Author : AYSHERCOOL Category : Arewa Story
da take da ƙarancin ni'ima a jikinta? Ina wadda take jin zafi a wurin saduwa? Hajiya kin taɓa amfani da maganin da zai matse ki ya mayar dake tamkar buduwa? Ko har yanzu kina nan a buɗe kamar bakin gari? To muna masu farin cikin sanar daku mun zo muku da ingantattun magungunan gyaran jiki na mata masu kyau da inganci kamar su..
Gumbar madara
Gumbar mata
Gumbar aya
Gumbar chaku
Gumbar dake saukar da ni'ima
Gumabar taƙadari
Gumbar riɗi
Gumbar dabino
Gumbar uku alkhairi
Kazar amare
Jijjiɓen saniya
Tabaje
Tsimi
Rikita mai gida
Jigidar tada sha'awa
Ruwan boom ruwan daɗi kenan
Ɗan matse
Karya gado
Maganin sanyi
Zumar ƙarin ni'ima
Zumar rage ƙiba
Zumar ƙarin ƙiba
Zumar riɗi
Mai zamani
Emergency powder
Tarhama
Kafi budurwa
Sabon budurci
Alfijir
Gamzaki
Garin dahuwar nama
Sabaya
Miskin ɗahara
Da dai sauran su. Namu ba irin na su bane, bamu fito ba sai da muka shirya, muka tabbatar da kwaliti da inganci kayanmu. Ƴar uwa gyara shi ne mace, aka ce ko kina da kyau ki ƙara da wanka, ina matan dake cewa ba sa shan kayan mata iya fruit kawai suke sha? To ku sani ko wane allazi da amanun sa, aikin fruit daban, aikin waƴan nan daban. Hajiyata ki saki jiki kawai ki zo musa labule, a gwangwaje ki da kayan da zaki rikita my house da su. Ki susuta shi, ya zamana duk inda yake kina maƙale a cikin ƙalbinsa. Matuƙar kika yi amfani da kayanmu, ina mai tabbatar miki da ba boka, ba malam za ki mallaki mijinki ciki ruwan sanyi, sai yadda kika yi da shi. Ga mai buƙatar kayanmu zai iya tuntuɓar waƴan nan lambobin 08163516796 ko 08081012143 muna aika saƙon mu a ko'ina.
https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g
SARA DA SASSAƘA
YOTA 002
P5
A tsorace Ya yi turus yana kallonsa, jikinsa a sanyaye yana jiran cin mutuncin da Isma'il zai yi masa a wannan karon.
Sai dai ga mamakinsa bai yi masa magana ba, ya raɓa shi ya wuce. Wata irin ajiyar zuciya ya sauke, ya juya ya tafi.
"Alina" ya shiga gida yana ƙwala mata kira.
"Na'am" Ta yi maganar tana fitowa daga ɗaki.
"Me ya haɗa ki da mutumin nan?"
A shagwaɓe ta ce "Yaya har ka bani tsoro, na dawo daga gidan su Hafsa, aka ɗauke wuta a hanya, shi ne ya haska mini fitila"
"Gidan su Hafsan ne ki ka je ki ka yi zamanki har isha'i ko Alina? Wallahi da na san ba ki dawo ba, har gidan su Hafsan zan je na same ki, na zane ki tun daga can mara ji kawai"
Ta risunar da kai ta ce "Ka yi haƙuri dan Allah"
"Ni ƙyale ni, sai kin yi laifi ki wani kwantar da kai kina a yi haƙuri kamar kyanwa"
Ta yi shiru tana sunkuyar da kai. A gida ya yi sallar isha'i, sannan Nadiya ta zuba masa Abinci.
Ganin yana jin haushinta, ya sanya Alina ba ta yi masa surutu ba kamar yadda ta saba, ta ja bakinta ta yi shiru.
Can Alina ta ce "Antynmu ni ko na tambaye ki mana"
"To tambai, me za ki tambaya?"
Alina ta karkace ta ce "Anty wai dan Allah ku na faɗa da ke da Yaya?"
Nadiya ta ce "Ai ga yayan naki a nan tambaye shi mana" Alina ta noƙe kafaɗa.
Nadiya ta yi dariya ta ce "Meyasa ki ka tambaye ni?"
"Hafsa ce take cewa babansu na zagin mamansu. Ya ce aure zai yi wa Hafsa da ta yi candy, shi ne ta ce ba ta son ta yi aure, mijinta ita ma ya din ga zaginta"
Nadiya ta numfasa ta ce "Duk yadda muke sonki ba kya laifi mu yi miki faɗa?" alina ta jinjina kai.
