Author : Maman Mama Category : Romantic Hausa Novels
aka ce Ameen, ta juya zata
tafi, na bita da kallo sai idona ya sauka
akan Daddy a can kofar shiga part dinsa,
yana zaune akan wheelchair din sa idonsa
a kaina fuskar sa dauke da murmushi. A
hankali nace masa "thank you" ta hanyar
motsa bakina yadda babu wanda yaji
sound din sai shi da yake kallo na. Ya
gyada kai sannan ya daga hannun sa yayi
min thumbs up sai kuma ya juya ya koma
cikin part dinsa ya rufe kofa.
Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️🩹Safiyya❤️🩹
Episode Sixty One: Selfishness
Not Edited
Him👳🏻♀️
One week ago
Idan yace a cikin nutsuwa yayi wannan
sati to tabbas yayi karya, daga shi har duk
wanda yake tare da shi ya tabbatar cewa
ba'a nutse yake ba. Sau da yawa mutanen
da suke tare da shi sukan tambaye shi
"are you okay?" Sai dai ya gyada musu kai
kawai ya sharar da maganar dan baya son
yin karya kuma baya son yin bayanin
abubuwan da suke damun sa din.
Na farko akwai labaran da Safiyya ta bashi
na gaskiyar abinda ya faru da ita, gaskiyar
abinda ya jawo ta rabu da shi a wancan
karon. Zai iya cewa tunda ya zo duniya bai
ta ba jin abinda ya daga masa hankali ba
irin wannan maganar, wannan tashin
hankalin ya janyo har likita ya gwada jinin
sa kuma ya tabbatar masa da cewa yana
gab da samun cutar hawan jini,
Sai na biyu kuma fahimtar da yayi cewa
duk maganganun da suka yi da Safiyya
Daddyn ta ya gansu kuma ya ji su,
wannan ma ya saka shi cikin damuwa dan
bai san wanne mataki Daddyn zai dauka
akan abinda yaji kuma ya gani ba. Will he
be satisfied cewa ya cancanta ya bashi
yar sa kamar yadda ya fahimci Safiyya
tana saka rai ko kuma zai raba su ne for
the second time. Ian kuma hakan ta
kasance anya kuwa zuciyar sa zata iya
dauka? Anya?
Sai dai kamar yadda Safiyya tayi shima sai
yabi hint dinta, sai ya sanar wa da
iyayensa duk biyun cewa ya hakura da
auren Safiyya tunda basa so, amma kuma
ba wai dan shi baya so ba, ya kuma nuna
musu irin damuwar da wanna hukunci
zai jawo masa, sannan kuma sai ya cigaba
da addu'a ba dare ba rana akan fatan
Allah yay guiding iyayen na sa su zaba
masa abinda yake mai alkhairi a gare shi.
Abu na uku kuma da ya dame shi a cikin
satin shine yadda Mama ta rufe idonta
tace ya tattara matarsa su koma gidan su
ta gama jinyar su. Haka yana ji yana gani
ya dauke ta a mota da kayan ta ya kai
gida. Dadin da yaji a wannan bangaren daya shine yadda Safinan ta dauke mass
wuta gabadaya ko kallon inda yake bata yi
ba tunda ta shiga motar har ta sauka, shi
kam sai yaji hakan yayi masa dadi sosai.
Suna sauka kuwa kowa ya kama gabansa.
Abu daya ne yake kwantar masa da
hankali a duk wadannan al'amuran, shine
waya da Safiyya. In suna waya manta wa
ma yake yi da kowa da komai ballantana
har ya tuna da wasu problems da suke
tattare da kowa da komai din. Duk da son
da yake yi ya ganta amma haka ya hakura
saboda babu dama. Duk kuwa da damuwar da yake ciki haka ya daure ya ke nuna mata bashi da damuwa dan baya son taji damuwar sa tai breaking down.
