SAFIYYA BOOK COMPLETE MAMAN MAMA.txt

Author :  Maman Mama Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   102 / 113

303K to 306K   out of 336.6K words

ma daina
magana sosai and it broke my heart to
see her like that amma sai in taushi kaina
da gayawa kaina cewa bani na saka ta a
cikin damuwa ba. Ina dai iyakacin kokarin
ganin nayi involving dinta a komai ko da
kuwa ta hanyar bata update ne akan duk
abinda ake ciki, in ta bada shawara kuma
ina kokarin gain nabi dan in faranta mata
ko yaya ne. Amma na san zuciyar ta tana
wajen yayan ta.

Bata taba yi min maganar Safina ba nima
ban taba yi mata ba, haka Muhammad,
bai taba yi min maganar ta ba nima ban
tambaye shi ya suke ciki ba,

At a point da abubuwa suka yi min yawa
sai da na gayawa Muhammad ko za'a kara
sati daya ne? Dan har lokacin masu gini
ba su gama finishing ba ga masu saka
kaya suna jira, ai kuwa a take yaje ya saka
Ya Amen a gaba ya hana shi shakar
numfashi mai kyau har sai da suka gama
komai in two days sannan ya bar shi ya
huta. Sai masu kaya suka fara aikin su,
saboda kurewar lokaci haka suka yi aikin
nan day and night, na tattara twins na
tura su gidan dan su tabbatar anyi komai
yadda ya kamata. Da suna can din ma ban
kyale su ba ko da yaushe muna waya ina
jin abubuwan da aka kawo da kuma a inda
aka saka komai, sai kuma su yi min video
su turo min in gani dan in tabbatar da
cewa abinda na ce ayi ne kuma an saka
shi a inda ya dace. Kuma interior
designers din sunyi kokari sosai gaskiya.
Few things ne naga an samu kuskure
akai dan haka banyi dragging ba sai kawai
na barsu tunda dan Adam tara yake bai
cika goma ba.
Aunty Hajjo ma kullum sai taje gidan taga
progress din aikin, in da gyara tayi musu,
at a point uncle Ahmad ma yaje ya ga
komai kuma ya bada nasa shawarwarin.
Sosai kuma nake jin dadin yadda komai
yake turning out, sosai kuma nake kara
investing in making my home as luxurious
as I can dan a raina ina ganin nan ne gidan da zanyi mafi yawa daga cikin
rayuwata a ciki, gidan da zan haifa kuma
in reni yayana. Gidan da zan kira gida na.
In three days suma suka gama saka komai
da jera komai sannan aka gyara gidan tas
aka rufe.
Ranar da aka gam aikin, ranar Alhamis
kenan, twins suka dawo gida da rana suka
tarar da ni tare da Muhammad a harabar
gidan mu amma daga side muna zaune
akan kujeru sai suka karaso suka gaishe
da Muhammad sannan suka gaya mana
cewa wai sun kama daki a gidan, yanzu
ma kayan su suka zo dauka. Muka yi
dariya Muhammad ya ce "to Allah ya sa
ba dakin Haidar kuka kama ba dan tun
dadewa yace shima ya kama daki"
Hassan yace "ko dakin sane tunda mu
biyu ne shi kuma shi kadai dole ya hakura
ya bar mana, in ba haka ba kuma sai a
gwada karfi aga wanda zai kayar da wani"
aka sake dariya suka shige, sai nabi bayan
su da kallo ina jin dadin yadda suka yiwa
Muhammad magana, they have been
quite about the whole issue kuma na san
an saka su a tsakiya ne, though ni ban
taba zama na tambaye su ra'ayin su ba
kawai ina involving dinsu ne a cikin
abubuwa. Bayan sun wuce Muhammad ya yi clicking
fingers dinsa a kusa da fuskata, wannan
ya dawo da ni hayyacina na juyo ina kallon
sa sai yace "ina kika tafi?" Nayi murmushi
"ina nan" yace "a'a, kin bi twins dai kun
shige gida kun barni anan" na sake
murmushi kawai. Tunda satin ya kama na
koma shiru sosai. Magana ma kadan
kadan nake yin ta dan abubuwa ne da
yawa a raina. Ina son muhammad ina son
auren sa amma kuma ina tsoron auren
sosai, kuma bana son rabuwa da Daddy.
Sannan kuma ga missing Ammie da nake
kara yi sosai a kwanakin nan, duk da cewa
uwa uku nake da ita a yanzu amma babu
wanda zai iya replacing gurbin uwa a
zuciyar yarta.
Muhammad tun yana tsokana ta yanzu
har ya bari, tunda in ya tsokane ni ma ba
kula shi nake yi ba. Sai dai ya shigo mu
zauna yayi ta min hira ina amsa masa
sama sama,