"To babu zamantakewar da babu saɓani, amma fahimtar juna ke kawo zaman lafiya. Ni da yayanki...
Yaya ya katse su a fusace "Shiyasa ba na son yawace-yawacen nan, a can ake gurɓata miki tunani. Babu wani mijin kirki da yake zagin matarsa. Ni kin taɓa ganin na zagi Masoyiyya?" Alina ta girgiza kai.
"Amma idan ta yi laifi, ina yi mata faɗa, shi ma ba kullum nake yi nata a gabanki ba, haka mijin arziki yake. Dan haka baban ƙawarki mahaukaci ne"
Nadiya ta ce "Subhanallah baban ƙawarta ne fa"
"To babanta ne? Mahaukaci ne mana, banda mahaukaci ya za a yi yaranka su san kana zagin babarsu a gabansu dan hauka. Ke tashi ki tafi ki je ki kwanta. Kema tashi mu tafi" Alina ta tashi sumi-sumi ta tafi ɗakinta.
Ko da suka shiga ɗaki Nadiya ta ce "Yaya
Masoyi, ka din ga gaya wa Alina gaskiya fa. Idan mu soyayya muka saka a gaba lallai ne ta samu miji irirnka".
Ya haye kan gado yana faɗin "Na raini yarinyar na aura maka, ka zagar mini ita, da kuwa na fasa wa mutum baki wallahi. Balle a ce duka sai na kusa binne mutum da ransa ba"
Ta tuntsire da dariya ta ce "Allah mai 'ya"
Ya ce "Sa wasa, ai yau ko da wani aka kama Alina, gara ya sako mini ita salin alin, a kan ya taɓa lafiyarta ko ya zage ta. A yadda Alina take babu yadda za a yi ta yi wa mutum laifin da zai dake ta ko ya ci mutuncin ta. Babu abin da ya yi mini zafi da laifin da ta yi, na aura wa mutum ita ya wulakanta mini sai ya gwammace mutuwarsa wallahi. Idan ta yi ba daidai ba, gara mutum ya dawo mini da kaya ta ta fasa auren"
Nadiya ta ce "Ohh anya zaka iya aurar da ita kuwa?"
"Eh mana, shiyasa ke ma nake ƙara lallaɓa ki masoyiyya, saboda kar na zaluce ki, wani ya auri ƙanwata ya cutar da ita
Allah ya ba wa Alinana wanda so ta ya kula mini da ita kamar yadda nake sonta. Shiyasa sai na dirje na tantance yadda yakamata zan ba wa mutum" Ya yi maganar yana kwanciya a jikinta. Ta so ta furta abin da ke ranta, amma ta san tana maganar za su yi faɗa, a dole ta haɗiye ta yi shiru ta rungume shi.
****
Yana daga kwance ya dafe kansa, da sallama ta shigo bakinta ɗauke da sallama, ya amsa ba tare da ya ɗago ba.
"Ashe kana nan, ina ƙasa ina ta bulayin neman ka ai"
Ya sauke hannun a hankali ya gyara kwanciyarsa ya ce "Ina nan"
Ta zauna a kusa da shi, ta ce "Ni wai dan Allah ya maganarmu ne?"
"Wacce kenan?"
"A'ah maganar motocina mana, waɗanan fa tsofaffi ne wanda waccan first ladyn ta yi amfani da su ne, a cikin allowances ɗina ka bayar da umarnin a sayo mini sababbi, wannan na rarrabawa mutanen da suka yi mana wahala"
"Dan Allah ni dai a yanzu ki ƙyale ni, mene ne aibun motocin nan, daga zuwanmu sai mu saka wa dukiyar al'umma wawa"
"Haba dan Allah, ba batun saka wawa bane ba, abu ne da yake a rubuce fa, ni dai gaskiya ka yi wani abu a kai, ni wannan motocin sun yi mini tsufa gaskiya"
"Shikenan na ji, zan yi magana da Halilu su duba"
Ta sauke numfashi tana murmushi ta ce "Ko kai fa" Ta tashi ta fice, ya bi ta da kallo, sam ba ta damu da jin damuwarsa ko ƙoƙarin taimaka masa ya sauke hakkin al'umma ba, kawai hanyoyin azurta kanta take nema.
Ya janyo wardrobe ɗin gefen gado, ya ɗaukko waya ɗaya ya gyara kwanciyarsa ya hau internet.
Twitter ya fara shiga ya dudduba gidajen jaridu, da al'amurn siyasar duniya.
Ya gama da twitter ya shiga wani shafin.
