Author : Nana Maryama Category : Romantic Hausa Novels
hannu aljihu yafito dasauran cash dinsa yamikawa dr ibrahim din baki daya karba yayi kafin shima yafito danashi yabawa malik “kowa yama kowa kyautan kirari kenan Wallahi abun nasu dole ya birge kowa kaiiii “dariya duk sukayi kowa na parlor ma haka hibba dai murmushi take tana girgiza kai abunda basu sani ba shine tunda suka fara maryam ke musu vedio “ kafin malik yace hutu fa bai ganmu ba tashi zakayi flight din baqin remains 20mins yayi landing airport zamuje mujira su daga can munyi magana da Abba gidajen dazasu sauka duk a can GRA suke dr ibrahim yace ohk yallabai muje koh?sallama sukayi musu kowa yamusu Allah yatsare suna fita maryam tace yesssss addah nayi musu vedio fa aysha tace dan Allah fa halime tace dan Allah baby sis drop it to me hibba ma tace haka maryam tace noo sai na fara nunawa auntie aydarh first followed by you guys “ aysha tace wai maryam bazaki barta suyi hidiman gabansu ba kije ki dinga matsa mata bikin nan fa nasu ne “maryam tace tau addah drop duk tayi musu sai ga sallaman baba da inna sai hajajju daga baya tana waya da abby daga gidan Abba suke yanzu din aysha tayi musu sannu dazuwa sauran ma duk sukayi musu “inna tace wuuu bara dai nazauna amma yau naga ruwan lefe masha Allahu “ kaman zaa bude shago aysha tace kai haba inna Allah yasa alkhairi “baba tace Ameen Ameen “hajajju tagama wayan tace ina audul din? Maryam tace sun fita shida yah ibrahim hajajju tace yanzu fa suka dawo shida matar kuma sun sake fita aysha tace ehh zasu dauko baki ne hajajju tayi shiru kafin tace tau mu dakika dauki dinki kika ba kawarki har yau fa bata kawo manah muyi magana ace bama son a zauna lafiya “ aysha tace idan kikayi hakuri ma gobe zata kawo muku “hajajju tace ko dana ji ai baba tace Allah yakaimu goben lafiya aysha tace Ameen. Baki daya oum tazama busy duk waennan classy mamas din na Abuja kaduna sun iso business partners dinta na outside countries ma sun iso da few families dinsu nacan sudan hadda auntien dinsu kanwar maman oum uwa daya uba daya murna wajan oum baa magana “ rufaidarh kam duk tayi wani kala ganin dai dagaske auran nata zaaayi ‘ suma su dr usaman yau zasu iso extra gyaran jiki akayi mata yau sai ka rantse kace she is 24 batakai 39 din ba wani irin hadaddan jan lalle akayi mata Wallahi kaman andaura shi a hannun yayi kyau bana wasa ba irin nasu na yan sudan itama aydarh kalar shi akayi mata oum ma haka su uku kawai tayi mawa saboda kabilanci irin na yan sudan din babu yanda oum da rufaidarh basuyi ba tayiwa su dr hafsa dasu halime tace bazata yi ba aydarh har cewa tayi zata kara wasu kudin kan yanda takeyi tayiwa maryam amma
tace ba zatayiwa kowa ba bayansu uku cus cikin dare ma zata bi flight takoma hakuri sukayi aydarh duk bataji dadi ba hadda maganin baki aka saka a lallan saboda yanda yayi “malik through out basa nan suna can wajan shirye shiryen su dasu dr usama “sau daya yakirata shima tace masa zaayi mata lalle ya kashe “ yanzu ma salla suka fito yasamu waje yazauna ya kunna data kafin yakira ta waya yace tazo Whatsapp time din an wanken lallan jikinta taji duk yana mata ciwo kaman tanajin amai “datan tabude yakirata vedio call dauka tayi “tayi wani cute smile kafin tadaka masa hannu showings him the lalle tace hey!bude baki yayi