Shine namiji dan haka shi zai zama
strength din ta
Sanda ta bashi labarin zuwan abban sa
gurin Daddyn ta yayi mamaki dan Abban
bai ce masa komai akan hakan ba. Ranar
ma bayan sun gama waya haka ya tafi
gida yayi ta zama ko zai ji abban ya ce
masa wani abu amma sai yaji shiru babu
bayani. Ranar kuma da ta gaya masa
abinda Daddy yace mata akan ya zabar
mata mijin aure sai ya nuna mata yana
murna, ya nuna mata yana tunanin shine
wanda Daddy din ya zaba, yayi hakan ne
dan va qa alamar zuciyar ta cike take da doubts amma kuma a zahirin gaskiya ta sa zuciyar ta fi tata raunana akan lamarin
Sai ya ga kuma hakan ya yi lifting spirit
dinta sosai ta kuma dan saki jikinta suna
cigaba da faranta wa junan su rai but
kowa a cikin su akwai doubt din shi.
His second major concern aside not
having Piya is what to do with Safina.
Safina have been like a thorn in his heart
tunda ya san ta ya san wacece ita, bai
taba tunanin zai iya wulakanta mutum
kamar yadda ya wulakanta Safina ba, bai
kuma taba tsammanin akwai macen da
zata dauki abinda Safina ta dauka daga
gare shi ba. She did everything she did
saboda tana sonsa, or rather because she
is obsessed with him, dan shi bai yarda
abinda take ji a kansa soyayya ce ba. At
the end kuma, she lost everything.
Wannan shi yasa yake jin tausayin ta a
kasan ransa, musamman bayan tayi
miscarriage, duk da cewa ba da ne ta
haita ta kuma rasa ba amma ya san a
matsayin ta na uwa already ta so abinda
ya zauna a cikin ta, Wannan ya sa yake daga mata kafa yanxu sosai, ya daina yi mata kallon wulakanci
¡ya kuma daina gasa mata bakar magana,
ya kan shiga gurin ta kullum ya dauki kudi
ya bata ya kuma tambaye ta in akwai
abinda take so. Sai kuma ya fahimci ta
fara daukan hakan a matsayin wani abu
daban, har ta dawo da yi masa girki
wanda tun a ranar farko da ta yi masa ya
gaya mata ta daina "ba ci zanyi ba, barnar
abinci kuma babu kyau" hakan ya sosa
mata rai sosai har ta zubar da kwalla ta sa
ya kuma jin tausayin ta but he stood his
ground, any na farko anyi na karshe,
yanxu kaffa kaffa yaje yi da sha ko cin duk
wani abu da yake gidan dan gudun kar a
kuma, kar ta kara samun damar yiwa
rayuwar sa illa. Sai dai kuma Safina wata
halitta ce wadda a duk lokacin da kaji
tausayin ta sai tayi wani abun da zai saka
kaji tausayin kanka for jin tausayin ta. Ya
fahimci rawar kafar da take tayi a kansa
tunda ta fahimci ta fara samun sassauci a
gurinsa, kwalliyar ta dawo, saka matsatstsun kayan sun dawo, amma shi yasan ba zai iya bata abinda take so ba, ba zai iya ba, wannan shi ya sake tuna
masa cewa dole ya san yadda zaiyi ya
rabu da ita as soon as possible dan idan
ba haka ba zata jashi zuwa wuta for not
fulfilling her sexual desires as her husband,
A bangare daya kuma har yanzu bai cire
Mukhtar a ransa ba, Safiyya tace yayi
mata alkawarin ba zai taba shi ba amma
ko a lokacin bai yi alkawarin ba, kuma
baya jin zai iya. Wani irin rage yake ji a
ransa a duk lokacin da ya tuna da shi. Ya
san kuma rage din da yake ji just need a
little push zai yi exploding, push din kuma
might be as little as seeing Mukhtar din.
anar Monday yaje gidan su kamar yadda
ya saba yi duk sanda ya tashi daga aiki,
sai dai tun a waje ya ga motar Uncle Faruk
a harabar gidan su, bai ma san uncle din
nasa ya zo gari ba dan haka ya shiga cikin
gidan da murnar sa dan yayi missing din
shi. Amma sai dai yana shiga ya ga
Mommy (his grandma) a zaune a falo tare
da Abba da Mama da kuma shi uncle
Faruk din. Ya kara fadada murmushin sa,
ba zai iya tuna ranar da yaga Mommy a
gidan su ba, bata zuwa sai dai su je
gurinta,
"Matar" ya fada da murmushi "yau auren
ne ya kawo ki har gidan nan? Ko biko kika
20 dan kinga kwana biyu ban leka kin
ganni ba?" Ta watsa mass harara "ohh
Wali nan kai namiji ne? Namijin da har za'a
y) biko idan yayi yaji?" Uncle Faruk yana dariya yace "maganar gaskiya dai Mommy bikon kika z0, kinga kyakkyawan saurayi kim kasa zama sai da kika biyo shi har gidan su" ta tabe baki "ina abin yake?
