Da So Kamane Complete Hausa Novel By Nana Maryama.docx

Author :  Nana Maryama Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   13 / 111

36K to 39K   out of 332K words

sha magani,shiru tayi kamar bata ji shi ba, bai sake maimaitawa ba sai ruwa daya fito ya dauko mata a kitchen, yace take “sai sannan ta tashi ahankali tana rike duvet din ala dole kar ya ganta da towel da hijab yarda take shan magani kadai zai nuna maka irin rashin kaunar dake tsakaninta da magani, saida tasha kowane kafin ya kwashe ya mayar a leda, kallonta yake can yace wear up your cloth akwai sanyin, kamar zatayi kuka ta saukar da kanta kasa tace babu “sai kuma tayi shiru shi fa har mamaki take basa komai na kuka ne wai “bai fahimce abunda take fada ba hakan yasa shi cewa babu mi? Tace kayan, bai sake ce mata komai ba itama bata sake magana ba, sai bude bag dinta dayayi ya fiddo dayan rigan atamphar da ummi ta bata da kallabi , abayar da take nan wajan katifar da veil din daukar abayar yayi dawani irin speed ta sa hannu ta dauke brassiere dake nan kasan rigan ,ta boye yaga abunda tayi tsaf Ko kallonta baiyi ba yashiga bathroom din dakin sai da yabi manyan pants din ta da kallo yayi saurin dauke kai pampo yabude ya tari ruwa a bucket ya yazuba detergent kadan yasaka sabulu yafara wanke mata kayan, saidai ya wanke su tass ko kadan babu dirty a kayan sai kamshinta daya adabe masa rayuwa kamar time din tafesa perfume din .fitowa yayi rike da bucket din daya dauraye kayan a hannu, Ko kallonshi batayi ba ta dauke kai shima bai ce mata komai ba yayi ficewar sa. Ramlah na tsaye a ventilation dinsu wanda yake opposite da part din su malik din wayarta a saman building din daya zagaye part din normal android ce ta yayi,wanda cikin samarinta irinta ya siya mata,tiktok take tana wani karya jiki kamar wata macijiya, ganin yafito tayi maza ta bi bayansa “cikin kissa tace barka da yammaci yallabai ina wuni “iya saman lips ya amsata yayi gaba idan Doctor ibrahim ya nuna masa ta bayan parts dinsu dake zagaye anan ke da igiya daure ya shanya mata kayan ko wane part haka yake da igiyarsu. Warming miyar yayi ya rufe, wayarsa tayi ringing yana dubawa yaga dr ibrahim ne ,gaisawa sukayi yace hala madam dince tahana ka fitowa dariya malik yayi yace karka jawa yarinya sharri babu ruwanta gajiya ne kawai ke damuna dr ibrahim yayi kasa da yace kaidai kasa hakuri zakayi ta warke shiyasa kake ta dakon ta, murmushi malik yayi yace idan ma hakan ne ai ba laifi bane, dr ibrahim yace kwarai dagaske amma dai a dinga jin tsoron Allah ana tausayi, malik bai ce Komai ba sai cewa yayi kaji dashi dai, dr ibrahim yace tau na biyo maka zakaje kallon ball din ko kuwa? Malik yayi shiru sai can kuma yace aaa gaskia sai mai jikin ta karasa warwarewa zuwa next week sai na dinga bin gwaraye yawon dare, dr ibrahim daga can ya rike baki yace naji magana saukin ma dai nima bai fi two months ba,dariya malik yayi sukayi

