SAFIYYA BOOK COMPLETE MAMAN MAMA.txt

Author :  Maman Mama Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   104 / 113

309K to 312K   out of 336.6K words

a turaka?" Ban amsa ba dan
banajin zan iya amsawar, numfashin sa
kawai nake shaka. "in gaya miki? In nuna
miki?" Na girgiza kaina da sauri "bana son
gani. Bana son ji. Ni dakina zan tafi" yace
"hmmm" tare da kissing hancina da kuma
haba ta, cikin dauriya nace masa "kai ma
hmmm" sai yayi dariya, "ba kin ce kina
son sanin ma'anar hmmm dina ba?" Nace
"bana so, na yafe, Ka rike ma'anar
abinka" dariya ya danyi tare da goga min
sajensa a gefen fuskata "ko ba kya son
sani yau sai na sanar da ke" ya fada yana
sake dawo da bakinsa kusa da nawa. Na
matse lips dina na shigar da su cikin bakina sai ya sake yin dariya tare da
mintsini na a cheek dina, na dan yi kara
"har da mugunta kuma? Daddy ya ....
Ban gama ba ya mayar da maganar tawa
ciki ta hanyar hade bakin mu.
Sai da yayi mai isar sa sannan ya janye
bakinsa, ya tsaya yana kallona idanuwana
a lumshe, sai ya mayar da bakin sa kunne
na yace min "I have got a favorite thing to
do yanzu. Kissing you is now my favorite
thing to do" na bude ido na ina kallon sa
sai ya kama hannuna "come, na siyo miki
kaji, kar ki ce nayi miki rowa".
Ya jani ya zaunar da ni akan
hargitsatstsen gadon sa, sannan yace
"ina zuwa, minti biyu, kar fa ki gudu" duk
da halin da zuciya ta take ciki sai da na
danyi dariya. Ya fita da sauri ni kuma na
cigaba da zama ina karanto dukkan
adduoin da na ke ganin zasu vani kwarin
guiwar fuskantar mijina. Kullum in ana
bayanin toro in aka ce mutum yana jin
kayan cikin sa suna rawa bana iya gane
wa, amma yanzu na gane, yanzu nima
nawan rawa suke yi sosai, hatta hakora na
karkarwa suke yi, Babu abinda yake yawo
a kaina sai azabar da Mukhtar ya ganar da
ni, sai irin tsoron da naji a lokacin da yake
gana min azabar. Na sani cewa Muhammad ba Mukhtar ba ne ba, na
kuma yarda cewa ba zai cutar da ni ba.
Amma kuma na kasa cire tsoron daga
zuciyata.
Ya dawo hannayen sa dauke da ledoji
manya guda uku, ya ajiye su a gefe na
yana kallon dakin yace
"gaskiya naji
kunya da yawa" sai ya sunkuyo kawai naji
ya daga na chak, na bude ido da sauri ina
kallon sa sai naga ya ajiye ni akan kujera
sannan ya juya ya fara gyara gadon, ina
kallon sa har da dauko turare ya fesa a
beddings din, gyaran na shi dai daga gani
ba iyawa yayi sosai ba irin yadda nake so,
amma dai ya gyara.

