Author : Nana Maryama Category : Romantic Hausa Novels
tsiwa ahankali ya furta yah rabbil alameen mike shirin faruwa dani ni kama yasamu kansa da tambayar kansa, sai wajan nine yashigo bai tsaya koi na ba yawuce bedroom din zaune take a katifa tana karatu tanajin sallamansa ta amsa tacigaba da abunda takeyi bata ko dago ba zama yayi kan katifan kusa da ita yana kallon littafin datake dubawa, littafin ta rufe kafin ta dago tace yau kace babu ball but you stay long a waje ‘’malik yace ai nashigo gida aydarh tace amma ai baka parlor yace ohh ai ba parlor bai na can tareda da Ramlah aydarh ta dauke kanta batace komai ba tana sake bude book dinta,yace ina shanyin tayi masa banza ganin kaman idan ya cigaba da mata zatayi masa kuka yasa shin yin shiru kafin yace ina shanyin ? Batace komai ba tayi shiru kaman bazata ce komai ba can tace ina nagaya maka kaje tayi maka shayi kuma tunda baka jin maganata duk ranar danaga umminka sai na gayan mata ,malik yaware ido jin abunda tace yace kai haba?mi zaki ce mata tau?tawani hade rai tace ai tace tabakani amana right?malik ya gyada kai yace ehh amma bai kowa yasan ban ci amanan bak oh ?aydarh ta girgiza kai tace zance mata baka jin maganata idan nace kada kay isai kayi kuma babu ma ruwanka dani ka fita am sleepy,tafada tareda zamewa zata da kwanta yayi maza yajawo ta jikin yace yau sai na maki proving nine mijinki yau sai kinsan you are not longer a child kema macen aure ne dawani irin speed take kallonsa chest dinta na over racing saboda yarda taga yayi
.
Ganin yarda yarike ta din, yace sai kin gayamun,miyasa kika ce “Aji tsoron Allah !gabanta yafadi tawaro ido tace ni nace haka? Ya girgiza kai yace aaaaaa ni nace,tayi wani iri da fuska tace eyyerh ni fa haka kawai nace kuma ba ma sake tuna ma nayi ba?malik yayi shiru yana kallonta yace mikika sake tuna mun? Yafada ya saasssuta rikon dayayi mata ba komai fa “yace ohh naji tsoron Allah kar naci amanan ki naje wajan Ramlah ko?tayi kasa da kanta batace komai ba,malik yace magana fa nake dake tace Erh “yace tau miyasa idan naje yazama rashin tsoron
Allah? Tace ai ba matarka bace malik yace amma ai budurwata ce ko? Tayi shiru tana sauraron sa Still kanta nakasa tak’I dagowa ta kallesa , yace kinsa yarda nake sonta kuwa itama take sona kam? Aydarh tayi saurin rufe masa baki da duk hannunta biyun tace ban sani ba and I did want to know,kuma ni dan Allah ma sai dasafe bacci zanyi kafin ta dauke hannunta daga bakinsa yace kwanta tau nima anan din zan kwana yafada ya nuna mata gefenta tawani ware ido tace Allah bazaka kwana anan ba “malik yayi murmushi yashafa kansa yace akwai rana yana fadin haka yafita yabar ta da kallonsa baki bude har yafita,yana fita tamike tasaka wa kofan key kafin ta kwashe books dinta ta mayar jikka tadawo ta zauna kan katifan, tayi tagumi “tunda suka baro gida sai yanzu take tunanin karatun ta, ganin tunani na neman zautar da ita kawai yasa ta zame ta kwanta tana sauraron bugun zuciyanta,miyasa tayi saurin sabo dashi sabon da bayan abba da salmerh babu wanda take iya zama suyi fira har tayi dariya sai shi wani zuciya tace mata ai dole tunda yanzu baki da kowa sai shi ,tau idan dagaske yake fa idan yayi kudin zai je ayi musu auran d ita fa? Tawani tabe baki tace tau sai mi sai araba