ABAR SO COMPLETE BOOK BY NAFISA MAARUF SHEHU

Author :  Nafisa Maaruf Shehu Category :  New Hausa Novels 2026

Chapter   9 / 11

24K to 27K   out of 32.1K words

nan kuwa amatsayin uwa Antyn take awajen Nadhira

"Allah yabiya ki da gidan Aljanna amaryata" Dady yafada acikin aranshi cos yasan dawata daban ne amaryan nashi to ba makawa yarshi tashiga gari amma ji yanda take nuna tsantsan so ga gudan jini Nargis dinshi daya rage

"Take care of yourself Baby" Antyn tafada

"InshaAllah" Salim tagani yakura mata ido, Sai asannan mah ta ganshi ahankali takarasa inda yake ga idonshi yayi raurau ,tsungunawa tayi agaban shi

"Hey why do you look sober??" Ta tambaye shi (yafi jin turanci akan Hausa)"

"I'm gonna miss you our baby"yafada hade da rungumeta

"Calm down I will be back it's a matter of my troby Salim and I will also miss you dear" tafada tana breaking hug dinsu sannan ta tashi, juyawan ta keda wiya taga Amin yanufi gurin mota da trolley dinta alaman shi zai kaita

" Antynmu!!! I love you so much"tafada da dan karfi cikin sweet slim voice dinta daidai ta isa wajen motan Abdul

"I love you more dear"Antyn ta amsa ga murmushi kwance asamar fuskarta cos itama Nadhiran murmushi takeyi,

(Toh gareku matan da suke kishi da yaran miji,wasu kam ma a idon miji zasuyi behaving normal Wato mai two face kenan wasu kuma they don't care... Toh bari Kiji daga lokacin dakika fara hantaran yaran kina nuna kishin ki karara akan yaran agaban shi toh in yana miki 100% So toh ki tabbatar zai dawo 40% cos bada yaran yakamata kiyi kishi ba da uwansu yakamata kiyi idan kuma bata raye kuma saiki ajiye kishin ki agefe ki Kula marayu. Ke kuma mai two face kina nuna musu so agaban miji dazarar ya fita Zaki fara musguna musu toh billahi lazi in yazo yagane toh in son dayake miki
100% ki tabbatar ko 15% sonki azuciyarshi baizai sake haurawa kuma kinyi loosing kimarki darajarki da kuma mutuncin ki a idon cos koda kin daina mawa yaran abinda kike musu still zai dauka as pretending kikeyi. In anzo kuma kice kinason mijinki ko kin manta Suma daga jikin mijinki suka fito neh hala?? In kikaso su tsakanin da Allah zai daukaka kimarki ,mutuncinki da soyayyarki acikin zuciyar mijinki bama shi kadai bah harda yaran nashi cos bazasuyi kukan uwa bah. In bakiso su bah kuma kinason babansu me kikayi kenan ??wannan shi ake Kira da naughty work.Wlhy yaran ma bazasu na kallonki da daraja bah kuma daga karshe suyi sanadiyar mutuwar aurenki da baban su!!! DanAllah mata akiyaye cos yana daga cikin matsalolin da ake fuskanta ayanzu)

Mamakine yakamashi ganin motan Abdul tanufa bacin kayanta na motan shi

"Jeka fito mi da kayana acikin wancan motan kafin raina yabaci" tafada lokacin data shiga bayan motan

"Ohk ma" Abdul yafada cikeda da tsokana

"Kai miye zakayi??" Amin yatambayi Abdul dake kokarin bude boot din motan shi

"Spare me Aika nazo dauka" yafada yana fitowa da ido waje,haka yagama daukan trolley din sannan ya rufe boot kafin ya bar wajen, haushi kuma kaman ya kashe shi ganin irin abinda tamishi agaban jama'a.

"Ba laifin ki bane"yafada underneath his breath.

"Arrange my meeting with those guys,i will be in your area in no time"shine message din daya shigo wayanshi cikin gaggawa yayi dialing din wata number

"Ya akayi ne??" Shine abinda aka fada cikin wata katuwar murya daga dayan side din wayan

"Cewa akayi kuzo yanxu"

"Ohk gamu nan zuwa" shine abinda mai katuwar murya yafada.