sallama.ko daya dawo daga salar isha backyard din ya zagaya domin kwaso shanyar yasan zuwa yanzu sun bushe ga kuma alamar tasowar hadari domin har walkiya akeyi tun dasuka zo gidan akwai nepa ko sau daya bata kifta ba daman dr ibrahim yagaya masa anguwar bakasa fai ake dauke nepa ba, Ahankali ta sake curtain din window this Time bai dauke idonshi ba akanta maganar dr ibrahim yadawo masa a rai dayace masa wai suna kama da ita kallonta yakeyi sosai shidai baiga kaman ba maybe ko dan itama tana da manyan ido ne oho ganin kallon dayake mata duk sai taji bata sake ba towel din daure yake a kirjinta sai hijabin da ta dauko waccan doguwar har kasa gani take kamar yasan babu bra a jikinta, kayan hannunsa yabuda wardrobe din yasaka mata tareda jikkar ta baki daya , har yakai kofa ya juyo yace mata ki saka rigan bara na kawo maki abinci, harara taraka bayansa dashi ahankali taja karamin tsaki tace who’s

he? Sai wani jin kansa yake.

Sharp sharp tabude wardrobe din ta dauko abayar daya wanke mata tass tasaka ta maida hijab din, saida ya dan bata lokaci kafin yadawo dakin saboda yabata daman shiryawa “ko daya shigo zaune ya iske ta saman katifa ta jinginar da Bayanta a pillow bai ce mata komai ba ya aje abinci ya juya ya fita “ bin plate din ta dinga yi da kallo same abincin daya kawo mata da rana ne ya sake kawo mata yanzu, ahankali ta dauki plate din tafara cin abincin kaman tana taunar magani bata ci wani dayawa ba ta ture ta sha ruwa, bacci ne sosai a idonta baccin da ta mance when last tayi sa “ Ahankali ta zame ta kwanta tana rufe idonta. Har sai da gari yayi haske kafin yashigo daga sallar asuba, babu motsin kowa a gidan” bude kofar yayi ya shiga, har yanzu akwai wuta tun jiyan basu dauke ba “har yakai hannu zai bude kofar bedroom din ta sai kuma yafasa ya koma nan parlor inda yasa bargo ya kwanta sai da gari yayi haske sosai kafin ya tashi “toilet din nan parlor ya shiga duk irin sanyi dake akwai na damuna bai dame sa ba ahaka yayi wanka da ruwan sanyi yafito kayan jikinsa ya maida kafin ya bude kofar bedroom din without making any sound har ya bude wardrobe inda yasa jikkar shi ya fido black jeans ne da T shirt itama black yafido Vaseline da perfume din sa ya dauko sai comb fita yayi ya koma parlor tsaf ya shirya yayi matukar kyau, “ kitchen ya shiga ya kunna gas ya daura mata ruwan zafi, tunanin abunda zasuyi break dashi yake hakan yasa shi yanke shawaran fita shagon daya gani ya siyo musu indomie.indomie yasiyo manya kwara uku da yellow label sai sugar,masu cefanan daya gani ya tsaya wajan su yasiyo vegetables da pepper sai kifi wanda aka gasa, zuwa yanzu mutane duk sun fito masu hadahadar tafiya office,nayi masu tafiya kasuwa da masana’antu nayi tun zuwan shi garin ya fahimce kowa anan din ta kansa yakeyi,daidai kofar shiga gidan ya hadu da daya daga cikin yan gidan namiji tun zuwansa gidan bai ga namiji ko daya ba sai yanzu “mutunmin ya washe baki ya tsaya yana kallon malik,hannu malik ya basa suka gaisa “mutunmin yace Allah sarki malan ashe kai ne wanda kuka tare inda dakta ya tashi,malik yace eh nine,mutunmin yace tau ni sunana malan sabo nima anan nake zaune da iyalina mata ta daya sai yaranmu biyu duk kananane,Kamar yarda kagani gidaje hudu ne anan din kowa da matarsa yake zaune dayan ba mazauni bane matar shi daya da yarinyarsu daya Ramlah mutunmin kirki ne kwarai dagaske saidai kash “wllh bai yi saar mata ba da diya abar dai kaza cikin gashinta, dayan kuma sabon aure ne Auwalu ko wata ba a cika ba shagon siyar da kayan shafe shafe garesa na mata a kwari, malik dai surutun malan sabo ya ishe sa,murmushi yayi yace Allah sarki daga haka malik yayi