auran tunda daman ai bakwa son juna,kowa sai ya koma gidansu kawai lokacin su abba duk sun bar fushin amma kuma ai ko an raba zaki cigaba da ganinsa tunda yanzu you are families! Maida hulanta tayi kafin ta dauko pillow tayi hugging kafin ta yafa duvet ta cure waje daya har bacci yayi gaba da ita. As usual bayan sun gama gyaran gida suka daura breakfast shayi kawai suka dafa yasiyo musu bread sai eggs dasukayi frying kwana biyun nan malik duk yaji sa wani kala kaman baya bata abincin daya Kamata aljihunsa yafara yin kasa ga har yanzu bai sai mu aikin ba daman 10k ne dashi sai yahada da 20k din da Allh musa yabasa making 30k dashi ne yasiyan musu kayan abinci those days Ko fruits din ma baya wani siyan musu dayawa na kudi kadan yake siya he is just managing the situation kafin yasamu wani aikin, kamar ko yaushe shayin rabin cup ta zuba sai madaran kadan sugar kam baa magana tana son sugar sosai bournvita ma haka kallonta yake ko kiftawa babu yarda take motsa tea spoon dagani kasan hankalinta ba wajan yake ba , yace what is wrong ko bakya son shayin ne?ta girgiza kai tace ah’ah yace tau tunanin miki ke? Tace babu komai yayi shiru kafin yace tau yi break din ki ya atare zamuyi wanka to kawai tace masa ta cigaba da shan shanyin haka nan babu bread shima kallacinsa yake can takarasa sha shanyin ta sa fork tayi cutting egg din kadan takai baki sai da taci kusan rabi kafin ta ajiye zata tashi bako dago bay ace come back here and finished it all waza ki bar mawa? Kamar bazata dawo din bas ai kuma ta dawo don tasan yanzu sai yace zai dauke ta itama wannan tabatan dayake na mugun daga mata hankali ganin take har yanzun fa babu kyau kawai dai suna fada ne wannan ai mugun iskanci ne ba kaman wani lectures da tagani a wayan hibba,zama tayi Ahankali take cin kwan sai daya dauke ta kusan 25mins tana cikin waina daya na kwai time din har yagama ya kwashe nasa kayan yakai kitchen yadawo yazauna yana taba wayarsa kawai, ganin tana daukan lokaci har kwan ma yayi sanyi yace idan bakiyi sauri ba zan dura miki abun nan,aikam kaman jira take tayi saurin cinye last cut din kafin ta goge lips dinta da tissue dake nan gefen su a parlor, kafin tamike takawai plate da fork din sai cup da bread din kitchen tana shiga ta hada danasa danata ta wanke tass kafin tasa karamin towel ta sake goge sink din da ruwa yabata kafin ta fita bedroom ta wuce tana fito da kayan dirty ta duk da ba su dayawa ana daga suma kamshi kawai ke tashi (lemme use this opportunity please and please kuyiwa mahammada rasulilahi S.A.W ko baku da kudin
perfume ku din shafa alimun na naira hamsin ya isa yana tsane zufa please, damsel zata baku labari saura kadan tayi barin dan cikinta a wani event damu kaje jiya tsaban an gigita da odor) yana ganin tashiga bedroom yatashi shima ya bita yadinga binta da kallo watau taji yace zasuyi wanki tsaban miskilanci ne yasa tayi masa banza baice komai ba ya dauke kai ya bude inda nashi suke, yacigaba da fitowa dasu, har sai daya gama time din itama tagama, toilet din ta yawuce yadauko buckets sai soap wanda can suke ajiyewa daman can gida yasaba wanki da fizz shiyasa ma dasuka zo nan shi yake siyowa (shima fizz baya da tsada a taimaka yan uwa Wallahi har wanka ana yi dashi shima yana taimakawa wajan yaye