Cikin motar dasuke babu wanda yayi magana, Nadhira ne ta katse shirun dacewa

"Kafara dire Hasana cos zanmawa ummi sallama"

"Toh matar yaya" Abdul ya amsa mata,suna isa daidai kofar gidan Nadhira ta sauka daga motan Sai ya rage daga Hasana Sai Abdul amotan,instead of tayi cikin gida sai tabiye wani hanya daban

" Aturo gidanmu sbd susan kafasa auren yarsu" Hasana tafada kaman bata damu bah at the same time tana kokarin bude motan domin fita.

Cak ta tsaya dalilin rike hannunta dayayi

"Haba Hasynah!!!"

"Nibah Hasynka bace" tabashi amsa a hasale

"Ohk Hasyn matar yaya"

"Better"

"Am so sorry,i never mean my words, kin ban haushi ne shiyasa am sorry,taya ma kike tunanin Zan iya rayuwa babu ke acikin?? Ki yafe min kinji" yafada yana girgiza hannunta jin bata juyo bah

"It's okay" tafada still bata juya bah

"If you know it's okay pls atleast look at me and smile" daman kuma abinda take jira kenan, ahankali tajuyo sannan ta mishi murmushi

"Wow pretty, one hug for this" yafada batareda tunanin komai bah ta rungumeshi, kankameta yayi Yan mai sauke ajiyar zuciya, breaking hug din tayi sannan tamishi Saida safe

"Baza'ayi haka bah barina rakaki"

"Ok"sannan suka fita

Bangaren Nadhira tana fita daga motan tayi hanyar baya, mika mata abu akayi acikin.....

*Vote,*
*Comment&*
*Share*

*💋💋 wurarh💋💋*
💝💝💝💝💝
*ABAR SO*
💝💝💝💝💝

*WRITTEN BY: NAFISAT MA'ARUF SHEHU*

WATTPAD: MHIZZPHYDO
🌟GEORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F🌟

HOME OF GORGEOUS INTELLIGENTAND EXPERT WRITERS, WE ARE THE BEST AMONG THE REST

*Page 91-92*

Bangaren Nadhira tana fita daga motan tayi hanyar baya, mika mata abu akayi acikin bakin leda sannan tamusu godiya kafinnan tashige gidansu Hasana. Tana shigewa toilet yin Alwala Hasana tashigo

"Kice mai yaje yayi Sallah"

"Toh Tasallah"

"Whatever lover girl" dariya kawai Hasana tayi sannan taje ta fada mai. Tana idar da sallah tamawa ummi sallama akan zata tafi gidan big dady , Addua ummi tamata sannan tafice daidai nan kuma yadawo daga masallaci,rungumeta Hasana tayi

"Take care and don't do anything foolish over there,and be a good girl cos matar gidan bata da matsala and am very sure heart naki zaiyi melting because of her behaviors"

"InshaAllah Hasynah amma batun heart dina zaiyi melting bai taso bah"

"We shall see to it then"

"Whatever" sannan tashige cikin mota,shidai bai gane akan me suke magana akai bah

"Darling bae saina zo hira koh??" Yatambaye ta

"Yauwa sweetest boo saika zo" tabashi amsa

"Ohk bye and take care of yourself"

"I will and you also"

"InshaAllah" yafada sannan tashige mota,sanda tadaina ganin motan tashige cikin gida.

Suna Isa kofar gidan taji wani sanyin dadi naziyartar ta ahankali ta furta

"Yar'uwarta nakusa cika miki Alkawarin dana dauka miki"

"Ya kikayi shiru kuma matar yaya??" Abdul ya katse ta da tambaya

"Nothing much wlhy" ta bashi amsa tareda bude kofar motan sannan ta wuce wurin booth,b babu bata lokaci ta fito da trolley dinta sannan tamai Sai anjima kafinnan ta yi wajen gate din tareda kwankwasa wa , alokacin kuma har ya bawa motan Wuta yayi gaba abinshi.