Zama kyawawa ai sun kare. Tun da mijina
ya mutu babu wani namiji da zai burge ni
anan duniya".
Gidado ya karasa gaban su yana jinjina
soyayyar Mommy da marigayi Muhammad
Dikko. Babu yadda za'a yi ayi magana da
ita bata saka shi a ciki ba. Ya durkusa ya
gaishe ta amsa tana kare masa kallo daga
kasa har sama, sai kuma ya juya ya gaishe
da Uncle Faruk amma sai uncle din ya
mike ya jawo shi jikin sa ya rungume,
Gidado ya lunshe ido yana jin zuciyar ss
tana yi masa dadi, yana son yan'uwan sa
sosai.
Har ya koma ya zauna Mommy tana bin sa
da kallo, sai da ya zauna sannan ya kalle
ta tare da daga mata kafada "what?" Bata
amsa masa ba sai ta juya gurin Abba
"gashi nan ai abinda na gaya muku tun
ranar nan kuka mayar da magana ta wasa,
jibi yadda matar can ta zuke yaron nan,
kunga yadda ya koma kuwa? Haka
gidadon yake? Yaro ya kare gabakidaya ya
lalace maimakon ace yayi kiba yayi
annurin aure amma shi sai bushewa da
naga yayi * Mama tace "Mommy kin manta bashi da lafiya ne? Accident fa yayi, har yanzu dinkin da aka yi masa a kansa bai gama warke wa ba, daga baya
kuma ya kwanta rashin lafiya again"
Mommy tace "dama haka zaku ce ai. To
waye ya saka yayi accident din? Ai
Maimoon ta gaya min komai abinda ya
faru, kuma waye ya saka ya fara rashin
lafiyar? Ba damuwa aka ce tayi masa
yawa ba? Me zai saka shi damuwa in da
yana samun kwanciyar hankali da iyalin
sa? Gaskiya da sake. Ai na ga ba kwa daukan abin da
muhimmanci shi yasa nace auta ya kawo
ni har gidan naku dan ku fahimci
muhimmancin magana ta" Abba yace
"Mommy rashin lafiya ai daga Allah ne ko?
Ai wani baya saka wa wani rashin lafiya"
ta harare shi tace "Allahu Akbar. Mai
karatu na gaba" ta nuna Mama "ke zaki
dora daga inda ya tsaya? Aya zaki jawo
min ko hadisi?" Mama ta girgiza kai da
sauri sai uncle Faruk ya yi dariya, Mommy
ta juya ta watsa masa harara sai ya dauke
kansa gefe yana kunshe sauran dariyar
sa. Mommy ta cigaba "magana daya ce
nazo da ita, Yaron nan aure za'a sake yi
masa. Ga jikoki nan kyawawa Allah ya hore min su, in ma baya so a cikin su yaje ya zabi wacce yake so a waje ya kawo in dal tayl a aura masa ita. Ba zan zauna ina kallo a cutar min da jika ba wallahi. Haka
kawai ba zai kare yarintar sa cikin wahala
dan ya faranta muku ba".
Abba ya yi gyaran murya ya fara magana
cikin lallami dan ya fahimci sosai
mahaifiyar ta sa ta dauki zafi. "Mommy ki
kwantar da hankalin ki. Mun riga mun
gama magana da ma da Zainab akan
issue din yaron nan. Har ma na yi waya da
Habib da Moon nace mu hadu yau a gidan
ki mu tattauna akan maganar dan mu
tsayar da shawara daya. Amma tunda
kinzo nan din kuma kinzo da maganar ba
ra in kira su kawai sai ince su taho nan
gidan, tunda ga Faruk ma yana gari...
Tace "auren za'a yi masa dai k0?? In ba
wannan maganar bace ba bana son jj"
Mama tace "auren za'a yi masa Mommy.