Shafinta suka fara hasko masa, fuskarta ɗauke da murmushin da baya gushewa daga fuskarta, a duk lokacin da zai ganta a kan screen ɗin wayarsa.
"Amincin Allah da yardarsa su tabatta a gare ku, ma'abota shafina. Kamar kullum ina miƙa saƙon gaisuwa ta musamman ga Babana na kaina, kuma his excellency mr. President. Eh mana so so ne amma son kai ya fi. Babana ne, ɗan yankina kuma ɗan garinmu. Yau ba labari zan ba ku ba. Har kullum nice taku Baby Laila Umar Faruk. Ku zo mu yi wa mr. President ɗan waken gujjiya. Ya yi abincin dare da shi"
Sai ya shagala a shafin nata, yana kallon yadda take gudanar da aikin ɗan waken komai daidai na talaka, sai dai tana yi tana bayyana ayyukan gwamnatinsa, tare da koɗa shi a cikin videon. Bai san lokacin da ya shagala da kallon matashiyar yarinyar ba, har ya manta da wasu daga cikin damuwoyinsa ba.
A hankali ya furta "Lallai har abada ba a iya biyan masoyi. Wasu ayyukan nasa yadda take zayyano su, ka san ba ƙaramin bincike ta yi ba, kafin ta gano su. Dan wasu ma tun kan ya ci zaɓe. Ya tsinci kansa da shiga shafinta, ya din ga duba videos ɗin ta na baya. Ya kan ganta lokaci zuwa lokaci, amma yau ne ya tsaya sosai yake kallon abubuwan da take yi.
Sai dai tana fuskantar ƙalubalen cin mutunci daga masu bibiyar shafin nata, mussaman waɗanda suke adawa da gwamnatinsa. Sai dai kaf babu wanda take yi wa martani da cin mutunci.
Alarm ɗin wayarsa ya fara ƙara, ƙarfe ɗaya da rabi na dare, ya tashi tsam ya ajiye wayar, ya tafi banɗaki ya yi wanka ya fito ya fice daga ɗakin.
****
Awanni biyu kenan Baffa su na tafiya a mota, a hanyarsa ta dawowa gida daga kai Rahama makaranta. Tun daga ranar farko da ya kai ta makarantar kwana da ƙanan shekaru, duk lokacin da ya kai ta, yana jin babu daɗi a ransa. Amma a wannan karon ba iya kewa ce ke damunsa ba, fargaba ce da ya rasa ta mece ce. Kawai ya din ga maimaita Innalillahi wa Innalillahi raji'un.
Ɓangaren Rahama ma, haka ta din ga jin wannan fargabar da ta kasa tantance dalilin jin hakan, duk da tana cikin farincikin cin jarrabawa da ta yi.
*****
Gaba ɗaya hankalinsa ya tattara a kan matashin, da fuskarsa ke ɗauke da matsananciyar damuwa.
"Majeed, ka nutsu ka yi mini bayani, are you serious wai?"
"Ta yaya zan yi jokes da serious issue like this. Wallahi Alpha da idanuna da kumma kunnuwana. Su Okoro ba su san me aka yi ba. Oga shi ya ce na ba su hanya su wuce, ka ji zuciyata ka ji zafin da zuciyata take yi...
"Shhh ka san me zai faru? Wannan maganar daga ni sai kai, kar ka kuskura ta fita, idan ka bari aka ji maganar nan wallahi kashinka ya bushe"
Majid ya shafi fuskarsa ya ce "Anyway ban gaya wa kowa ba, kai kawai na gayawa in sha Allah ba wanda zan sake gaya wa" Alpha ya daki kafaɗarsa ya ce "Good boy, ka koma office"
Majid ya jinjina kai, ya juya ya fita.
Bayan fitarsa Alpha ya ɗaukko wayarsa, ya daddana, ya kara a kunnensa. Sai dai har wayar ta gama ringing bai ɗaga ba. Ya sake buga wayar ta sake ringing ta gama ba a ɗaga ba. Ya ja guntun tsaki tare da faɗin "Ɗan rainin hankali, babu wanda nake yi wa kira sama da ɗaya idan ba kai ba" Ya yi maganar yana ajiye wayar.