"Ina wuni baba" tagaisar da baba mai gadi

"Lfy yen nan,daman kuna nan?"yatambaye ta cikeda mamaki

"Erh wlhy muna nan"tafada tana kutsawa gaban cikin gate din

"DanAllah baba akwai chemist neh kusa??"

"Eh akwai amma saikin dan fita ta bakin hanya"

"Toh ga kayana nan barina siyo magani nadawo"

"Toh adawo lfy"

"Allah yasa"tafada hade da ficewa, tafiya tadanyi kadan kafin ta iso chemist din babu bata lokaci aka bata abinda take bukata kafinnan ta yi gaba abinta.

"Assalamualaikum"shine abinda wani yafada daidai lokacin daya shigo chemist din

"Wa'alaika Salam" suka amsa mai

"DanAllah ina tambaya neh"

"Allah yasa mun sani"

"DanAllah yarinyar chan data fita miye tasiya neh??"

Sanda suka kalle juna tukunna kafin daya yace

"Oh kana nufin wancan yar hannun kake tambaya??"

"Eh ita dai wanda tabarnan yanzu"

"Dinger tasiya" yafada cikin ko in Kula

"Dinger kuma!!!" Sadiq Ya maimaita cikeda mamaki

"Eh mana ko baka gane bane"

"Nagane, nagode sosai" yafada hade da ficewa har lokacin bai daina mamaki bah, ahankali takarasa wajen motan su sannan yashiga

"What's up dude?? Ina fatan ba ciwo mai tsanani bane yake damunshi??" Amin yatambaya cikeda tsoro , tsaki kawai Sadiq yaja sannan yace

"In fada maka abinda taje siya zaka yarda??"

"Erh mana"

"Dinger taje siya"

"Dinger kuma!!??"yatambaya afirgice

"Kasan miye ake Kira da Dinger kuwa??"yafada har wani zufa ke keto mishi

"Toh da bansaniba ne toh bari na maka dalla dalla, CONDOM tasiya"

"Innalillahi, miye zatayi da Condom kuma??" Yatambayi Sadiq cikeda damuwa

"Waye San mata" Sadiq yabashi amsa

Haka suka bar wajen tareda jimami dakuma tambayoyi aranshi.

"Sannu baba nadawo"

"Yauwa sannu da dawowa" baban yabata amsa sannu takarasa wajen da ta bar trolley dinta sannan tashige cikin gida da sallama sauke abakin ta

"Abin mamaki!!! Waye nake gani kaman enbiyu(haka take kiransu)"

"Nice"

"Ai ba'a fada mana kinji sauki bah(dayake daman basusan tafara magana bah)

"Ai kuwa inaga banyi wata 2 dajin sauki bah"

"Ayyerh Allah yakara sauki"

"Ameen ya Allah"

"Kardai ke Alhaji yace zakizo mana kwana biyu?"

"Eh wlhy "

"Ok sannu da zuwa,bari yaran nan suzo su nu.....

Kuyi manage da wannan babu yawa, naso nayi dayawa amma ban jin dadi sosai.....

*Comment,*
*Vote&*
*Share*

*💋💋 wurarh💋💋*
💝💝💝💝💝
*ABAR SO*
💝💝💝💝💝

*WRITTEN BY: NAFISAT MA'ARUF SHEHU*

WATTPAD: MHIZZPHYDO
🌟GEORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F🌟

HOME OF GORGEOUS INTELLIGENTAND EXPERT WRITERS, WE ARE THE BEST AMONG THE REST

*Dedicated to*
*Hasynah*

*Page 93-94*

*Alhmdllh Hasynah tayi waya,toh Allah yasa ki mora kuma ki kashe lfy, namiki murna besty wannan page din naki ne kedai..."*

"Ok sannu da zuwa,bari yaran nan suzo su nuna miki dakin da zaki zauna"

"Toh mumy" nan mumy ta Kira Maimuna sabuwar yar aikin ta wanda tayi bayan tafiyan Hasana. Nan tafada mata akan tanuna mata dakin da ta gyara dazu..

"Muje" Maimuna ta fada, batareda Nadhira tayi magana bah tabi bayanta...