An gama tsara komai na yadda bikin zai
kasance, kamar yadda Daddy ya bukata
ya kuma cigaba da insisting, baya son duk
wani abu da zai jawo attention din
mutane, ina ganin kuma hakan da yayi ta fada ne ya saka suma gidan su
Muhammad ba su shirya wani shagali
babba ba. Ya dai ce min zasu yi wuni a
gidan kakannin sa ranar friday. Ni ma
kuma a ranar Friday din ne zanyi taron da
na shiryawa friends dina "Fiyya's Sourie"
na kira taron, Muhammad ne ya kama
mana inda zamu yi taron ya kuma biya
komai, Mufida kuma ta aiko min da
gudummawar sovenniers masu tsada da
za'a raba wa mutane, da ma na karbi
number dinta a hannun Muhammad tun a
week to taron muni magana kuma na
aika mata da cards guda ashirin nace ita
da cousins din su mata. Salima ma tayi
wadansu sovenniers din.
Daga taro na kuma sai walima da za'a yi
ranar Saturday, ranar da za'a kai ni gidan
Muhammad. Ita kuma walimar a gidan na
wa za'a yi ta a harabar gidan, both family
na da na Muhammad zasu yi attending a
lokacin ne kuma danginsa zasu ganni,
kowa kuma zai samu damar ganin gidan
amarya.
Muhammad ne ya kawo shawarar kuma
aka karba, amma kullum in muna maganar
sai nayi masa mitar zai saka a bata min
gida, Dan sosai nake ji da gidan nan nawa shima kuma ya sani. Ya kance "ni kam in
aka bata gidan nan ina jin ba za'a barni in
vi bacci ba"
Na dago kai na sake kallon sa dan jin da
nayi a jikina cewa kallona yake tayi, muna
hada ido na sake mayar da kaina kasa ina
yin murmushi sai yace "Please Piya. Ki
rufa min asiri ki dawo dai dai. Ni ban saba
da wannan ba gaskiya" nace "zaka saba
da ita ne ai a hankali" ya girgiza kai "no.
Ba zan saba da ita ba. Zan dai dawo da
Piya ta ko da karfi ne. Allah dai ya kaimu
jibi" a haka ya gaji da shiru shiru na ya yi
min sallama ya tafi amma ace zai sake
dawowa da dare ya kawo min sako.
Na tashi na koma gida. Already gidan mu
ya fara cika da yan'uwan mu da suka fara
zuwa daga Kano. Cousin din su Daddy da
muke kira da gwoggo Hauwa tazo tare da
yayanta uku da kuma surikarta. Matan
kanin baban su Daddy ma sunzo su biyu.
Kanwar babarsa ma wadda take kamar
kaka a wajen mu a yanzu ita ma haka ta
matsa sai da aka taho da ita tare da
matan yayan ta su uku tunda ita yayan ta
duk maza ne, Sauran yan'uwa kuma sai
washegari muke saka ran zuwan su,
Ina shiga tun a falo suka dasa tsokana ta, "'Amarya wanna sheki haka da kike yi
duk na amarcin ne?" "Amma kuma ta
rame fa" "tsoron auren kike ji?" "To ko dai
a fasa ne?" Na juya ya zabga wa wadda ta
fadi haka harara, abokiyar wasan mu ce
da ma, tayi dariya tare da fadawa goggo
Hauwa da take zaune a gefe "harara ta
tayi, wallahi goggo harara ta tayi" na
sunkuyar da kai kamar ba ni nayi ba na
zauna a gefen gwoggo nace "sharri zaki
yi min? Ai Allah yana kallo kuma zai saka
min" Hasina tace "ni ma na ga hararar fa.
Kuma yanzu ma daga gurin angon take, ai
na hango su sanda naje ba da sako waje"
goggo Hauwa tace "kika je bada sako ko
kika je tsegumi?" Ta juyo tana kallona
tace "wai so take ta ga wanda yafi
Mukhtar da har kika rabu da Mukhtar kika
aure shi" Salima da take kwance a gefe ta
tashi tace "ai kam dai in kyau ne yafi Yaya,
kuma yana da kirki sosai, ga kudi, baku ga
motar da yake hawa ba" Hasina ta saki
baki tace "lahh ka ga yarinya mai gudun
dangi? Nawa ya baki?" Suka sake yin
dariya sai gwoggo tace "ni kam ba zance
nafi son sa akan Mukhtar da yake da na
ba. Amma ina musu fatan alkhairi. Allah ya
sa albarka a gidan auren su ya sa mutu ka
raba" a hankali nace "Amen" Hasina ta
sake cewa "aah gwoggo wallahi Ameen
ta ce, ba zaki bari mu mu amsa ba?" Haka muka cigaba da zama a tare muna
ta hira, naji suna ta tambaya akan Safina
wai basu ganta ba ko sai gobe zata
shigo? Su a gain su tunda a garin take
aure ai ya kamata a ganta actively a cikin
shire shiryen bikin ba wai sai ranar taron
zata zo ba. A lokacin na kara fahimtar
cewa ba su san waye na aura ba kuma
bana jin ko sun ganshi zasu gane shi in
dai ba fada musu akayi ba. Watakila zasu
sani nan gaba. Watakila kuma akasin
haka.