Insha Allahu in muka yi miki bayani zaki
fahimta" Mommy tayi ajiyar zuciya "zan
saurara inji. Duk wani hukunci da za'a
yanke ina nan zaune zaku yanke shi. Ba
zan barku ku sake daukan wani shirgegen
aikin ku hada shi da shi ba. To me yayi
zali shi ba wuta ba? Haka kawai
santalelen saurayi kamar wannan a tashi a
dabaibaye rayuwar sa a guri daya a hana shi zaben abinda yake so. Ni ba dan Ayaan ya riga yayi maganar Khausar ba da Gidado zan bawa"
Faruk yace "wai ya batun Bassam kuwa?
An gano inda yake?" Abba yace "eh an
samo shi. Yana wani hotel ya kama daki,
Sun rufe masa account din sa dam haka
very soon zai nemi gida da kansa. Ja'irin
yaro mai tsaurin ido" Mommy tace "irin na
ubansa ne ai. Wanne irin tsaurin ido ne
ubansa bai yi ba? Zasu zo su saka yaro a
gaba wai yayi rashin kunya bayan su babu
irin rashin kunyar da ba su yi ba".
Gidado da tunda Mommy ta ambaci
kalmar aure yaji cikin sa ya juya, yana
sane da kallon da Mama take jifansa da
shi da nufin ya tashi ya basu guri amma
yayi kamar baya ganin ta dan so yake yaji
komai a maganar, sai dai kuma sai yaji sun
saki maganar sa sun koma maganar
cousin dinsa Bassam da yake son khausar
ita kuma suna soyayya da Ayaan, wannan
ya sa yayi yaji ya bar gidan Auntyn su
Hafsat bayan yayi mata rashin kunya, ya
koma hotel da zama, yanzu yadda za'a yi
ya dawo gida a hukunta shi ake nema.
Yana jin Abba yayi waya da Mammy da
kuma Uncle Habib yace su zo gidan sa,
sannan suka cigaba da hirarrakin su. Sai da Mama taga dai bashi da niyyar fita sannan ta kira sunan sa direct. "Gidado" ya juyo ya kalle ta "tashi ka tafi" babu
musu ya mike tare da yi musu sallama ya
fita, Sai dai kuma zuciyar sa bugawa take
yi sosai, ya tabbatar tunda Mommy ta
dage akan maganar auren nan to dole sai
anyi shi? Amma kuma da wa? Kar fa aje a
sake daura masa igiyar da zai kasa
kwance wa bayan ga waccan igiyar har
yanzu yana fama da ita.
Haka yaje yayi ta shawagi a gari, yasan in
yahe gidan sa ma wani takaicin zai tarar, a
karshe sai ya tafi gidan Ya Amen ya ci
abinci a can suka kuma tattauna akan
maganar. Ya gaya masa duk abinda ake
ciki, except for abinda ya samu Safiyya,
ya dai nuna masa iyayen ta ne suka matsa
mata suka hada ta aure da Mukhtar,
yanzu kuma da zaman auren yaki yiwuwa
sai suka raba.
Anan ne Al'ameen ya kuma tabbatar wa
da kansa cewa Gidado yana matukar son
Safiyya kuma at this stage abu ne mai
wahala ya rabu da ita. Dan haka ya yanke
shawara a ransa cewa zai je ya gwada
bugar cikin Mammy yaji shawarar da suka
yanke kuma ya nuna mata abinda ya
tahimta da dan uwan nasa, Humaira ta fito sun gaisa, ya karbi Ayman yana yaba wa da yadda yaron yayi girma sosai, a ransa yana fatan ranar da zai ga
nasa dan shima, Sai kuma suka vi hirar
karatun da Humaira zata fara yi very soon
a jami'ar Oxford akan harkar zane zane.
Daga nan suka koma hirar Bassam and
his drama.
Sai da dare yayi sosai sannan ya tashi zai
tafi, Humaira tace ya gaishe da Safina, sai
yaga sun kalli juna ita da Al'ameen sunyi
dariya, ya tambaya "what?" Sai Humaira
tayi saurin girgiza kanta "babu komai fa.
Ka gaishe ta Please" koma menene bata
son ta gaya masa dan ta san tsakanin
mata da miji, kar ya gaya masa shi kuma
ya gaya wa matar tasa.