yana kallon hannu ai kashe wayan kawai yayi yazare car key hannun dr ibrahim dake waya da dr faisal yace masa wajan dayan dare zasu sauka adamawa shi da sauran doctors din dr ibrahim yace ma dr faisal hold kafin ya janye wayan a kunnansa yace where are you heading to? Malik yace kadai kawaii ina zuwa idan uncle yafito daga masallaci kace masa ina zuwa dr ibrahim yace tau shknn motar yashiga few minutes yakaisa anguwan su gidansu yashiga sai da yaji kunya ganin mutane kuma duk manya mata ga oum da rufaidarh anata hada hada cike da wayewa gaishe su yayi rufaidarh tayi introducing dinsa as mijin aydarh “kowa masha Allah yake kira anata yabon malik din sai addua ake masu matan prime minister data iso itama tun yau bikin amaryar sa ce tight friend din rufaidarh ce “ tace barakallah hajiya fatima amma yan uwa ne ita dashi oum tace sure cousins ne ita dashi “matan prime minister tace barakallah zanso nagansu atare nasan they mades a beautiful couples masha Allah rufaidarh tace bana wasa ba fa “shidai wucewa yayi rufaidarh tace tana dakinta knocking yayi tazo tabude masa yana shiga yayi hugging dinta yacigaba da juya ta dariya yabata tace wait wait kana jina bana jin dadi Allah kadaina juyani fa “yatsaya yakama both hand dinta yace Tabarakallah masha Allah Allahumma bareek wife “ tace Ameen Doctor “ addua yatofa mata na baki a hannun kafin yayi kissing dinsu tayi murmushi yakamata suka zauna yace where’s the lady?tace which lady yace the henna designer tace tana can guests side kanaji wai tace bara tayiwa su yah mariam ba kaga bara su ji dadi ba yace tau su ina ruwansu da wacce tayi muku lalle banda abunku na mata tace babu dadi aie “yace bazasu ce komai ba Allah kila su hannunsu bayayin kalan shi tayi masa wani kallo tace who said so akwai hannun dabayayin lalle ne daman?yace nidai ban sani ba tace I need a favour please yace anything for you my life tace dan Allah zan raka su wajan mai yi manah lokacin yace kedawa yace me and salma “malik yace kaiii ina salma wife namanta itace wacce a lokacin bikinmu ko?tagyada masa kai yace Allah yasaka mata da alkhairi aydarh dai batace komai bayace ina take please I wanted to thanks her Wallahi tace nidai yanzu naga ba maganar salma nayi bay ace ohk ohk sorry dear waye zai kai ku tace kayi dropping dinmu yanzu manah wurin hadda salon duk sai ayi manah yace ohk tau dauko veil din abayanki mu tafi ina sauri tace yeyyyyyy nagode my Doctor yayi murmushi yace anything for my dan aseey “suna saukowa aydarh tayi kasa da kai tana gaishe su kowa sai kallonta yake ana yabawa ga lallan ta yadauki hankalin mutane sosai wata client din oum tace masha Allahu matan da mijin ma kama suke rufaidarh tayi murmushi tace kaman jini ba ,malik dai yayi musu sallama aydarh tace zasuje ayiwa su mariam lalle ayi musu salon rufaidarh tace kiyi kitso baby yau daya dai aydarh tace don Allah ah’ah mom kibari dai nayi salon din rufaidarh tace tau shknn itama zuwa dare sai taje ayi mata “motar suka shiga yayi horn aka bude musu a Parking space ya tsaya yace bazai shiga ba amma nan da five minutes idan yaran basu fito ba