Wata kila idan suka sani zasu san
complete labarin kuma su goyi bayana,
watakila kuma ba zasu fahimta ba zasu
zage ni. But in whatever case, I don't
care.
Anan muka ci abincin dare tare, wadanda
basa kusa ma duk suka dawo falon aka
hadu aka ci abincin tare, Esther wadda
already ta hada kayanta kamar ita za'a
yiwa auren ta na ta hidima da mu tare da
sababbin yan aikin da aka kawo su uku,
Bayan mun gana cin abincin na kira
Salima da Hasina da Hafsat muka tafi
dakina nace su taya ni hada kayana, Ko
kuma ince su hada min kayana, Dan zama
nayi kawai ina kallon su suna hadawa ina jin babu dadi a raina, dan lokacin auren
Mukhtar babu abinda na dauka a cikin
kayana dan ban ma yi tunanin zan yi
dadewar da nayi a gidan sa ba. Kayan
gurin Ammie gabakidaya na dauka dan ba
zan iya bayar da ko daya daga ciki ba.
Kayana kuma na dauki wadansu da nake
so sauran kuma gabaki daya nace
bayarwa zanyi. Ai kuwa su da suke gurin
su suka fara zaba, nace "idan kuka dauki
da yawa to babu ku a wadancan kayan"
Hafsat tace "wadanne kayan?" Nace "ba
zan fada ba, amma in dai kuka dauka da
yawa babu ku a wadancan" sai suka
rarrage, daga nan nace su fifftar su raba
wa dangi dan sun fi ni sanin dangin.
Ai kuwa haka suka sha rabo, gida gida,
duk wadda kaya na zasu iya yi mata sai da
ta samu. Sai na bar su suna rabon kayan
na tafi gurin Mommy na gaya mata kudiri
na "Mommy kayan can na lefe da aka
kawo daga gidan uncle Ahmad, ki rabar
wa da mutane, duk yan'uwa a raba a
bawa kowa, komai da komai, har
akwatunan" ta tsaya tana kallona sai na
daga kafada nace "babu abinda zanyi da
su Mommy, ga wannan lefen da aka kawo,
ga dinkunan da nayi, ga kuma kayan da
already nake da su". Ta gyada kai tace "shikenan, za'a bayar", Itama haka ta
zauna ta rabar da kayan tas, dangin uwa
da dangin baban Daddy kowa sai da ya
samu, ma'aikatan gidan mu both Kano da
Abuja, hatta masu gadi da drivers sai da
Mommy ta basu wani abu a ciki. Amma
bata bayar da kayan kwalliyar ba sai yace
in tafi da su gidan Muhammad saboda
baki yan uwansa in sun zo. Na amince da
abinda tace, sai ta hada da kayan
kwalliyar da kayan lefen da aka kawo daga
gidan su Muhammad da kuma kayana da
na hada na gida wadanda zan tafi da su ta
bawa su Salima Hassan ya kai su suka kai
min gidan Muhammad.
Ni dai tunda muka yi maganar kaya da
Mommy ban kuma bin ta kan su ba, sai
dai duk wanda yazo yayi min godiya sai
inyi masa murmushi kawai. Da dare
Muhammad ya dawo kamar yadda yace
zai dawo. Ina tare da Daddy ya kira ni
yace yazo yana waje a mota. Na dan j
faduwar gaba amma na danne na saka
hijab dina na fita. A motar na tarar da shi
a zaune a seat din driver sai na zagaya na
zauna a gefen sa, na gaishe shi yayi shiru
bai amsa ba sai na dago kai muka hada
ido na sake mayar da kaina kasa, ya kira
sunana "Safiyya" na dago kai da sauri dan
ba zan iya tuna ranar da ya kira sunana
haka ba. Sai ya juyo ya kama hannayena duk biyun ya rike "look at me" na sake
dago kai muna kallon juna "me yake
damun ki?" Na dan kirkiri murmushi "ni
kuma? Nothing fa. Kawai abubuwa ne dai
suka dan yi min yawa" ya girgiza kai "ban
yarda ba. Ba zaki fada min ba?" Na sake
mayar da ido na kasa ina jin kamar zanyi
kuka.
"Ba kya son rabuwa da Daddy? Shine
damuwar ki" nayi saurin gyada masa kai
tunda hakan yana cikin damuwata. Yayi
ajiyar zuciya "ba zaki rabu da Daddy ba
kinji? Insha Allah kullum zamu ke zuwa
muna gaishe shi. Nayi miki wannan
alkawarin. Ki saki ranki ki daina damuwa
kinji?" Na sake gyada masa kai sai yace
'to kiyi min hira. I really miss the sound of
your voice " na danyi murmushi nace "to
me zance? Dazu ma ba muni magana
ba" yace "nayi magana dai. Ni kadai nayi
magana ta dazun ma. Kuma na san gobe
ba lallai in samu ganin ki ba. Ko inzo in kai
ku gurin gyaran gashin?" Na girgiza kai
"muna da yawa ai, ba zaka ji dadin shiga
cikin mu ba. Hassan sai ya kaimu ko mu
dauki driver" ya dan yi murmushi "ko dai
kina kishin kar a gane miki miji?" Na
harare shi tare da kwace hannuna in
kishin nake yi ma ai babu laifi