Sai kuma ya kwashe tarkashen kayan sa
ya shiga da su ciki, ya fito yana sake
kallon dakin sannan ya kalle ni yace "yayi
ko?" Ban amsa masa ba sai ya karaso
gaba na yace "sallah ko kaza?", A hankali
nace "ni sallah zanyi. Ni ba zan ci kaza ba,
Nina koshi" ya danyi dariya
"kwadayayyiya, ranar nan ma haka kika ce
ai, sai gashi har kin fi ni ci" na dan harare
shi kadan. Sai ya wuce zuwa toilet dinsa
yayi alwala, ni ma yana fitowa na tashi na
shiga, na jima a cikin toilet din ina kokarin calming kaina down sannan nayi alwalar
nima na fito. Na tarar da shi ya shinfida
mana wani karamin carpet akan carpet
din da yake dakin already, naji kamshin
dakin ya chanja kamar ya kara wani
turaren na daban mai dadin kamshi, "bani
da hijab" na ce masa, "bara inje daki in
dauko" ya girgiza min hannun sa "uhm
uhm. Ki zauna anan inje in dauko miki" na
bude hannu na, "to ai baka san inda yake
ba" da kyar ya yarda muka tafi tare, ban
sani ba ko tunani yake yi zan gudu idan na
tafi ni kadai?
Na dauko hijab dina na hada da kayan
bacci na da sauran abubuwan da nake
bukata idan zanyi shirin kwanciya. Kamar
wadda zanyi hijira zuwa wani garin. Muka
koma dakin nasa na ajiye kayan da na
debo sannan na saka hijab dina muka
tayar da Sallah. Bayan mun idar shi yayi
mana adduoin masu tsaho, nayi mamakin
yadda ya juya bakinsa yana jero mana
adduoi cikin karshen larabci, sai naji
kamar yaren sa ne, muka shafa sai ya
tambaye ni idan ina da wata addu'a da
zanyi mana sai na daga hannu na a zuciya
ta na roki Allah ya yaye min wannan
tsoron da nake ji sannan na shafa, ya
shafa shima sannan ya yambaye ni "mai kika roka mana?" Na girgiza kaina "shirri
ne" ya bude ido sirri? A tsakanin mu da
ma akwai sauran secret?" Na sunkuyar da
kaina ban ce komai ba. Ina jin sa yana
cigaba da kallo na sai na dago kaina na
kalle shi cikin ido nace "Yaya Muhammad"
bai amsa ma amma gabakidaya attention
dinsa yana kaina, a hankali cikin karyewar
murya nace "tsoro nake ji, I am scared
Yaya Muhammad" bai ce min komai ba sai
naga ya sunkuyar da kansa yana kallon
kan cinyata, nima na kalli inda yake kalla
sai na ga hannayena da suke kan chinyar
sun karkarwa kamar wadda take jin
tsananin sanyi, nayi sauri na rike su da
junansu sai ya matso ya dora nasa
hannayen akan nawa ya rike gam har sai
da suka daina karkarwar sannan yace "I
know. Na san kina jin tsoro Safiyya, sai dai
kuma bayan haka na san wani abu daban,
na san kina sona kamar yadda nima nake
son ki" ya gara zaman sa sosai sannan ya
cigaba "kin san wani abu? ranar da kika je
office dina a MD kika gaya min cewar kina
da aure, I was devastated a lokacin,
maybe tashin hankalin da na shiga shi ya
hana ni ganin gaskiya, amma bayan na
koma gida, bayan na nutsu nayi tunani sai
na tuno da fuskar ki a lokacin da kike yi
min maganar, na kuma tuno da yadda kika furta kalaman, sai kawai naji na fahimci
wani abu, na fahimci kina so na sosai,
wannan son kuma shine abinda ya bani
hope, shi ya rike ni ya hana ni hakura da
ke inyi moving on, ya hana ni giving up.
Tun daga lokacin kuma har zuwa yanzu
soyayyar ki ita ce take jagoranta ta a
dukkan decision dina, yanzu ma kuma ita
ce hope dina. You have fear, Yes, but you
also have love".
Ya mike tsaye tare da mikar da ni tsaye
nima sannan ya zaunar da ni a bakin gado
sai ya tafi gurin ledojin da ya shigo da su
ya dauko wata karama ya dawo kusa da ni
ya zauna ya bude ta ya dauki wasu boxes
guda biyu kanana tare da wasu takardu,
ya ajiye takardun sannan ya bude box din
farko ya nuna min "look at this beauty" na
kalli abinda yake ciki, a take na bude baki,
ya danyu dariya yana jin dadain yabawa
abinsa da nayi. Zo be ne na diamond, anyi
mass rings din sirara guda uku amma
saman su an hade shi da dunkulallen
diamond mai shape din heart. Ya fito da
shi sannan ya kama hannuna ya saka min,
yayi dai dai a danyatsa na kamar an
gwada, kamar ya san me nake tunani sai
yace "na karbi measurement dinki ne a
wajen matar da ta hada lefe. Do you like it?" Na sauri nace "like it? I love it Baby.