‘zaiyi tafiyar sa tace to “tana shiga duk suna parlor mariam tayi mata oyoyo suna ta yabon lallan ta “tace auntie muje yana jira dr hafsa tace tau duk muje dan Allah kusan halin mutumin nata fita akayi malik yace wa driver yadauki wasu a tafi da hibba sai halime da rabiah suka shiga dayan motar aydarh da aysha sai maryam da dr hafsa suka shiga na malik “bakin wani babban wajan salon aydarh tasa yayi parking “kudi ya dauka kusan 200k yabata yace su biya idan aka gama afara yi mata salon din zaya dawo yadauke tace masa ah’ah sai angama musu “ kissing cheeks dinta yayi tafita yatayar da motar yatafi matar kaman zata cinye aydarh har ta fidda ran zata sake ganin aydarh duk abunda shagon ta yazama silar aydarh da salma ne sai wajan matar take jin ma salma na new york can take karasa karatunta” dan danan aka kama hannunwan su mariam tace bata son na kafa aydarh tace eyyerh yah mariam dan Allah ayi miki manah maryam tace tau auntie “ salon din aka ma aydarh wani irin gyaran kai akayi mata yayi matukar masifan kyau wurin experts ne “ sun iya komai bana wasa ba ‘babu bata lokaci ya rage daga hibba sai halime yarage “ ayi mawa suma an musu gyaran kai lallan ne yarage kawai “ basu suka tafi bas ai kusan isha daga aydarh har rabiah duk sun sha wahala sun gaji amma babu wanda yayi magana cikinsu dr hafsa duk tausayi suka bata bakaman aydarh dake wahalar laulayi “ don kar yayi fada takira sa “yace hidima tayi musu yawa lokacin suna tare da dr usama yace bara yakira driver yazo yadauke su motar biyu aka turo ta tafi dasu “ dr hafsa tace baki sun fara yawa ma Wallahi ko zaki kwana gidan ummi tunda nan kawai yan tsohuwar anguwan su ne?aydarh tace ah’ah auntie aie babu kowa a part dina lapia lau “ dr hafsa tace tau shknn ita da rabiah daman tun jiya anyi musu tare da ummi “shiga sukayi ummi sai data rungume aydarh tsaban yanda lallanta da gyaran kan yayi kyau ummi ta dinga musu addua dr hafsa tace Ameen ummi mungode baba tace Tabarakallah masha Allah da yanmatan da matan aura duk sun hade ubangiji Allah yayi albarka “duk sukace Ameen halime tamike tace dan Allah muje mu nunawa auntie rufaidarh da oum tare suka fita ‘rufaidarh na dakinta oum kuma na can tare da wanda zasuyi serving gobe wajan kamu “ a daki suka tarar da rufaidarh ta shirya tayi wani kalan kyau perfume kam kaman tayi barinsa a jikinta kaiiiii “ dark green din abaya tasaka ga lallan su duk yakara duhu Masha Allah tashafa powder da lipgloss dr usama zai zo yanzu su fita gyaran kai wannan shine haduwar su ta biyu face to face “daga waccan time din dayaxo kuma shima ranar yajuya saidai vedio call yau ne na biyun “tana ganinsu tace hun wannan hadewa haka maryam ta washe baki tace duk saboda kene mom rufaidarh tayi murmushi ta dinga hyping dinsu “kowa nashi yayi kyau Wallahi fita sukayi yarage daga ita sai aydarh “Aydarh tace mom naga kina shiryawa uncle ne zaya zo tafada tana rufe baki ‘rufaidarh tayi wani smile tace erh fa dota “Aydarh tace kuma kinyi kyau sosai mom rufaidarh tace thank you my love “suna cikin magana kiran wayar malik yashigo wayan aydarh dauka tayi yace mata tafadawa mom ga uncle nan a parlor abba sun gaisa da abba shine kawai a parlor abba yafita wajan bakinsa dasuka iso ‘tace ohk kashe wayan tayi tafadawa rufaidarh abunda yafada mata “ rufaidarh tace kingani ma kunya nakeji Allah “ Aydarh ta kwashe da dariya tace ba ruwana nidai bara naje daki wanka zanyi na kwanta kaina na mun ciwo ‘rufaidarh tace ki sha magani gajiya ne ki dinga kula baby yanzu bake kadai bace “ kinsani tace ohk mom sai kun dawo atare suka fita aydarh tayi dakinta ita kuma rufaidarh ta tafi wajan da oum take hidima take kan jiki kan karfe hakika kowaye kai dole wannan yan uwantakan ya birgeka “ yarda
