koma ba yanace ƙememe sai tareda amaryarsa zai tafi. Hardasu Aneesa a ƴan rakiyan amarya. An shirya Innati cikin lafaya aka ɗora Mata alkyabba daban bana jiya ba, na yau harya ninka na jiya haduwa da kyau. Motoci sunyi jeri awaje suna jiran fitowar amarya, Ameera da Aneesa suna gefen Innati sun rirrike mata hannu, sun bar ƴaƴansu dasu Mamy da Ammi wadda suma dasu za'ayi tafiya. Motar dake tsakiya aka sa Innati Ameera da Aneesa suka shiga, su uku ne kawai amotan sauran mutane suka jera kansu a sauran motocin. Jirage guda uku private Jet aka tanada saboda kai Amarya. Jirgin farko aka sa Innati dasu Mamy su Aneesa su Ameera dasu Ammi. Jirgi na biyu kuma Abby da Ango Saisu MJ da su Isma'il. Jirgi na uku kuma sauran mutanene ƴan kalan dangi wadda ba'a rasawa a ko wani sha'ani. Cikin kowani jirgi aka zuba jiga jigen sojoji da guards. Ansauka a jihar Adamawa, airport yacika maƙil da jama'a, anzo taya Governor murnan aure da yayi. Ba'a wuceda Innati gidanta direct ba, Masarautar Yola aka wuce da ita, fadan sarki aka kai Innati. Ga mahaifiyar yarima tana zaune agefen Sarki akan kujerarta na alfarma. Agabansu Innati da angonnata suka rusuna suna gida iyayensa, da sauri Sarauniya Zainab ta mike ta ƙaraso inda matan ɗanta ke rusune ta jawota jikinta ta runguma. Daɗi kamar ya kashe His Excellency ganin matarsa ta samu karɓuwa awurin mahaifiyarsa. Karramawa babu irin wadda su Abby da mutanensa basu samu ba. ANEESA daɗi takeji, Allah sarki komai yayi farko zai yi ƙarshe. Gashi abinda Innati ta rasa a gidan mahaifinta gashi tasamu a gidan wani daban. Wani ƙwalla ne taji ya zubo mata, MJ ya kalleta ƙasa ƙasa yace "baby kuka kuma? Meya faru"? Murmushi tayi ta girgiza kai tashare hawayenta tace "ba komai Sweetheart, kawai hawayen farinciki ne" shima murmushin yayi yasa hannu abayanta yana shafawa ahankali cikin sigar rarrashi. Sai bayan sallan Asr aka wuce da innati Government House, dake ba permanent house dinsa bane, amma anan yake zama a matsayinsa na Gauna. Gidan ya haɗu iya haɗuwa ba'a Magana. Washe gari su Aneesa suka fita yawon ganin gari itada su MJ da su Isma'il da matansu amota biyu. Har unguwarsu Aneesa sukazo. Mutane sai faman kallo sukeyi suna mamakin su wanene wannan kuma suka diro cikin unguwarsu da rana tsaka. Daidai zasu sha kwanan gidan su Aneesa suka ci karo da mai wheelbarrow. Tundaga nesa MJ yagane Abba, mamaki yakamashi, abinda Abba yakoma yi kenan🤔. Ikon Allah. ANEESA na ganinshi tace "innalillahi Ameera wlh Abba ne fa" da sauri suka fito da ƴaƴansu ahannu suka zagayo inda yake. Mamaki yakama Abba, mekuma yakawosu Aneesa cikin garinnan. Duk sai jikinsa yayi sanyi, baiso suganshi a wannan yanayin ba. Rayuwa takoya masa darasi wadda har ya koma ga Allah bazai taɓa mancewa ba. Wani irin kuka ne ya taso masa ya zauna awurin yanayi kamar ƙaramin yaro, durƙusawa Aneesa da Ameera sukayi suka kamo hannun babansu suma suna hawaye. Haɗa hannunsa yayi wuri ɗaya yafara neman gafarar su, atare suka rungume ubannasu suna bashi haquri akan yadaina kuka. MJ da sauran duk jikinsu yayi sanyi, lallai Abba ya gane kuransa kam, Allah ya kyauta. Har gidan da suke zama ayanzu yakaisu, sun ji tausayinsu akai kuwa. Ga Goggo yadda rayuwa ta koma mata, ga kuma halin tsufa, itama kukan tayi tana neman yafiyarsu. Saida sukayi shiru suke tambayan Innati. Ananne suka basu labarin aurenta da Governor, sosai Abba yaji zafin abun amma yazaiyi da ransa yanzu haquri yarage nashi. Girgiza kai Goggo tayi tana hawaye tace "Allah sarki, Allah maiyida bawa yanda yaso. Hussaina Alkhairi yacimiki aduk inda kike. Haqiqa mun zalunci rayuwarku data mahaifiyarku. Dan Allah ku yafe mana" sai kuma tafashe dakuka har tana fyace majina da gefen zaninta. Karɓan Haseena da Aadil tayi ta haɗasu wuri ɗaya ta rungume, dake Aadil yanada wayo, sai yasa hannu afuskarta yana share mata hawaye. Duk awurin sai da jikinsu yayi sanyi. Kafin su tafi saidai MJ yayi musu alƙawarin zai taimaka masu, zai bawa Abba sana'a sannan zai basu gida, kuma yanemawa Goggo mai aiki dan afadinsa aiki banata bane kuma a wannan shekarun. Kiran Innati Aneesa tayi awayarta tabawa Goggo sukayi magana, ta ƙara neman yafiyarta, itama Innati saida ta tausaya musu. Kuma tayima Goggo alƙawarin bayan kwana biyu zatazo har inda take tareda mijinta suzo su gaida