Miji na mai kyau ne kuma ina son sa" yaji
dadi sosai sai ya saka dan yatsa ya dago
haba ta yana kallon cikin ido na for some
seconds sannan yace "kina da kyau sosai
Piya. Ina son ki sosai",. Na danyi murmushi
sai yace "I am glad ba za'a yi taron da
maza ba, yadda kike ta kara kyau din nan
bana so maza su ganki ballantana ace
kinyi kyalliya" na dan yi dariya "ohh and
you are calling me sarkin kishi ko?" Ya
daga kafada "I wasn't complaining ai. Ina
son kishin ki sosai. Yana kara kin
confirming kina so na" nace "to yanzu su
friends din naka babu abinda zaka shirya
musu kenan?" Yace
"kamar kin san da zu
muka gama rigima. Sunce wai ban
gayyace su daurin aure na ba ballantana
in shirya musu reception and I told them
ni ma ba'a gayyaceni daurin auren na wa
ba. Haka suka zauna suka tsuye ni wai
nayi musu karya nace kin mutu" na bude
ido "what! Yaushe kace musu na mutu?"
Yayi dariya "lokacin wancan daurin auren
ne suka dame ni da tambayar ya akayi ba
ke zan aura ba, and su ba su san irin
heartbreak din da nake going through ba
a lokacin, Ni kuma nace musu kin mutu"
dariya nayi sosai sai ya tsaya yana kallona
kawai yana murmushi. Sai kuma naga yayi
sauri ya dauko wata leda a baya ya miko min "Har na kusa mantawa, I bought you
chocolate slurry, irin wadda kike so" na
dan bude ido kadan sannan na bude ledar
na dauko dan karamin cup din ina kallon
sa sannan na kalli Muhammad "a hana ni
sha fa, kai fa kace min in ban daina sha ba
zan zama katuwa" ya dan daga kafada
"yau dai kadai. Daga yau ba zaki kara sha
ba" na bude cup din na dauko dan
karamin spoon din da yake makale a jikin
cup din na diba na saka a bakina ina jin
dadin narkakkiyar chocolate din da aka
chakuda da madara kuma ba'a saka sugar
ba, na kwantar da kaina a jikin motar tare
da lumshe ido na memories din rayuwata
da Muhammad yana dawomin kaina. Na
bude ido naga idon sa yana kaina, na sake
diba da spoon din na kuma sha sai yace
"babu tavi ko?" Ban ce komai ba na dibo a
spoon din na mika zuwa bakinsa. Mai
makon ya sha sai ya kama hannu na ya
dawo da shi baya ya mayar da spoon din
cikin cup din sannan ya saka dogon dan
yatsa na a cikin chocolate din ya
dangwalo sannan ya kai bakin sa, na
lumshe ido ina jin wani irin feeling na
yadda yake yi wa finger din nawa a cikin
bakinsa, nayi kokarin karbe wa amma yaki
saki, sai ya sake mayar da shi ya kuma
dangwalo wa ya sake mayarwa bakin sa,
"hmmm" yace "chocolate din nan akwai dadi fa" ya sake kokarin mayar da yatsan
nawa cikin cup din for the third time sai na
janye cup din, "zaka shanye min ai'" na
fada trying to make him stop, yace "rowa
ko? To shikenan, ki rike taki chocolate din
in rike tawa" ya fada tare da mayar da
hannuna zuwa bakinsa. Sai da yabi
fingers din daya bayan daya kamar wanda
ya samu sweet din gaske, sannan ya juya
hannuna ya manna min kiss a tsakiyar
tafin hannun. Nayi saurin janye hannuna
tare da boye shi a bayana trying to hide
yadda yake saka ni nake ji. Ya sake cewa
"rowa ko?" Na mika masa cup din gaba
daya,
"gashi na bar maka" yace "taki ce
wannan ai, ki bani nawa kawai" na girgiza
kai sai yace "okay to bana son wannan
din, ki sha kayar ki kawaj" na dauki spoon
din na cigaba da sha da sauri da sauri, ina
son in rage wa zuciya ta bugawar da take
yi. Sai da nayi nisa da sha sannan ya
karbe cup din daga hannu na da hannun
sa daya, daya hannun kuma ya kamo
fuska ta ya juyo dani gare shi and
unexpectedly ya hade bakin mu guri daya.
Sanda ya sake ni babu sauran taste din
chocolate a bakina, ya shanye tas, abinda
ya rage min a bakin kawai taste din sa ne,
wanda nake jin sa kamar ba'a iyakacin
bakina kadai ya tsaya ba, kamar dukkan
jijiyoyin jikina ya zagaya. Na bude idanuwa na da suka yi min nauyi na ssuke su a
kansa, har lokacin fuskarsa tana kusa da
tawa, idanun sa a cikin nawa, murmushi
mai fadi akan fuskar ta sa yace "nima na
sha tawa" sannan ya daga min gira yace
"and mine is sweeter" na tura baki tare da
saka hannu ina goge lips dina nace "kai
kazami ne Allah kuwa" ya danyi dariya
"kar ki damu, da sannu zan jaki zuwa
class dina, watakila ma ki fini kwarewa"
na murguda baki ina magana kasa kasa
sannan na