oum zatayi hidima a bikin aydarh haka takeyi yanzu a bikin rufaidarh da a bikin aydarh ma batayi ba shine ta hada biyu a yanzu takeyi “ oum naganin rufaidarh tace hun barakallah matan sudan inyeeee kinfito a balarabiyar ki Masha Allah rufaidarh tayi murmushi tace kai uktiee oum tace Wallahi har yazo ne? Rufaidarh tace eh yana parlor yallabai zamuje gyneotype daga can sai nayi salon din ko nabari mutafi taran dasafe din oum tace haram haram yau zaayi miki shine kingani kawai na rage sai nayi tunda kamun na yamma ne kuma makeup artist din ita kanta gobe zata iso daga FCT din kinga babu time a gobe kwara kawai ayi miki yau din idan yaso ni sai naje dasafe in sha Allah rufaidarh tace sannu uktiee duk yau fa ko wajan yallabai baki je ba fa “ oum tace shima yasan dole nayi aie shima yafita yanzu haka guest dinsa sun karaso suna guesthouse ma “rufaidarh tace eh haka son ke fadawa baby oum tace sun dawo ne?rufaidarh tace eh “ oum tace kiyi sauri ki je kar yagaji da jira bara nasa aka wo masa ruwa “rufaidarh tace kibarshi uktiee kinsan bazai ma sha ba “oum tayi murmushi tace haka fa .Dr usama ne zaune a parlor abba yayi kyau bana wasa ba sky blue din yard ne a jikinsa hadda hula yayi kyau sosai Masha Allah rufaidarh tayi sallama ahankali ta durkusa yace no wife up ta girgiza kai tace ka amsa kafin yace Alhamdulilah darh “rufaidarh tace kazo lafiya
?
Tace anyone of your Choice tafada kanta akasa yace no darh ai bana gane abunda kike fada tunda bakya kallona ma yayi kasa da murya yace look up takasa dagowa balle su hada idon shidai sai murmushi kawai yake yace kinyi kyau tace thank you your highness “yace oh wow nine highness?cikin wani soft voice tace you are more than highness aie ranka dade yace tau where we heading amaryan jibi?tayi wani smile tace zaka taimaka ma angona ne muje asibiti kaima zan taimaka wa amaryar ka a duba ka “yace Alright princess muta fi?ta gyada masa kai mikewa yayi ya warwari tissue yagoge hannunsa kafin yazuba a dustbin din dake nan parlor ita har mamakin sa take Wallahi har fargabar zaman su take saboda wannan tsafta nashi no bawai wani abu ba cus tsafta daga kansu ankare sunada tsafta nakin kari amma nashi yayi yawa bazata so tana bata mashi rai ba domin duk duniya babu mutunmin datake matukar masifan so irin sa bazata san dawani abu zata sakawa malik ba nan wannan abun datayi mashi abunda tasani kawai shine duk duniya babu wanda yataimaki rayuwarta bayan oum,abba sai aydarh da malik sun hadata da lifeline dinta “babu abunda ke sake birgeta dashi irin yanda voice dinshi ke fita idan yana magana kaman ba hausa yakeyi ba kaman wanda ke indiyanci ko turanci idan yana hausa turanci kaman a bakin dr usama kaman shi yakawo British a world baki daya he is real definition of perfect “tsaban illimi da zaman waje daya kama jikinsa har yakoma kaman wani bature ma amma kallo daya zakayi masa kasan bafulatanin usuli ne shi “ ahankali ya waiwayo yace banga matan son ba and banga your favorite sister ba yakamata nayi gaisuwa tace oh namanta suna can they are preparing for tomorrow muje