odor) kanshi yadaga yana kallon very clean and attractive brassiere dinta dake wanke kal tayi hanging dinsu a nan toilet din murmushi yayi shafa kansa kafin yasa hannu ya jawo su ya dauki bucket din da soap din yafita, yana fitowa ta lura da abunda ke hannunsa ai dawani irin speed takarasa gabansa ta sa hannu ta figze kaman zatayi kuka ta mayarda su bayan ta “malik yabude ido alaman bai ma gane abunda take nufi ba yace ko wanki nace miki zaayi ba? Tayi masa banza yace ko bazaa wanke su ba su? Sai sannan da muryanta har yayi na kuka tace ai dai kasan a wanke su ko,malik yabude hannu yace aaaaa relax hajia kar kiyi mun kuka a ina nasan kin wanke su nayi tunani ai bakima iya wanki ba shiyasa nadauko sai mun wanke,har kwalla ya kawo idonta tayi gaba zata mayarda su toilet din tayi hanging tace daga yau karka sake taba mun,yace Alright booby girl!! Ai har kusan faduwa tayi jin abunda yace aikam da mugun gudu ta kwasa ta shige toilet tana shiga ta fashe da kuka kaman irin sai daya sharara mata mari,ya lura wannan yarinya tafisa fitina rigima gareta da shegen shagwaba sai ka rantse kace she is 15 wani yarinyar ma yar 15 tafita wayyo bazaka tabawa cewa tayi ashirin da biyu ba,kawai dan Allah yayi ta hakane and she deserves to even do more than this duk wani gata na gidan duniyan nan babu wanda bata gani bah, girgiza kansa yayi kafin yadauki veil dinta yakai a nose dinsa lumshe ido yayi yana jin wani irin precious air na bi ta koi na a dakin he is mad akan kamshin nan nata yana son kamshinta fatar take ke very warm gawani natural scent mai yin kaman tana using da rose yana sa shi jin wani iri duk sanda suka samu kusance da juna “ tunda take kukanta yana jinta taki shiru kuma taki fitowa ita kunyar ta daya dayace mata booby girl,bakaramin kunya yasata ba,ganin taki fitowa yasa shi yin knocking tana jinsa tayi masa banza ta dinga zubawa kofan harara kaman irin shine a tsaye wajan,can yace open the door, nan ma tayi shiru kafin yace tau ai shknn bara naje sai ita Ramlah ta tayani tunda ke bazaki fito ba tanaji abunda yace tayi saurin bude kofa, tana kallonsa da fuskanta dahar tayi ja tace Wallahi bara ta taba kayana ba balle naka ma, idan bahaka ba I will beat her blue and black Allah, malik yayi murmushi yace tau kiyi hakuri yanzu mu tafi can ventilation sai muyi wankin ko? Aydarh ta gyada masa kai shi yadauki kayan dukka ita ta dauki musu bucket da soap, nata aka farawa da ya wanke sai yasa mata yayi tunani bata iya bas ai gashi yaga tana yi , har suka kusa gama nata babu mai magana cikin su amma there looks good kallo daya zakayi musu ka kasa dauke ido can yayi kasa da murya yace ashe kin iya wankin?ta dago tana kallonsa kafin tace erh yace kinyi kokari tayi murmushi kallonta yake ko kiftawa babu yace bana son asaka hakuri amma your own looks cute tayi murmushi tace thank you hakurin gwal din yasake kalla wanda yazauna mata dass a jerin white teeths dinsan sai shine shine yake sau dayawa idan tayi dariya yana so yayi magana shiru kawai yake can dai suka karasa nata ya kwasa ya wuce can bayan part
