Author : Sumayya Abdulkadir (Takori Kabara) Category : Romantic Hausa Novels
kukanta
kamar
farkon
zuwansu
nan da
zaka
ga in ta
fara
itama
uwar
sai
ta
dinga
tayata
suyi
ta
yi
”.
Femi
dake
gefe
yana
aikinsa
cikin
wasu
files, amma
kunnensa
na
tare
dasu
, nan
ya
sako
musu
baki
da
cewa
.
“Kun
san
me? Ni
kuma
burgeni
sukayi
,
na
yaba
kwarai
da
nutsuwar
uwar
,
kalleta
a
nitsenta
tsaf
,
kamar
ba
wadda
ke
cikin
walagigin
rayuwa
ba
.
Kalli yadda ta
nutsu
tana
baiwa
rigimammiyar
‘
yarta
baki
cikin
lalama
,
kulawa
,
tausasawa
da
juriyar
uwa
akan
rigimar
dan ta.
Duk da ban
jin
yaren
da
takeyi
, amma
na
karanceta
akwai
nutsuwa
da
addini
kwarai
,
sannan
da
tawakkalin
zaman
wajennan
tattare
da
ita
.
Sannan
kaga
bata je tana
kokawa
da
maza
don
amsar
tallafi
ba
(yadda
matan
wurinnan
keyi
),
duk
da ‘I am quite sure’
su
basu
samu
komai
ba
,
ba
kuma
zasu
samu
din
ba
”.
Gabadaya
surutansu
daga
Femi din
har
Haladu
ya
fara
hawa
masa kai, bai
cika
son
ayi
ta
maganar
mutum
a bayan
idonsa
yana
zaune
yana
ji
ba
.
Sai
kawai
ya
rufe
system din
gabansa
ji
kake
bam!,
ba
kuma
tareda
ya
tsaya
kasheta
ba
,
sannan
ya
mike
cikin
nutsuwa
ya
saka
takalmansa
ya
bar
musu
wajen
,
uffan
bai
ce
ba
.
**** **** ****
Koda
ya
koma
hotel
dinsu
yau
,
sai
da
yayi
waya
da
Ammih
yaji
lafiyarta
,
ya
tambayi
Abbih
tace
yana
office bai
dawo
ba
tukunna
, ta
tambayeshi
komai
lafiya
ince
ko?
sabida
a
cewarta
taji
muryarsa
wani
iri
kamar
yana
cikin
damuwa
. “I hope ka ci
abincin
rana
dana dare Ibny?”
Murmushi
Yassar
yayi
,
cike
da
kaunar
mahaifiyarsa
,
yace
“
komai
lafiya
Ammih
sai
kewarki
,
bana
cin
abinci
da rana,
saboda
a
lokacin
ina
aiki
acan
Anka,
sai
na
dawo
hotel
nake
saka
order a
kawomin
dan ‘light dinner’.
Amma
kwarai
kullum
da safe
ina
yin
kyakkyawan
breakfast
mai
nauyi
kafin
na
fita
.
Litinin
,
Alhamis
da Jumaah
kuma
kinsan
azumi
nake
”.
Yassar
ya
dan
nisa
,
cikin
nauyin
baki
dana
zuciya
,
shi
ya
san
baya
iya
boyewa
Ammih
komai
nasa
, ko
abinda
ke
damunsa
komai
kankantarsa
, amma
yau
ya
kasa
gaya
mata
abinda
ya
gani
ya
dameshi
,
ya
wuni
surr
! Yana
tunawa
,
suna
raunana
ilahirin
kuzarin
jikinsa
. Wadannan
idanun
…
wadannan
jajayen
jikakkun
idanun
masu
kama
da
shatin
kwan
zabo
…
wadannan
idanun
sun
kassara
shi
. Da
Ammih
ta
matsa
da son
jin
dalilin
sauyawar
muryarsa
sai
yace
.
“
Ammih
yau
din
kawai
ji
nake
jikina
da
zuciyata
suna
wani
irin
sauyawa
.