****
Tun da ta fito daga gida yake kallonta, tana tafe tana ta karkaɗe uniform ɗin ta, duk da gugar da su ka sha, da hankicinta a hannu, ta durƙusa ta goge takalmi ta karkaɗe uniform, ta karkaɗe jakarta. Har ta zo tsakiyar layin abin da take ta yi kenan. Sai da ta ɗago suka haɗa ido, sai ta yi murmushi, shi kuma ya sunkuyar da kai, ya ci gaba da kallon Alqur'anin hannunsa. Sai da ta zo inda yake sannan ta risuna ta ce "Ina kwana"
"Lafiya kalau" Ya amsa yana ɗan ɗagowa cikin tsoro, saboda fargabar kar yayanta ya gansu.
Ta sake cewa "An tashi lafiya?"
Sai ya jinjina kai kawai.
"To na gode da haska fitilar jiya da daddare" Sai ya ɗan yi murmushi kawai.
Ita ma murmushin ta yi, ta ce "Da aka ɗauke wutar nan fa tsoro ne ya kama ni, ba na son duhu, ina tsoron duhu kwanan ne na daina kwana da fitila ma"
Ya ɗan kalle ta ya yi murmushi, ƙamshin turaren da take yi, duk ya cika gurin da ƙamshi.
"Na tafi makaranta, idan ka idar ka saka ni a addu'a"
"In sha Allah" Ya furta a hankali yana jinjina kai.
Ta ce "To na gode"
Har za ta tafi ya sake cewa "Ba ki kawo takalmi an wanke ba" Ta kalli ƙafarta ta kalle shi ta ce "Goge shi kawai na yi da duster, ai bai yi datti ba ko?"
"Kawo a saka masa mai" Ya yi maganar yana kallonta. Duk da kwarjinin da yake yi mata sai da ta yi murmushi ta ce "Ai ba ni da kuɗi yau".
"Eh kawo" Ya yi maganar yana fito da kayan gyaran takalminsa.
Ta zauna a dakalin gefensa, ta ciro masa takalman. Ya zauna ya ɗauki takalmin nata tomes, ya fara gogewa.
A zuciyarta take faɗin dama ya cire wannan gashin na fuskarsa sai ya fi kyau.
Ya shammace ta ya ɗago idanunsa, ta yi saurin sunkuyar da kanta, tana goge jakarta. Ya kammala goge mata ya ajiye mata a gabanta. Cikin murmushi ta saka hannu ɗago takalman ta ce "Wow wannan ai sai na gano fuskata a jikin takalmin nan, ya yi kyau sosai ya gogu, na gode sosai Allah ya saka da alkhairi. Ka na bi na bashin wankin takalmin nan" Ta ƙarasa maganar tana ajiye takalmin a ƙasa. Tana kallon yadda yake ta ƙyalli.
Ya jinjina mata kai, ta saka takalman ta tashi ta tafi.
****
Hanne ce take kallon Bukar, ya gyara zamansa ya ce "Hanne, Ramata ce ta ce mini na gaya miki, saƙon nan, cewar abin ɓoye ya kusa fitowa fili, me hakan yake nufi?"
Hanne ta sunkuyar da kanta, hawaye ya fara gangarowa daga idanunta.
"Ki yi mini bayani, me Ramata take nufi da abin da ta faɗa?"
Hanne ta girgiza kai tana sunkuyar da kai.
"Hanne ki yi mini bayani kin san me take nufi"
Ta ɗago fararen idanunta. Hanne baƙa ce mai fashin goshi irin nasa. Ta ce "Yaya mene ne alaƙarka da Rahama ne, har ta yi wannan sakewar da kai, ta baka saƙo ka gaya mini?"
Ya tsuke fuska ya ce "Ina tambayarki kina tambayata?"
Ta ja numfashi ta ce "Ina kyautata zaton alaƙar da ke tsakaninka da Ramata, ita ce ta shiga tsakanina da yayanta. Kaf Yalwa Rahama ba ta da ƙawar da wuce ni, na san halinta ciki da bai, bana raba ɗaya biyu soyayya ku ke yi"
Ba shiri ya gyara zamansa yana waiwaye da fatan babu wanda ya ji abin da ta faɗa, ya yi ƙasa da muryarsa ya dube ta da kyau ya ce "Hanne, kar dai abin da nake tunani ne, dama saboda ke ne aka kashe Iro?" Ta fashe da wani irin matsanancin kuka tana kallonsa.
"Hanne dama saboda haka ne, aka saka miki takunkumi aka hana ki shiga, aka hana ki fita? Innalillahi wa Innalillahi raji'un, wace irin masifa ce wannan?"
Hanne ta haɗa kai da gwiwa tana wani irin kuka, mai tsuma zuciya. Saleh da ke laɓe a jikin taga ya ja da baya yana ƙwafa, ya fice daga gidan.