masa sallama ya wuce ciki.karshe ya kai wutan gas din hakan yasa akayi daidai toni sanda yashigo ruwan na tafasa yau ma kamar jiya a bucket ya juye mata ya kai mata bathroom din already towel din daya fiddo mata yana nan rataye a kofar toilet din Sai da yasa detergents ya wanke toilet din kal duk da babu dirty ko kadan a toilet din “duk motsin da yake tana jinsa amma ko da wasa bata motsa ba har yagama yafita, kusan 5 minutes kafin ta tashi ta sawa kofar dakin key ta cire kayanta ta daura towel din tashiga bayin kusan 20mins ta bata kafin ta fito toilet din ba karamin kyau raman datayi yayi mata ba, Zama tayi gefen katifar sanyi take ji kadan kadan stain kadan tagani jikin pad dinta a pant din ma babu” shiryawa tayi tasaka rigan atamphar daura kallabin tayi simple style tayi wani irin kyau,bata saka brassiere ba amma zaka iya rantsewa da Allah akwai bra a jikinta saboda yarda breastcuff din ya zauna mata dass a jikinta, toilet din ta koma ta wanke bra din ta data shanya tass tayi hanging dinta a inda tayi hanging pants dinta, sun bushe hakan yasa ta kwaso su ta bude wardrobe din ta saka a ciki kallon bag dinsa dayasa a dayan gidan wardrobe din tayi ta dauke kai tana sakin karamin tsaki, Alhamdulilah yau tanajin saukin jikinta sosai babu abunda ke mata ciwo kawai dai har yanzu abun na mata yawo a kai yana kuma yi mata ciwo a zuciya, komawa tayi ta zauna kan katifar ta zubawa waje daya ido, duk wani abu nata mai muhimmanci shikenan fa yanzu?tambayar data samu kanta dayi ma kanta kenan sai ga kwala ya cika mata ido tayi maza ta goge kamar mai tsoron wani ya ganta tana kuka. Yarda yayi shaping vegetables din kamar wata mace ba karamin mamaki zai baka ba cikin nutsuwa yake girkin Kamar yadda wata hadadiyar chef din zatayi saidai indomie ta kusa yi kafin ya zare kayar kifin tass ya zuba, kamshin ne ya cika gidan ko ina 15 minutes ya dauke sa dafa indomie da ruwan Lipton a plate ya zuba mata daidai daidai ba dayawa ba,saboda yasan ko yazuba da yawa din asaran shi zaayi ba ci zatayi ba shima ruwan Lipton din half cup yazuba mata ya saka sugar kadan kafin ya dauka yashiga dakin da sallama,baiji ta amsa masa ba,kuma bazai iya cewa bata amsa din ba shidai yashiga kawai ajiye kayan hannunsa yayi bai ce mata komai ba itama ko kallon sa batayi ba” ledar maganin ta ya dauko ya ajiye mata tareda pure water ya juya yafita yana tafiya kamar wani boss “ sai daya cika plate da indomie yazuba ruwan Lipton din kafin ya zuba sauran da ta rage a warmer ya rufe ya koma parlor kan shimfidar dayayi ya kwana domin bai dauke ba” tafara samun appetite hakan yasata cin almost half of the plate ba karamin dadi indomie tayi mata ba ruwan zafin ma tasha ba laifi saidai bata shanye ba raurau tayi da ido sadda tana ballar maganin ta tsani magani miye ma abun ya dinga ajiye mata magani while ta warke , da kyar dai tasha magani ta ture ledar. Agogon wayarsa ya kalla 10:00am daidai tashi yayi Sai da yafara kwashe shimfidar daya kwanta akai kafin ya share parlor tass, kitchen din yashiga ya share yayi arranging abubuwa dayayi amfani dasu kafin ya hada wanda ya bata wuri daya, fitowa yayi ya dauke bargon da bedsheets din da pillow ba waenda yasiyo bane duk a gidan yasame su, dakin yashiga yanzu ma da sallama,can ciki ta amsa shi sai dayayi da gaske kafin yaji ta amsa din bargon hannunsa ya buda wardrobe ya saka can gidan kasa inda babu komai da bedsheet din da pillow, ahankali yabude ledar magani sai da ya tabbatar da tasha din kafin da dauki plate din da cup din ko ina ta rage, ya wuce kitchen ya wanke 2 plates din da few kwanunin, ko ‘ina a parts din nasu looks very neat and tidy babu dirty ko’ina saboda baya son kazanta tun can mutun ne shi mai son tsafta, zama yayi yana ta juya wayarsa babu number ko