Tamkar
wanda
measles
ke
shigarsa
. Ji
na
nake
kamar
ba
ni
ba
,
kamar
sabon
ni
(new me),
wato
kamar
an sake
haifoni
duniya
.
Ammih
yau
gabadaya
na
manta
duk
wani
tension
dina
”.
Ammih
tace
“
toh
fa! Idan
kaji
irin
haka
toh
sauyin
alkhairi
ne
ke
tunkaroka
.
Yawaita
karanta
‘
hasbunallahu
waniimal
wakeel”.
Yassar
yace
“
toh
Ammih
. Bari in
yi
waya
a
kawomin
abincin
kafin
nayi
wanka
,
dawowata
hotel
kenan
daga
can Anka”.
Sannan ne
sukayi
sallama
ya
shiga
wankan
da tun
dazu
yake
son
shiga
sakamakon
zafin
Zamfara
dake
uzzura
masa.
Yassar
na
cikin
wanka
a
tsakiyar
shower,
yayinda
ruwa
mai
dumi
ke
bi ta saman
sumar
kansa
,
jajayen
matan
, (ta
bakin
Haladu)
suka
sake fado masa a rai.
Yana
wanka
yana
tunanin
fuskokin
Uwa da ‘yar.
Gasunan
kamar
an
tsaga
kara,
saboda
tsabar
kamanninsu
da
juna
.
Surar
yarinyar
da
mahaifiyarta
ta
kira
da
suna
KELTOUMA
ke
sake
gilma
masa,
kamar
yadda
ruwan
ke
bi
yana
wanke
sumar
kansa
haka
yake
jin
yana
wanke
masa
kwakwalwa
yana
zuba
masa
sabon
vibe
na
rayuwa
wanda
a baya bai
taba
experiencing
ba
,
Keltouma
ga
haiba
ga
kyau
kamar
balarabiyar
Hijaz,
sannan
ga kamala a
kan
fukokinsu
duka
,
mai
nuni
da
cewa
su
din
ba
mutanen
banza
bane
ba
kuma
wulakantattu
ba
,
kaddarar
rayuwa
ce
ta
tafi
karfinsu
ta
yi
sanadin
shigo
dasu
IDP Camp.
At the same time
yana
tuna
annakiyar
dattinsu
(
dauda
) data
samu
muhallin
zama
a
farar
fatar
jikinsu
da
atamfar
jikinsu
, da
kwantacciyar
damuwa
mara
misaltuwa
dake
kwance
a saman
kyawawan
fuskokinsu
.
Sunan da bai
taba
jin
mai
irinsa
ba
,
ya
sake
yi
masa
dirar
mikiya
hadi
da
amsa-kuwwa
cikin
kunnuwansa
; “KELTOUMAH!
**** **** *****
Daidai
lokacin
da
ya
fito
wankan
,
hatta
jijiyoyin
jikinsa
jinsu
yake
ba’a
yadda
ya
saba
jinsu
ba
, sun
yi
relaxing
sosai
.
Fatarsa
tayi
sumul
da
wankin
data sha,
jikinsa
yayi
tas
,
ya
kara yin fresh,
sai
sheki
fatarsa
keyi
kamar
koyaushe
ya
fito
wanka
, a
hannunsa
karamin
farin
tawul
ne,
yayinda
yake
daure
da
faffadan
a
kugunsa
,
yana
tsane
kansa
da
tawul
din
yana
kallon
agogo
duka
a
lokaci
guda
. Sai ga
kiran
Abbih
ma
ya
shigo
masa.
Daidai da
zuwan
mai
kawo
masa
abinci
a
bakin
kofa
,
shi
kuma
yana
kwankwasawa
.
Yassar
ya
fara
da
amsa
kiran
wayar
mahaifinsa
tukunna
, da
matukar
ladabi
irin
nasa
ga
Abbih
kamar
yana
gabansa
,
sannan
ya
nufi
kofar
ya
bude
aka
shigo
masa da
abincin
,
kamar
yadda
ya
saba
gaida
Abbih
yau
ma
saida
ya
rankwafa
kamar
Abbih
na
wurin
,
yace
cikin
damuwa
,
“
Abbih
save this date for me
kaima
a DIARY
dinka
…. 1/09”.