*****
Dandazon 'yan mata ne, suke ta ɓarkowa daga area classes zuwa hostel ɗinsu, kasancewar an tashi daga ɗaukar darasi.
Sannu a hankali cike da nustuwa take takawa, fuskarta ɗauke da yanayi na gajiya, ko da ta shiga Hostel ɗin su, kai tsaye kwanarsu ta wuce.
Cak ta tsaya tana murmushi, wadda take yi wa murmushin, ita ma ta hau murmushi ta ce "B Yalwa, ina ta addu'a Allah ya sanya kar a yi miki transfer" Ramata ta ƙarasa ta zauna a kusa da ita tana faɗin "Anty Ruƙayyata, dama za ki dawo, na ga sati guda kenan da dawowa amma shiru ba ki dawo ba, har na fid da ran za ki dawo"
Anty Ruƙayya ta ce "Ina can ina ganin Likita ne, ba ni da cikakkiyar lafiya, sai da na gama sannan aka dawo da ni. Wai ƙodata ce ke cikin hatsarin kamuwa da ciwo"
Cikin tausayawa Rahama"Allah sarki, ya jikin naki?"
"Alhamdillah. Na samu sauƙi sosai da sosai"
"Allah ya ƙara afuwa"
Ruƙayya ta ce "Amin, su Rahama an shiga Ss1 ina fatan komai normal?"
Rahama ta jinjina kai tana murmushi. "To Alhamdillah, duk da ba na jinki, ƙwaruwa ce ke, amma duk abin da ba ki gane ba, ki yi mini magana Rahama, iya wuya sonake muƙamin headgirl ko health prefect kar ya bar kwanar nan tamu mai albarka, dan haka za mu ƙara zage damtse a kan karatu"
"To iyayen son zuciya, wallahi kuwa sai ya bari, ko ba kwa so" Cewar ta gefen gadon Ruƙayya, da take class mate ɗin Ruƙayya.
Ruƙayya ta ce "Ƙwalli ki kiyaye ni, so so ne amma son Kai ya fi ehe, an san yan kwanarmu dai akwai kai"
Rahama dai murmushi kawai take yi, ba za ta taɓa mantawa da Ruƙayya ba, lokacin da aka kawo ta, ga ƙuruciya, ga ƙauyanci, kusan ma ƙyamarta ake yi. Ruƙayya ce take yi mata komai, dan haka akwai shaƙuwa sosai a tsakanin su, yanzu Ruƙayya na ss3 Rahama kuma ss1 wanda suka yi candy head girl da health prefect 'yan kwanarsu ne, Ruƙayya aka bawa riƙon ƙwaryar head girl. Ta kuma bawa Rahama gudunmawa sosai a wajen karatu.
Kamar kullum bayan dawowa daga pref, sai da Ruƙayya ta tara 'yan kwanarta su Rahama, suka yi karatu, sannan suka hau gado domin su kwanta
A kan gadon ma, Rahama addu'oin kwanciya bacci ta yi, ta ɗan sake buɗe litattafanta tana karantawa, bacci ya yi awon gaba da ita.
Misalin ƙarfe uku saura, Ruƙayya na gadon ƙasa tana karatu ita ma, kawai ta ga Rahama ta diro daga saman gado, a gigice za ta yi waje. Da sauri ta fito daga net, ta riƙo Rahama.
"Rahama lafiya kuwa?" Gaba ɗaya bata cikin nutsuwarta, kamar wadda hankalinta zai gushe. Ruƙayya ta sake cewa "Rahama lafiya kuwa?...
"Hayaniya na ji ne"
"Wace irin hayaniya kuma? Mafarki ki ke yi, amma ba wata hayaniya" Da kyar ta lallaɓa Rahama ta koma kan gadonta ta kwanta, amma zuciyarta na ci gaba da bugawa, saboda ita dai kamar a zahiri ta ji hayaniyar mutane.
Sai dai kwanciyar tata babu wuya, ta tafi mafarkin abin ƙaunarta da bai san tana yi ba. Mutumin da ba ya shafe sati bai zo a mafarkinta ba. Wasu lokutan yanayin mafarkin har kunya yake saka ta.
*****
Tun da Alina taje makaranta, take kaffa-kaffa da takalmin nan, take goge shi, gani take idan ta bari ya yi ƙura bata kyauta ba, saboda yadda ya dage ya goge mata shi ya saka mata mai, ba tare da ta bayar da ko sisi ba
*****
Cikin girmamawa yake kallon ubangidansa, ya risunar da kansa yana ɗaga masa babban yatsansa alamar jinjina ya ce "Kacalla mai