Hadadiyar daki aka nuna mata amma baikai dakinta na asalin gidansu bah, kasan mattress tadaga sannan tacire ledar da aka bata ta ajiye likewise Condom dinda tasiya chemist,ta ajiyewa tagyara wajen yayi smooth kaman ba'a sa komai bah ,kai tsaye wajen sif din dakin tanufa ahankali take jera kayanta aciki wanda duk cikin kayayyakin babu atamfa ko daya ,tana gamawa tazare towel dinta sannan tashiga toilet da nufin yin wanka.

Daidai ta fito daga wanka Maimuna tayi sallama sannan tashigo sannan tace" wai inji mumy kizo kuyi dinner kuma Alhaji yadawo"

"Ohk kice sallah zanyi sufara ci ,in na idar Zan fito"

"Toh" tafada tana hararan bayan Nadhira cos tinda taganta taji Nadhira bata mara bah

A Palour tasamesu sannan tafada musu aiken Nadhira din. Daidai kowa yazauna a dinning din Nadhira ta fito, comfy sleeping dress ne ajikinta kasancewan ana sanyi agari ga wani shegiyar kamshin dake tashi ajikinta. Kura mata ido sukayi suna kallon ta,cikin tsarguwa da irin kallon da Nadhira ke jefan shi dashi yasashi tashi yanufe ta

"Babynmu ce tagirma haka, lallai kice sauran kawai muji anzo tambayar aurenki" yafada tareda rungumeta ajikinshi, murmushin karfin Hali ta daura a saman fuskarta, rabe runguman tayi tareda shagwabe fuska da fadin

"Haba big dady wani irin za'a zo tambayar aurena bayan ga wa'incan hajiyoyi azaune , su ba'a yi musu aure bah Sai ni??"

"Ai su karatu sukeyi shiyasa" yafada hade da Jan hannunta zuwa dinning table,azuciyarta cewa take

"Wato nine ban karatu soboda banda gata, dan iskan mutum harda goga mun kirji da wayo,wlhy da badan ubanka da ubana daya bane dana auna mai zagi.." zaunar daita akan kujeran dayayi ne yasata dawowa daga tunanin data fada

"Sannunku" tafada batareda ta kalle su Fatiman bah

"Yauwa" suka amsa cikin shan kamshi,cikeda nutsuwa suke cin abinci har suka gama, suna gamawa Maimuna tazo kwashe plates,da gangan ta fadar mata da cup din juice ajikinta

"Wayyo momma!!?"Nadhira tafada da karfi Sai asannan hankalin kowa yadawo kansu dasauri Maimuna take bada hakuri cos bata zaci zata chanchara ihu bah, kallon ta Nadhira takeyi sai alokacin talura ashe da gangan ne cos inba da gangan bah ai tin kafin tayi magana yakamata ta bada hakuri amma saita share

"Wlhy Sai na rama" tafada azuciyar ta

"Miye kike kallo har Kika zuba mata abu baki sani bah" big dady yafada cikin ihu irin alamun ranshi yabacin nan

"It's okay big dady,bada sanninta bane" Nadhira tafada hade da tashi daga kujeran

"I need to use the wash room" yafada hade da barin wajen, dukda tabar wajen big dady bai daina surfa ruwan masifa bah,mumy kam hakuri tadinga bashi while su Fatima sunyi kaman ba'a wajen suke ba.

Maimuna nashigewa kitchen tafara tunanin waye yarinyar da har Alhaji zai dinga mata masifa haka ahankali tafurta"zamu hadu da kaine "(nace towww...)

Kai tsaye toilet tanufa tana mamakin halin Maimuna cos she she sees no reason dazata zuba mata abu ajiki itada yaune kawai zuwanta gidan,dazuma da ta harareta tagani ta mirror,tsaki taja hade da fadin " zakiyi bayani "...