dinsu zai shanya shanya su yayi kafin yadawo yana dawowan yace tau kiji ki huta sai na karasa nawa ko? Ta girgiza tana wasa da foam din dake cikin bucket dinta tace ah’ah zanyi “yayi shiru kafin yace okay wankin suka cigaba dayi babu wanda ke magana a cikinsu kowa da abunda yake ransa sallama akayi suka amsa dr hafsa ce tsaye suna hada ido tayi murmushi tace yau wankin kauna ake tau sannunku malik na murmushi ya amsa gaisuwan datake masa kafin Aydarh tace welcome auntie ina kwana? Dr hafsa tace lafiya alhamdulilah ya gida?aydarh tace lapia lau “kafin ta mike tana wanke hannunta tace ki shigo Auntie dr hafsa tace aaa kawai tunda mun gaisa bara na wuce ai aiki kuke, malik yace no sai fa kin shiga ai mun kusa gama ku shiga kawai nakarasa aydarh ta bude kofan babu yanda dr hafsa zata iya haka tashiga anan parlor suka zauna Aydarh nasake tambayan dr hafsa ya jikinta ina inna? Dr hafsat ace naji sauki sosai Aydarh ina na nan lafiya tama tafi kasuwa maybe yau ma ku ganta saboda naji tana cewa yau bazata kwana bata shigo ba “kwana biyu bata ga audu ba kila ke kika hanasa zuwa Aydarh tabude ido sosai kafin tace ah’ah auntie Wallahi bani bace,banma san yadaina zuwa ba tayi hakuri “dr hafsa tace ahtau idan tazo dai sai kuyi mata bayanin komai kenan Aydarh ta mike tana cewa Allah yakawo ta lapia shiga tayi kitchen ta fito hannunta rike da plate sai pure water biyu akai ta ajiye gaban dr hafsa,dr hafsa nayi mata sannu ta dauki ruwa daya tafasa tana sha,.hibba tayi shiru kafin tace tau yanzu wa zakayi wa maganan kasan yarda zaka samu shi Doctor? Dr ibrahim yayi shiru kafin yace akwai wani yaron gidansa abokina na ne munyi dinki shago daya kafin yasamu aiki a gidansa nikuma nakoma clinic duk karshan wata yake zuwa kano saboda Doctor usaman yasa mar masa aiki a can wani babban private hospital a lagos in sha Allah idan yazo komai yake nan nayi tunani abunyi,hibba ta gyada kai tace nan da kwana sha daya kenan? Dr ibrahim ya gyada kai tace tau Allah yakaimu lafiya asa munada rabo baki daya dr ibrahim yace Ameen wifey “kafin yawani marairaice fuska yace massage please,batace komai ba domin tasan abunda yake nufi hannunsa kawai takama suka tashi, anan bedroom suka zauna kan gado hibba ta cigaba dayin ta mijinta, kafin kuma suyi tafiya can.bilki ta dinga kallon rabiah ko dauke ido babu batace komai ba rabiah tace kiji wani iskanci niga banza sai surutu nake kinyi mun shiru bilki tace aaaaa wai ai jirana nake kigama tunda na lura kaman kin fara samun damuwa a kwalwa,rabiah tayi wani zagi tace ban ma gane ba mikike nufi ne?bilki tace rabiah banda mu bamu san ciwon kanmu ba kawa isai muje mu kama masa mata mu daka tsabar ke baki da kugu ke kanki dakikayi maganar kinji abun ya hau daidai fisabillahi?rabiah tayi shiru tana kallonta,kafin bilki tacigaba dacewa yoo ko shi bai ce manah komai yayah ibrahim bazai ya hallaka mu ba har lahira “balle wannan bawan Allah da idan kika yana kallon matar sa kamar ya afka mata jikin jamaa ke kalan jikinta ma yayi maki kama da jikin da ake duka?tau idan baki da lissafi ni inda shi babu ruwana kawai kibari mu samu kudi sai a koma wajan malam muga abunda Allah zaiyi,rabiah dai tayi shiru amma bakin ciki kamar ya kasheta so tayi suje su chanza mata kama ko kila ko sau dayane ya kalli ita rabiah da idonsa ko sau dayane tunda duk wani magani data karbo baya aiki har kudinta ma yakare yanzu haka so take tahada su koma amma abun ya faskara shiyasa take ganin shine mafita hakan
.