bude kofar motar na fita nace masa "kayi
wa kanka, na fasa yin hirar da kaj" na rufe
kofar sai kuma na sake budewa na dauki
cup din chocolate dina nace
"kuma ba
zan bar maka chocolate dina ba" yayi
murmushi "na sha tawa ai" har zan rufe
kofar sai yace "hey Piya" na tsaya sai
yace "I love you" na danyi murmushi ina
jin har na huce nace "I love you too Baby".
Na rufe masa kofar amma sai ya cigaba
da zama a motar har na shiga cikin gida
sannan ya tafi,
Na danyi kokarin calming kaina down a
compound amma shima da mutane dan
haka na wuce cikin gida, ina shiga sai nayi
sauri na wuce kitchen na wanke fuskata gabaki daya dan duk dankon chocolate
take yi, sai kuma na zauna a kitchen din
na cigaba da shan chocolate dina ina ta
zabga murmushi ni kadai.
Washegari da sassafe muka tashi muka
shirya zamu tafi gurin gyaran gashi, na
shiga yiwa Mommy sallama na tarar har
lokacin rabon kaya take tayi, har zan fita
sai ta kira ni "Safiyya, ni kuwa yaron nan
bai yi miki maganar yadda yake ciki akan
Safina ba?" Na danyi shiru ina kallon ta,
trying so hard kar in nuna bacin rai na, sai
kuma kawai na girgiza mata kai nace "a'a.
Bai ce min komai ba" sai nayi sauri na fita
daga dakin kar ta sake yi min wata
maganar. Ni bana son jin duk wani abu
daya shafi Safina da Muhammad, bai taba
yi min maganar

102 / 113