Abbih
yace
“me
ya
faru
a
yau
1/09?”
Nan
yake
labartawa
Abbih
, “
jikina
ne
yake
ta
karbar
wani
sabon
sauyi
,
yana
kaiwa
zuciyata
ita
kuma
tana
karba
,
wanda
yake
bani
tabbacin
rayuwata
zata
canza
salo
da
taku
daga
yau
”.
Abbih
yayi
murmushi
kafin
yace
“
ina
yiwa
rayuwar
nan ta
tilon
Da
na
Muhammad Yassar
fatan
nasara
, da
cikar
kamalarsa
cikin
dan
lokaci
,
addu’ata
shine
yayi
AURE
kafin
zagayowar
ranar
1/09”.
Yassar
yayi
‘yar
dariyar
maganar
Abbih
yace
.
“
Abbih
nah
kenan
!”.
Nan
ya
shiga
labartawa
Abbih
yadda
ya
samu
dangi
a
zuwansa
Sokoto da
wajen
Baba Ado a Tambuwal.
Sai
Abbih
yace
“
ina
fatan
kaga
‘
yan
uwanka
mata
na
wajen
Yaya
babba
?” Yassar
yace
“eh
na
gansu
Abbih
” “
sai
Abbih
yace
“
duk
sun
girma
ko?” (‘
Ya’yan
Alhaji Abdulqadir Abbih
ke
nufi
). Yassar
abun
ya
bashi
dariya
yace
“
su
wa
kenan
Abbih
?”
Abbih
yace
“Sahlah da
Shafa’atu
mana?” Yassar
yace
“Toh
Abbih
ni
ina
idona
ya
kai
kan
girmansu
, sun
dai
gaisheni
na
amsa
,
na
basu
tsarabarsu
”.
Abbih
yace
“
dadina
da kai
rashin
iya
mu’amalla
da
kanne
, ai
wato
girman
yaran
nan
harda
na
ban
tsoro
,
kamar
masu
cin
dusar
kajin
Agric”.
(Girman
jikin
Yaya Babba
duk
‘
ya’yansa
suke
debowa
,
sai
ka
gansu
kamar
sun fi
shekarunsu
mazansu
da
matansu
).
Yassar
cikin
subutar
baki
yace
“
musamman
wannan
Sahlar
”.
Sai
Abbih
ya
samu
gangara
,
ya
kada
kai
ya
hau
cewa
.
“Awo
wollah
. Kaga da kai
wani
dan
kirki
ne da
zan
iya
ciwa
alwashi
bai
sakani
kaffara
ba
, ai da a
cikinsu
zaka
zabo
mana
daya
,
ayi
‘yar
gida
kowa
ya
huta
,
Tuwo
na
maina
,
dakan
daka
shikar
daka
tankaden
bakin
gado
,
duk
mu
huta
da
tuzurancinka
”.
Zancen
zucin
Abbih
ya
fito
fili
ba
tareda
ya
sani
ba
. Sai ji
yayi
Yassar
yana
dariya
wadda
bata ko kai ga
shiga
cikin
cikinsa
ba
.
Yace
.
“
Abbih
! Sau
nawa
zan
gaya
maka
banida
ra’ayin
auren
zumunci
? Ka manta da
wannan
tunanin
, please
Abbih
nah.
Ni
dukkansu
kannena
nake
ganinsu
,
wadannan
yaran
masu
rawar
kan
tsiya
Abbih
masu
kama
da
kajin
gidan
gona
ina
zan
kaisu
ribda-ribda
dasu
haka?
Sannan
kaga
raini
zai
gitta
tsakanina
dasu
,
raini
irinna
‘
yammatan
family ga
yayyensu
maza
,
wanda
ke
zuwa
sanadin
auren
zumunci
.
Saboda
duk
girman
nan da
suke
bani
zubewa
kasa
zaiyi
warwas
Abbih
.
Muddin
suka
ji
irin
maganar
nan da
kake
yi
akaina
dasu
. Please
Abbih
! Idan
kanada
wannan
burinma
ina
rokonka
ka
cireshi
a