ita. Haka suka rabu cikin jin daɗin yadda komai ya dawo normal yanzu. Washe gari kuwa duk suka koma Kano. Kwana biyu suka ƙara Isma'il ya wuce da matarsa Port, shikuma MJ yawuce danasa iyalin birnin tarayya. Ten years later Wata kyakkyawar yarinya na hango zaune a kan cushion tana danna tablet ɗinta, idanunta sanye da medicated eye Glass. Kana kallonta kaga ANEESA basai kayi tambaya wacece mahaifiyarta ba. Da gudu suka fito daga ɗakin ɗaya a gaba ɗaya abaya suna rige rigen zuwa wurin sister Haseena. Suna isowa babban wadda namiji ne yace "sister Haseena, pls ki raba wannan gardaman. Inace Dad yafi Mum kyau ko? Kenan Ni kuma ina Kamada da Dad automatically nafi Basma kyau" murmushi Haseena tayi tace "nidai ba'a bakina za'a ji mutuwar sarki ba. Kuje ku tambayi Dad dakansa zai baku amsa" wadda yaron mai suna Khalifa ya kirada Basma cikin maganarsu ta yara wadda bai gama fitowaba tace "wlh kayyane, mum ina tafi Dad cau, Dan haka nima nafi big bro cau" harara Khalifa ya bankawa Basma yawuce waje da gudu ya dauki ball dinsa ya fara wasa a field. Horn akayi abakin gate, yana ganin motan iyayensu ya shigo da gudu ya ƙarasa wurin ya tsaya yana tsalle. Mujahid ne ya fara fitowa kafin Aneesa, sun ƙara girma musamman Aneesa wacce yanzu tazama "Nurse Aneesa", kuɗi ya zauna ga kwanciyan hankali ba'a cewa komai. Basma da Haseena suka fito suma farfadan gidan, sama MJ ya daga Basma yana wasa da ita ita kuma sai ƙyalkyala dariya take, yarinyar babu inda yarage Aneesa itama kamar saidai eye colour ɗinta dabanne dana iyayenta, nata wani blue blue dashi. Cikeda farin ciki suka shigo cikin gidan suna wasa da dariya da junansu. Abubuwa dayawa sun faru cikin wannan shekaru masu yawan. Ciki harda auren Raihanah wadda ta auri wani ɗan matashin mai kuɗi bayerabe can garin Lagos sukeda zama. Mustapha kuwa yanzu yazama cikakken mutum, accountant mayen kuɗi. Shima ansa bikinsa nan da ƴan watanni. Yaran Ameera biyu, da Aadil da Fadeela tundaga lokacin bata ƙara aihuwa ba har yanzu. Isma'il kuma yanada yara biyu shima da Usman da Abdulazeez mai sunan Abby ana kiransa da Junior sai Ashna. Sultan kuma yaransa uku, da Alqasim sai Na'ima ƙaramar kuma tana hannu sunanta juwairiyya. Tauraronmu da Tauraruwa kuwa yaransu uku na huɗu yana ciki, Haseena da Khalifa mai sunan Abba wato Zaid sai Basma mai sunan Hajja wato Aneesa. Can Adamawa kuma Allah ya azurta Innati da samun ƴan uku alokaci guda, dukkansu baby boys. Aranan His Excellency kamar ya zuba ruwa aƙasa yasha saboda murna. Sarki ma haka, sune jikokinsa wadda Allah yabawa ɗansa ƙwalli ɗaya. Yaran sunsha gata ta gefe daban daban. Akwai Abeer, Ameer akwai kuma Aneek. Yara masu tsananin Kamada junansu, ƙaryane mutum ya iya bambanta su kota wani irin hanyane, ana ji dasu bana wasa ba. Alokacin da Innati take shayar dasu masu aiki guda uku aka kawo masu kulada yaran, kowa da ɗaya sune wankansu da wankinsu, iyaka aikin Innati tarbiyyansu sai ci da shansu. Yanzu haka shekarunsa shida a duniya, suna primary One kenan a wani babban private school. Kullum His Excellency dakansa yake kaisu makaranta ya kwaso su. Abba kam Masha Allah,sai godiya. Business dinsa yake yi ba kama hannun yaro, shagon saida atamfofi yake dasu har guda biyu. Yana aure da wata bazawara mai suna Hajara, har Allah yabasu ƙaruwan ɗa namiji. Goggo tsufa yazo bako ina take zuwa ba. Dake Hajara tana aiki as attendant awani ƙaramin asibiti, Goggo itace mai kulada yaron mai suna Mujahid suna kiranshi da yaron EFCC 😂. Ayau ake bikin fourtieth anniversary na Abby da Mamy. Gaba ɗaya jikokin Hajja da yaransu sun sauko agari. Babban hall aka kama na taron, inda komai su MJ ne dasu Isma'il sukayi. Dake Abby ya ritaya yanzu, saidai kawai ya miƙe ƙafa yaci arzikin ƴaƴansa abun alfaharinsa. Babu wani sauran bakin ciki da tashin hankali awannan ahali, saidai ace Alhamdulillah kawai.... Tammat bi hamdulillah Anan na kawo ƙarshen RAYUWAR ANEESA. A wannan tafiyar idan akwai wadda na taɓa ɓatawa rai ayi haquri ayafe mun🙏. Masu bibiyan littafina Nagode ƙwarai da gaske. Bazan taɓa mancewa daku ba ako ina. Nagode Nagode Nagode sosai sosai. Sai mun haɗu a littafina na gaba wadda insha Allah zai zo muku ne bayan na huta na miƙe ƙafa sosai sosai🥹🥹 Atayani da addu'a Allah yabani Sa'a a jarabawata🙏🙏 Taku har kullum REEMAH ✍️