ciki sai ta dr ibrahim tun bayan tahowar su daga adamawa ya fida sim din ya yar ya siyi sabo a tasha dialing number dr ibrahim din yayi bugu biyu ya daga cike da barkwanci Doctor ibrahim yace balarabe mijin balarabiya, dariya sosai dr ibrahim yaba malik, yace wai waye balaraben kai yanzu fisabillah idan larabawa suka ji ka ai sai su sa akamani, dr ibrahim yace a kama ka sukoma da kai kasar su ko? Daman can Daga can din ka gudu “ malik bai sake cewa komai ba “ dr ibrahim yace ai nayi tunanin duk kamar yanzu baka tashi ba ,malik ya girgiza kai yace aa ni ai bana ranar bacci da asuba tayi shikenan da anga nayi ranar bacci tau a tabbata banda lapia gaskia “dr ibrahim yace kace kai ma iri na ne, malik yace naji kamar ma ba ka fita aiki ba lapia dai ko? Dr ibrahim yace lapia lau alhamdulilah am off today kasan daga karshan month din nan ma zan dauki hutu sai kuma bayan biki “malik ya ware idonshi yace no kabari dai sai can irin ya rage one week haka amma kace tun ending this month kusan wata daya da sati daya fa zakayi kana hutu “ hakane kuma tau shikenan yallabai na dauki shawarar ka malik yayi murmushi yace tau nagode “ ya mai jikin takara ji? Da sauki alhamdulilah dr ibrahim yace tau masha Allah in sha Allah nan da 20mins zan shigo gidan naka, malik yace tau Allah yasa daga haka ya kashe kiran. Dr ibrahim sai bin parlor da kallo yake koina tsaf tsaf sai kamshin turaran tsinke yake,kasa hakuri yayi har sai da yace wai har taji saukin fara gyaran gidan malik dai yayi shiru kamar bai ji sa ba, kitchen ya shiga ya zuba mashi sauran indomie da yasaka a warmer cikin plate ruwan Lipton din daya dafa ya huce saboda babu flask a cikin tukunya ya barshi hakan ya daura masa pure water biyu a wani plate ya kawo masa “ dr ibrahim yace sannu kace rabon naci dadi yasani zuwa gidan nan dawuri fara cin indomie yayi,can yayi kasa da murya yace kai fa abokina Allah yabaka wannan iya girki haka ko dai a catering tayi degree ne,shidai malik murmushi kawai yayi kafin yace kadai kar ace santi ne ya ruda ka,Kaci abinci kawai malam,tass dr ibrahim yacinye indomie bai rage ko kadan ba sunyi suna fira, har wajan 12:00pm dr ibrahim bai ko ji motsin aydarh ba “kuma bai ji malik yayi zancanta ba, kasa hakuri yayi yace ma malik,yallabai wai ina mai jikin ne ko bacci take sai sannan malik ya tuno ma da ita danshi sam ma ya mance da ita, malik yace kasan cikin drugs dinta kamar akwai na bacci , tunda tasha na safe bayan mun gama breakfast take bacci gashi yanayin garin akwai sanyi damuna kwara ta zauna a cikin dakin saboda yanayin lafiyanta kasan masu asthma “dr ibrahim daya gama sauraron malik yace “sure”fira suka cigaba dayi kamar waenda sukayi shekara 30 da sanin juna wannan ne karo na farko a rayuwar malik daya taba wani irin dama da matsayin daya ba dr ibrahim lokaci daya yaji ya yarda dashi kuma bugu da kari ma jinin su ya hadu;Dr ibrahim yace like I was saying before clinic din nan da chemist ne ahankali ya mayarda wurin clinic nida dr hafsa mun riga da mun san juna tun muna yara babana Allah yajikan sa malik yace Ameen ,da babanta tight friends ne a tare suke komai na rayuwa tare da ita mukayi primary school har sai da muka kai secondary kafin ita aka kaita boarding school ni kuma aka bar ni day,malik yace Allah sarki, dr ibrahim yacigaba dacewa Bayan munyi graduation ne daga secondary government ta dauki scholarship ciki har da sunayen mu ni da ita , saboda parents din mu daman sunyi kokarin ganin mun samu din saboda basu dawani karfin daukar nauyin mu,munyi jami’i anan BUK mukayi medicine kafin na karasa babana ya rasu itakuma bayan graduation dinmu da month daya mahaifinta da mahaifiyarta suka rasu yanzu haka tana zaune da kakarta inna daga nan gida daya ne tsakanin ku da gidansu,dr