Bilki tace tau Wallahi babu ruwana a wannan hau din idan kingani a lahira fa kaine akai wooo ni shegiya kina ganin mutane jiki duk Hutu bakisan daga inda suke ba, kice zaki haye musu billahi
babu ruwana, rabiah dai tayi shiru tana sauraron bilki har tayi shiru kafin tace tau ni Wallahi wayata zan siyar na koma wajan madawaki asan abun yi, bilki tace tau shknn ai yafi dai kafin ta mike tana daukar mayafinta tace rakani wajan anty hibba mu gaisa nawuce gida babah tace kar najima rabiah ta mike tace mutafi Allah yasa yayan bai nan kinsa sa mayyanta ne Wallahi ko da yaushe ya baibaye da ita Wallahi bilki tayi dariya tace halinsa guda da abokin nasa kenan rabiah tace uhm Allah ya kyauta bilki Tace Ameen , Sallama suka hibba ta amsa musu shiga sukayi tana nan zaune parlor tana kallo tana ganin su tayi murmushi tace sannunku da zuwa bilki tace yauwa anty ina wuni? Hibba tace lafiya lau ya gida? Bilki tawashe baki tace lafiya lau, rabiah ma tagaishe ta amsa kafin ta mike ta shiga kitchen zata kawo musu ruwa bilki ta kalli rabiah tace ashe matar nan da kyaunta har kiba ma tayi nagani rabiah dai ta tabe baki tac eke kullun sai kin gama yabon mutane ina dalili kam tafada tana tsaki ruwa ta kawo musu sai chin chin batayi girki bat ace su zauna ta daura ko indomie bilki tace aaaa sauri take idan tadawo zata ci wata rana hibbah tace Allah yakaimu ruwan suk asha da chin chin sama sama sukayi fira domin hibba sam bata son rawan kan yaran, har bakin kofa ta rako su sukayi sallama ta koma ciki. Kallonsa take har yagama kafin tace to ka kwanta Allah zanyi fa nace maka, malik dai sai kallonta yake kafin yace nace miki ciwon kan kadan ne saboda nashiga rana ne,tayi shiru bace masa komai ba ya mike,yace muje kitchen din suka shiga yayi mata blending, kayan miyan duk da daurewa kawai yake ji yake kaman zaiyi fever tana lura da yarda yake ta ciza lips dinsa ,can tace ka fita zan karasa ya girgiza kai kawai yacigaba da abunda yakeyi, bata sake magana bai ta ta cigaba da yanka vegetables din, kasa daurewa yayi kawai yamike yafice daga kitchen din nan parlor ya dawo ya kwanta kan carpet kansa na wani irin sarawa rufe idonsa kawai yayi yana sauraron yarda yake kyarma,kaman kar ta fita sai kuma ta wanke hannunta ahankali tasa karamin towel ta tsane hannu “ fitowa tayi yana kallonsa ko dauke ido babu karasawa tayi kusa dashi kafin ta kai hannu ta a neck dinsa temperature dinsa yayi high sosai dasauri ta dauke hannunta gabanta nafaduwa kafin tace,jikin yayi zafi sir daman baka da lapia? Girgiza kai yayi bai iya ce mata komai ba mikewa tayi ta nufi bedroom very clean duvet dinta ,ta dauko masa tadawo ta yafa masa, har kai ta rufe masa tama rasa mi zatace masa can tace sannu, tazuba masa ido kawai hankalinta bakaramin tashi yayi ba,tana tunani ko ta kira dr ibrahim can tace sir ka kira Doctor manah hannu yasa cike da dauriya yabude duvet din yace kije ki karasa girkin zan kira sa bata tashi ba kuma bata daina kallonsa ba, can dai ta mike ta koma kitchen din ta cigaba da girkin amma hankalinta na wajansa, sharp sharp takarasa ta fito tasame sa,zuwa yanzu ya daina zufan sai ajiyan zuciya dake saukewa kadan kadan alaman yayi bacci bude duvet din