Sanda tasake wanka sannan tafito a palour tasame su ga tea cup agaban big dady,ahankali takai idonta kan agogo taga exact time din Hasana tafada mata ne acikin zuciyarta tace

"Aikin ki yayi kyau Hasynah.." Big Dady neh yakatse ta da fadin

"Karaso mana Babynmu" cikin sanyin jiki taiso wajen su as usual wannan munafikin murmushin na face dinta

"Ahado miki tea neh??"yatambaye ta cikin kullawa

"Munafiki kawai"tafada azuciyar ta while azahiri tace

"A hadomin kuma bayan nasan hanyan kitchen,karka damu daga gobe nizan na hada mana tea din cos na tabbata Zan fita iyawa"

"Ai Dole kifita iyawa ko kin manta da Mommanku ba indiya ce, kuma sune dagin shayi"mumy tafada, dariya sukasa gabadayan su

"Toh indai hakane Babynmu ce zatana mana tea kullum" big dady yafada

"Kai naji dadin wannan contract din"tafada tareda sakin asalin murmushin daya nuna farincikin ta dahakan

"Natafi bacci,mukwana lafiya" tafada hade da barin wajen..

"Toh nima kasameni adaki cos natanadar maka da kayan dadi" mumy tafada tana shafa gefen fuskanshi kaman na karamin yaro(nace su love kenan...),

Shigarta da 30 minutes Maimuna tafito daga daki ta kitchen tanufa ai yana ganinta yabita, daidai tajuyo ta ganshi kawar da kanta tayi tareda turo baki...

Kishin ruwan daya dameta ne yasata fitowa daga dakinta ahankali gudun karta tashi masu bacci , abinda tagani ne yasata mannewa dagaru ahankali tafurta

"Dan Akuya kawai", matsawa tayi domin taga kaman magana sukeyi...

Tsaye yake shida Maimuna yawani rungumeta ita kuma Sai zillewa takeyi alaman bataso chan ta numfasa hade da fadin

"Ni kabarni,bayan kagama min masifa dazu zaka wani zo kana manne min ,baga yarinyar chan ba kaje ka sameta tinda naga dazu har runguman ta kayi"

"Haba Rafin dadi nah yazakice min haka, baby fah yar kanina ne, kuma kema kinsan bazan cuceki bah kuma inason nabaki wani assignment"yafada hade da shafo boobs dinta,itakuwa har wani lumshe ido takeyi alamun nan ne weak point dinta ahankali tace

"Fadi assignment din naji"

"Yauwa Rafin dadi nah daman so nake ki samin Id...


*Comment,*
*Vote&*
*Share*

*💋💋 wurarh💋💋*





💝💝💝💝💝
*ABAR SO*
💝💝💝💝💝

*WRITTEN BY: NAFISAT MA'ARUF SHEHU*

WATTPAD: MHIZZPHYDO
🌟GEORGEOUS WRITERS FORUM🌟

🌟G.W.F🌟

HOME OF GORGEOUS INTELLIGENTAND EXPERT WRITERS, WE ARE THE BEST AMONG THE REST

*Page 95*

"Yauwa Rafin dadi nah daman so nake ki samin Ido akan wannan yarinyar yazamto kowani motsinta akan idonki zai kasance"

Wani irin dariya tayi sannan tace"indai wannan ne karka samu damuwa…"ahankali takoma dakinta batareda ta karasa jin abinda suke fadi bah…

Wata ajiyar zuciya tasauke data shige cikin daki, tunani dayawa neh yake shawagi a brain dinta kafin tasaki wata shegiyar murmushi tana fadin

"Taab lallai kinshirya barin aikinki indai ido zaki samun, ke zanfara kawarwa tukunna…

**********

Amin kam yana komawa gida yashiga matsanancin damuwa, bayani yake bukata gameda condom dinda tasiya…

Tashi yayi yaje palour soboda wani tunanin daya darzu mishi azuciya,yakuwa ci sa'a kowa na wajen…

Sallama yayi cikin nutsuwa inda suka amsa mai hankali su yana mai komawa kanshi…

Gaban Dady yaje ya tsuguna tareda sune kanshi akasa alamun jin kunya,shiru ne ratsa wajen na mintina…

Dady ne yakatse shirun fadin"Da akwai magana abakinka Aminu"

Gyada kanshi kawai yayi still baiyi magana bah

"Kai banson shashanci inbaka da abin fada kayi gaba,kawani zo kasamu agaba kaman wasu yaranka" " mumy tafada ahasale