mu yanzu dare yayi idan yaso gobe zaku gaisa in sha Allah yace ohk tau bismillah yanuna mata da hannu datayi gaba ta girgiza kai tace you first Allah shi taimake ka yayi smile yace your wish is my command sarauniya yanda yafadi sarauniyar yabata daria tayi dariya kafin yashiga gaba tana bayan sa motar da malik yakawo su da ita suka nufa yatsaya yace then bana driving a dare gashi kuma titin Nigeria zamu kira driver ne?tagirgiza kai tace no zanyi yace are you sure?tagyada masa kai yace i didn’t want you to stress yourself wife idan bazaki iya ba nakira son sai yakaimu ta shagwabe fuska tace zan iya fa Doctor yace tau
shknn “ko na one minute dr usama baiyi loosing kallon rufaidarh ba baki daya kunyar sa take ji ta maida hankalinta kan driving din datakeyi kadan kadan sukayi magana wanda shine ma ke firan rabi da quarter din tafiyar amsa waya yake kuma duk da vip din dasuka zo bikin ne daga different countries “duk sun sauka adamawan malik da dr ibrahim ba karamin kokari suke ba wajan dauko mutane daga airport ‘abba ma da abby suna nasu kokarin wajan attending dinsu kasancewan duk manya sun sauka a adamawan yasa garin dauka koina maganar bikin akeyi “ wata hadaddar private hospital sukaje babba ce sosai mai kyau da tsada handbag dinta yakarba tayi kasa dakai kafin su cigaba da tafiya suna shiga reception din ga nurses nan zaune office din MD din suka nufa direct ba wai yasan su ba no kawai yana ganin su yasan wasu ne mikewa yayi tsaya with due respect yagaishe da su dr usama ya amsa kafin MD din yace have a sit please suna zama dr usama yadauki sanitizer a wurin yagoge hannunsa kafin yamikawa rufaidarh murmushi kawai tayi takarba tayi kaman yanda yaje nufin wani white clean handkerchief yafiddo daga aljihun sa yasa yazare medicated glasses dinsa yana kallon MD din kafin yayi masa bayani abunda yakawo su without spending much of time aka fara masu test din duk da asibitin specialists ne amma shi da kansa yakarba yama rufaidarh nata wajan deban jinin kaman wanda zaiyiwa dan jariri kadan yayi mata ouch din datace yasa shi saurin janyewa yana fadin sorry darh aie nagama ta gyada masa kai hadda wasu yan kwallan karya nan take aka fido result din and everything is Alright in the rest Alhamdulilah! Payment yayi in dollars ma kafin MD har wajan motar yarako su don sai yanzu yagane dr usaman sun taba haduwa wani conference a lebanon “ suna shiga motar yace ko I should driver har yanzu da zafi?murmurshi tayi tana son taji yayi hausa akwai dadi hausan shi gashi yana fadin words da hausa kaman dai wani bakatsine “tace no nace zan iya muje yace saura mi yanzu tajuyo tana tura masa baki alaman shagwaba tace kaiii yayarh har kagaji ne ya girgiza kai dasauri yace haram ni na isa nace nagaji I can spend the whole with you without getting tired!tace oh really tafada tana dariya yace hundred percent sure tace tau thank you yace anything for my darh bakin wani wajan salon tayi parking yace zan iya shiga najira ko kuma na zauna anan tayi shiru kafin tace zaka iya zama a reception yayi murmushi yace kina tsoro kar nashiga naga you didn’t have long hair right tayi masa wani kallo banda har yanzu shi ba muhararminta bane dasai tabude masa yagani amma zuwa jibi bazai maimata haka batace Allah Doctor maybe duk kasan dakake zuwa kana ganin ladys