Thank you" na fada tare da daga shi ina
kallon sa sosai, a cikin heart din anyi
design din rose flower, petals dinta
different colors kuma na lura kamar
colours din nasu yana chanja shade idan
aka haska shi, yayi murmushi ya sake
kama hannun nawa yana shafa yatsun
yana kallon ring din sannan ya kai shi
bakinsa ya sumbata yace "I may not have
a gold company and all the rest, but I do
have love and I am today giving you all of
my heart together with all of my love, as
far as love between couple is concern. I
want to share my parents, my siblings and
all of my family with you. I want to share
my life with you. And I promise you that I
will work hard to give you all that you
deserve. And I promise you, insha Allah,
that you will never shade sad tears again,
sai dai in abinda yafi karfina, and ko da
yafi karfin nawa ma, I promise you that we
will cry together, wipe away each other's
tears, and pick up each other. We will
walk through the journey of this life
together. You will never be alone again",

Na fara sheshshekar kuka ina kallon sa "Muhammad……Yaya Muhammad.......
have been through a lot a rayuwata, zan
iya cewa tun kafin a san za'a haife ni
rayuwa ta take dabaibaye da tragedies iri
iri. At a point na dauka cewa ny family is
cursed. Amma yanzu.... Yanzu da nake
ganin ka a gaba na..... Sai na fahimci cewa
kai ne sakamakon da Allah yayi min a
duniya for all that I went through. Kai ne
light din da ta jira ni at the end of the
tunnel. Yanzu na fahimci duk abinda ya
same ni Allah yana jaraba nine dan yaga
idan na cancanci ya bani kai. Thank you.
Thank you for loving me. I love you so
much Baby na".

Na fada kirjin sa ina cigaba da kuka na.
Sai da ya bar ni na danyi kadan sannan ya
dago ni yana kallon fuskata yace "next
year by now, babyn mu yana kuka ke ma
kina kuka. Da ana bayar da sarautar kuka
da na nada ki" na harare shi tare da magana
kasa kasa "ni sai na yi kuka na wallahi",.
Ya kalli daya box din da take ajiye yace
"baki saka min nawa ring din ba fa"
na dauka da sauri na bude ina kallon
nashi zoben, irin nawa be sak sai dal shi
nashi anyi da azurfa ne ba diamond ba,
Sannan instead of rings duda uku nashi
mai kauri ne guda daya, kuma rose din
cikin nashi bata colours kamar tawa. Na
kama hannunsa na hagu na cire zoben da
yake jikin danyatsansa na hudu na saka
masa zoben, yayi mass kyau sosai ya kara
haska hannun. Ya miko min hannun tare
da hade rai "and now you kiss it". Na
makale kafada "kai komai kiss komai kiss"
yace "au haka kika ce? To wallahi sai kinyi"
ya taso kaina kamar zai hau jiki na sai na
yi sauri na kama hannun nayi kissing na
mayar masa da kayan sa, yace "Allah ya
taimake ki yarinya".

Ya mike tsaye "yanzu kuma saura in baki
kaza ki ci." Na makale kafada "ni fa na gaya
maka ba zan ci ba" ya wani table ya kawo
gaba na "to shikenan, ba zaki ci ba ni zan
baki a baki" ya dauko another leda ya bude,
kaji ne a ciki ba zan iya cewa ga adadin su
ba saboda anyi pieces da su, ashe har da
guzurin plate din sa a cikin ledar, ya zuba a
cikin plate din sannan ya dora akan table din
sau kuma ya fito da wani drink da ban taba
gain irinsa ba ya zuba a cup ya ajiye a kusa
da plate din sai kuma ya bude daya ledar, na
lura fruits ne a ciki, sai yace "na manta ban
dauko wuka ba" nace masa "ni fa ba ci zanyi
ba" bai nuna yaji abinda nace ba sai ya durkusa
a gaba na ya dauki tsokar naman guda daya ya
kawo baki na "bude. Bude mana" na bude a
hankali ya tura min a ciki "sai kinci naman nan
yau ko dura zanyi miki. Kin san dadin sa kuwa?
To wannan yafi na ranar nan dadi" naji dadin
masa kuwa, amma ni yanzu ba ta nama nake
yi ba. Kalamansa su sassauta min toro na amma fa
yana nan babu inda yaje, sannan kuma a cikin kalaman na sa banji inda ya am bata cewa ba
zaiyi ba, sai ma zancen Baby da ya yi min. Haka
ya ringa cusa min naman nan, sannan ya dauko
drink din ya kawo bakina "sha wannan. I bet duk yawon kasashen ki baki taba shan wannan
ba" na kurba, yayi dadi sosai, na karba na kara
sha yace "kinji da dadi ko?" Sai na gyada kai na
zuba wani na mika masa. "'yayi dadi. Na gode. Na koshi. Kai ma ka sha" ya karba ya shanye
sannan ya ajiye cup din tare da mike wa.
yace "yau yaki za'a yi in gaya miki,
between your fear and my love. Zamu ga
wanda zai ci nasara. Ni kuma na san nine
da nasara, Tunda na san love is the greatest weapon of all. Da mana jima ina share hanya, yanzu filin yaki kawai zan shiga ko a mutu ko a yi raj" yadda yayi
maganar sai ya bani dariya, amma kuma ban dara din ba dan babu dariya a tare da ni.