Cikin nutsuwanshi yace"Ayi hakuri mumy,daman… daman… nace in ba matsala auren…" sai kuma wutanshi ya dauke yana dada sune kai kasa…

Dariya irinta manya dady yayi inda Abba kuma mamakin rashin kunyan Amin yakeyi, antyn ma dariya tayi mumy kuwa kunya taji yakamata…

Dady ne yace"Nagane abinda kakeso, kaje zan neme ka"

Cikin sosa keya yace" Nagode Dady Allah yakara girma"

"Ameen" suka amsa sannan yafita daga palourn

Dady neh yamayarda duban shi zuwaga Abba sannan yayi gyaran murya yace

"Ina fatan kasan inda zancen yaron nan ya dosa??"

"Eh ranka shi dade" Abba yafada cos yana mugun ganin girman dady…

Murmushi dady yayi sannan yace "nalura baka son in cigaba da zama anan gidan fah"

"Na isa??"

"Bagashi kana kirana da ranka shi dade bah bayan ni yakamata nakira ka da ranka shi dade" dady yafada

"Toh nadaina"

"Yanxu yah kke ganin zamuyi??"dady yatambaya

"Ai duk yanda kace haka za'ayi"

"Toh InshaAllah ranar da za'ayi nasu Abdulkadir Sai ahada danasu, Sai afara shirye shirye" Dady yafada…

Wani irin farinciki yakeji acikin ranshi cos tindazu a labe yake ajikin kofa yanajin abinda suke fadi…

***********
*3 days later…*

Yen kwanaki ukun datayi acikin gidan ta kara Lura da abubuwa dayawa acikin gidan,daita ake kowani abinci agidan yanz u inda kuma yanzu Maimuna ce target dinta dan haka yau tayi niyyar fara aiwatar da kudurinta akan Maimuna din.

Maimuna mah bata fasa bibiyarta bah cos itama kowani motsin Nadhira akan idonta yake amma har yanzu bata samo komai gameda ita bah,

Data fadawa Big Dady Sai yace kawai su shareta , yanxu dai zance Maimuna ta share batun sawa Nadhira ido…

Tindazu take kitchen tana taya Maimuna aiyuka inda Maimuna ta Lura Maimuna ta fiye shan coke,abu kadan Sai adan kurbi coke dinnan,

Fakan idon Maimuna tayi tazuba mata codeine acikin coke dinta ,inda tsantsan mugunta irin na Nadhira babban kwalba tazuba mata aciki, su Maimuna kam banda waka babu abinda takeyi, kuma dayake tabawa coke din baya amma tsantsan rashin Kula irin na Maimuna ko jijigawan datake yi bata ji bah,

"Nikam Maimuna wannan coke din daya rage dinnan zaki iya shan duka alokaci daya"Nadhira tafada tana nuna coke dinda ko rabi bai kawo bah,

Sanda Maimuna tayi wani irin dariya kafin tace" ke bakisan nayi course a iya shan coke bah??"

"Toh taya za'ayi nasani inba gwada min kikayi bah??"

"Tsaya kisha mamaki" Maimuna tafada tana kafa goran abakin ta , tsantsan hadama ko irin kwarewan nan batayi bah,gyatsan da Maimuna tayi bayan ta ajiye gora neh ya katse mata mamakin ta.

"Ya Kika gani??"tafada tana dage mata gira

Dariyan jin dadi Nadhira tayi sannan tace " wlhy nadauka bazaki iya bah, barina dauko miki nawa kisake sha mugani"

Dadi kaman ya kashe Maimuna cos daman kullum guda biyu take sha arana amma gashi yau garabasa tasamu zatasha guda 3,

Fita Nadhira tayi straight dakinta ta nufa sanda taboye kwalban codeine dinda ta juye mata dafarko abayan gado sannan tasake fitowa dawani again sanda tadan zubar da kadan kafin tasake zubawa aciki(nace kaii Nadhira ke muguwar karshe ceh…) sanda Tajijiga dakyau sannan tayi takoma wajen uwar kwadayi

"Gashi harna bude miki"tafada tareda mika mata,karba tayi sannan tace

"Kin kyauta wlhy" aranta kuwa fadi take ashe

9 / 11