ibrahim na fadin sunan inna malik ya tuno da tsohuwar da ta rakasa siyan gas jiya sai sannan ya tuna daya ce mata zai shigo yau ma da basuyi wannan firan ba ya manta ma da zancan ta, malik yace indai innan dakake nufi ne jiya mun hadu da ita a kofar gidan nata har ta rakani siyan gas, Dr ibrahim yace kai haba? Malik yace am serious,dr ibrahim yace lallai kam ajiqa ka asha innar da kowa hakuri yake da ita,ita kanta dr hafsa dan bata biyeta da tuni kowa ya kama gabansa fa,malik yayi murmushi yace nima a jiyan na fahimce haka, dr ibrahim yace kasan yanzu government din aiki wahala yake sai idan akwai wanda ke tsaya maka, malik yace hakane, dr ibrahim yace wannan bawan Allah mai clinic din shine yayi employing dinmu nida ita duk karshan wata ana biyanmu 30k nurse saratu kuma yarinyan wani abokinsa ce diploma ne da ita a chew 20k ne salary duk month dan dai kawai kar mu zauna ba aiki amma mutumin dake da degree a med yafi karfin 30k as salary malik yayi murmushi yace in sha Allah komai mai wucewa ne, dr ibrahim yace tunda dai madam tak’I farkawa na duba jikinta bara na wuce akwai inda zani daga nan din, malik yace tau shikenan dr muje na taka ma nagode Allah yasaka “ dr ibrahim yace babu komai ai an zama daya har kofar gida ya rakasa anan suka tsaya dayake center ce har yasamu keke yawuce, har ya juya zai shiga gida yaji ana tafa hannu ga salati ana rabkawa,juyuwa yayi suka hada ido da inna dake tsaye da katuwar jikkarta da uban mayafinta da alama daga anguwa take,malik yashafa kansa yayi murmushi yace ina wuni, inna tayi mitsi mitsi da ido tace aaa haram aaa haramun miye wani ina wuni bayan baka kaunar Allah ina zaman zamana kace mun zaka zo hadda saman lambarka a waya dana kira lamba yan kamfani suka ce man layin waje ne bana najeriya ba,bacin ina tsoron Allah karya ba halina bane ai da yanzu nace daman baka da gaskiya,nagaya ma hafsa yarda akayi tayi banza dani kamar wata tababba daman can niba shiga harkanta nake ba tunda na lura babu Allah a ranta tak’I fito da miji tayi aure ina jin fa yanzu zata iya 50 zuwa hamsin da,samari duk wanda yazo sai ta koresa tau irin wannan mi zai sa ka dinga shiga harkar

13 / 111