A dai dai lokacin ne kuma abin ya faru.

Ina zaune akan gado ina facing kofar
shigowa, shi kuma yana tsaye a gaba na
yana kallona ya juya wa kofa baya. Idona
yana sunkuye a kasa, amma duk da haka
sai na ga kamar kofa ta motsa duk kuwa
da cewa babu kara. Nayi sauri na dago
kaina and I saw him, a tsaye a bakin kofar,
muna hada ido ya karasa shigowa ciki da
sauri sannan ya ja kofar ya rufe ya murda
key din sannan ya zare key din ya saka a
aljihu. Mukhtar.

Kusan abinda ya faru ya faru ne in
seconds, a take na kwalla kara muryata
da fuskata cike da toro, dukkan tsoron
da nake kokarin dannewa ya ninninka
kansa sau babu adadi. Muhammad ya
juya da sauri saboda ganin inda nake kallo
da kuma razananniyar karar da nayi. Cikin
bazata Mukhtar ya damki wuyansa
sannan ya hankada shi da karfi ya buga
shi a jikin bangon dakin, Kansa ya bugu a
jikin bangon, dama gashi bai jima da jin
ciwo a ka ba, ya dafe kan yana kokarin
regaining kansa, wannan ya bawa
Mukhtar damar binsa ya kuma damkar
makogwaronsa tare da matse shi a jikin
bango da dukkan karfin sa.
Muhammad yana da girma, dai dai girman
da namiji matashi mai irin shekarunsa ya
kamata ya samu, Mukhtar ba sa'an sa
bane ba, sannan kuma Mukhtar kato ne,
tun yana yaro dama Mukhtar ba karami
bane ba dan haka yanzu za'a iya kiran sa
da katon mutum. Na sake kurma wani
hun tare da yin tsalle na tsallake table din
gaba na nayi kan Mukhtar ina dukan sa da
dukkan karfin da Allah ya bani. "Ka sake
shi.…. Ka sake shi ....." Na cigaba da ihun
a yayin da Muhammad ya samu ya
banbare hannun Mukhtar da kyar daga
makogwaronsa. "Run........" Yace min "ki
shiga toilet ki rufe kofa" ya kara fada a
lokacin da Mukhtar ya murde masa
hannun sa zuwa bayan sa sannan ya sake
hada shi da jikin bangon kansa yana sake
buguwa".

Tsoron Mukhtar da nake ji ya rinjaye ni da
farko, na ruga toilet da gudu kamar yadda
Muhammad yace min amma kuma sai
soyayyar Muhammad ta hana ni shiga
toilet din, In na shiga na tsira dan na
kofofin gidan suna da kyan da Mukhtar ba
zai iya balla su ba, Amma kuma
Muhammad fa? Zai iya yi masa komai
musamman idan ya kasa samu na, sai na
juyo a guje kamar yadda na tafi a gujen

amma sai na fara bude window nayi ihun
neman taimako sannan na dawo na fara
daukan duk abinda zan iya dukan Mukhtar
da shi ina kwada masa.

Dakin babu wani tarkace a ciki, dan haka
sam babu wani abu da zan kira makami.
Naji ina missing wukar da take kasan
gado na a gidan Daddy, na kuma jinjina
hikimar Annabi da ya shawarce mu mu
ringa ajiye makami a dakunan mu. "Run
nace miki. Take my phone and lock
yourself in the toilet. Then call someone"
na girgiza kai ina jan hannun Mukhtar da
dukkan karfina "gurina na kazo. a sake
shi. Don't hurt him. Ni kai min duk abinda
zaka yi min ka rabu da shi" na fada ina
hada masa da duka da yakushi da duk
abinda zan iya, na lura a jike yake da
gumi, na lura har wan wari yake yi. Ya
saka hannu daya ya ture ni na fadi kasa,
Muhammad ya zaburo "don't touch her!"
Ya fada a zuciye, Mukhtar ya sake mayar
da shi ya buga a jikin bango "or what? In
na taba tan me zakayi? Mama's boy. In na
taba tan babu abinda zaka iya sai dai ka
ruga gida da gudu kana kuka kaje ka fada
wa maman ka. Stupid, Shashasha, Ban
taba ganin sakarai irin ka ba. Duk
shekarun da kuke tare, duk kyawun nan
na ta, na dauka you already had her ashe
kai sakarai ne, wata kila ma baka iya ba.
Maybe kana jira sai an koya maka ne a
gida"

Muhammad yace "say whatever you want
to say, maganar dai guda daya ce, ba ta
son ka ni take so, shine kuma abinda yake
damunka. Shine abinda duk ya jawo maka
halin da kake ciki" ran Mukhtar ya sake
baci "karya kake yi, tana so na. Ni ta zaba.
Da kanta ta zabe ni tace ni zata aura. laifi
ne kawai nayi mata. Fushi ne kawai take
yi. She is mine, mine, mine, ni kadai. And I
am here to take her. Zan tafi da ita in bata
hakuri mu cigaba da zaman mu"
"delusional" shine abinda naji Muhammad
ya fada masa.

Ya sake shi ya matsa baya da sauri, daga
gani kasan ba'a cikin cikakken hankalin sa
yake ba. Muhammad ya durkusa yana
mayar da numfashi. Sai kuma Mukhtar ya
juyo yana kallona da irin kallon da na saba
gani a idonsa sanda ina gidan sa, kallon
sha'awa "or maybe I should have her
here" na mike tsaye da sauri, ya juya yana
kallon Muhammad yace "I will have her
here a gaban ka inga abinda zaka yi a kai".

Bacin ran da na gani a fuskar Muhammad
ban taba gain irin sa ba a duniya, ban
taba tunanin yana da irin sa ba. A fusace
yayo kan Mukhtar, Mukhtar ya rike
hannun da ya kai masa duka da shi ya
hana shi zuwa jikin sa, nan take suka
cigaba da gumurzu. Na dauki wayar
Muhammad a kan table kuma sai na rasa
wa zan kira, wa zan tayarwa da hankali.
Na sake lekawa da taga na cigaba da ihun
neman taimako, na tabbatar security na
suna waje, na kuma tabbatar sun ji ni,
amma tashin hankali na daya shine tun
sanda muka sauka kasa da niyyar kallon
gida Muhammad ya rufe kofa, duk kuma
inda muka shiga muka fito sai ya rufe
kofa. Dan haka kofa nawa zasu bude kafin
su shigo inda muke. Na kuma tabbatar
sun kira duk wanda ya kamata su kira,
maybe sun kira police ma already. Na
tuna bindigar da suka bani, tana can
dakina a cikin safe din gwala-gwalai na na
wajen Ammie,

Amma kuma sai naga Muhammad ya fara
bani mamaki a fadan nasu, a da in za'a ce
min za'a yi fada tsakanin Muhammad da
Mukhtar ba zan dauka cewa Muhammad
zai lasting minti biyu a hannun Mukhtar
ba, amma sai naga yana neman ya gagare
shi. Na fahimci Mukhtar kokari yake yi ya
hada hannayen Muhammad ya rike da
hannu daya dan ya samu damar shake
mass wuya da daya hannun, so yake ya
sumar da shi, may be a lissafinsa sai ya
dauke ni ya gudu da ni. Amma
Muhammad ya hana shi wannan damar.

Daga wancan bangon su koma wannan
bangon har suka fadi a kasa, Mukhtar
yana saman Muhammad yana ta kokarin
kama makogwaronsa, a lokacin naji
alamar an shigo cikin gidan, sai dai ban
san a wanne floor suke ba, na ga wani
frame a cikin bango na hau kan table na
ciro shi na buga wa Mukhtar a ka amma
ko gezau bai yi ba.

A lokacin na lura da abinda Muhammad
yake yi, kafafuwan sa da suke free yayi
amfani da su ya bude kafafuwan Mukhtar,
sannan cikin dabara

104 / 113