Sai bayan sun fita sannan Al'ameen ya ke
gaya masa ashe wai drama akayi ranar da
Safina tazo barkan Ayman. An bata jariri
taki karba wai ita bata iya daukan jarirai
ba, ai kuwa aunty Amina tana gurin dan
haka ta wanke ta tas a gaban mutane,
daga baya ta hada da nasiha, shine ta
shiga daki ta zauna ita kadai ta ki yiwa
kowa magana, Mufida ma da tazo tayi
mata magana da niyyar ko zata saki
jikinta, har tana janta akan su shiga
kitchen suyi girki tare sai tace ita ba zata bata kayan ta da kamshin abinci ba, ai kuwa Mufida taji haushi da kyar su Basma suka hana ta kula ta suyi rigima.
Shi dai Muhammad murmushi kawai yake
yi, a ransa hangowa yake yi Safiyya ce,
yana hango yadda zata shiga kitchen din
nan tayi girki, yana hango yadda zata
dauki babyn nan ta rungume, yana
hango..... Sai da Al'ameen ya taba shi
sannan ya lura da murmushin da vake tavi
"wato kai murna ma kake yi matar ka bata
samu karbuwa a family ba k0? Mugu"
Muhammad ya yi dariya kawai ya shiga
mota ya tafi amma ya san rashin samun
karbuwar Safina a family yana nufin
higher chance of samun karbuwar
Safiyya.
Duk da dare yay amma bai hakura ba sai
da ya biya ta gidan su wai ko za'a ce
masa wani abu, ya tarar bakin duk sun tafi
amma kuma daga Mama har Abba babu
wanda yace masa komai. Hakan kuma ya
damu zuciyar sa sosai. Gani yake da ace
maganar Safiyya suka yi ai da zasu gaya
masa ko dan su faranta masa ko?
Babu wanda ya kula shi da niyyar faranta
masa din sal anar Alhamis, ranar ne Abba
yay masa magana casually a harabar
gidan su sanda yaxo yake kokarin shiga, "Uhmm Muhammad, maganar da kaji munayi ranar nan da Mommy akan auren da tace ayi maka. Ka amince ayi?" Ya danyi shiru yana kallon sa ya rasa abin
cewa, gashi kuma abban a tsaye yake
amsa yake jira "aure Abba?" Ya tambaya
muryar sa cike da damuwa. Abba ya bata
rai "ka zama kurma ne?" Ya girgiza kansa,
there is a chance na cewa Safiyya ce
sannan kuma akwai chance na cewa ba
ita bace ba. Risk ne wannan zai dauka,
babban risk. Ya gwada tambaya "Abba
aure da wa?" Sai kawai ya ga Abban yayi
murmushi sannan ya dan daki kafadar sa
kadan yace "some one better than your
wife. We will never repeat the mistake we
did a baya" ya danji sanyi a ransa, tunda
ake maganar Safina sai yau yaji ra'ayin
Abba a kanta. Ya san dai koma menene
iyayensa ba zasu cutar da shi ba and he
trust they will make the best decision for
him. A hankali yace "shikenan Abba na
amince" Abban ya sake murmushi sannan
yace "Allah ya baka ladan biyayya" sai ya
juya ya shiga motarsa driver ya ja suka
fita.
Washegari juma'a ta zagayo amma babu
labarin komai. A juma'ar ne kuma bayan
yaje masallaci ya dawo Safiyya ta kira shi
da tashin hankali a muryarta, tambayar sa
kawai tayi yana ina sannan ta katse kiran ba tare da ta ce komal ba, yayi ta kira bata dauka ba, daga nan ta kashe wayar ta ma gabakidaya. Wannan ya tayar da hankalin sa, a niyyar sa in ya koma gida zai dauki
motarsa ya tafi ya zaga dangi yayi
gaisuwar juma'a kamar adda ya kanyi in
ya samu dama. Amma sai ya fasa, yana
zuwa motar ya dauka kawai ya fita ba tare
da ya ji abinda Safina da ta sha kwalliyar
lace take gaya masa ba.
Hanyar gidan su Safiyya ya dosa, ko bai
shiga ciki ba maybe zai samu wani labari
daga gurin mai gadi duk da dai mai gadin
shima wani kallo yake yi masa kwana
biyun nan. Sai da ya kusa zuwa sannan kiran waya ya
shigo masa daga gurin Mama "kana ina?
Kazo gida yanzu akwai magana mai
muhimmanci" sai yaji a muryarta kamar
farin ciki take yi, a yanayin order din da ta
bashi kuma kamar laifi ne yayi. Ya rasa
menene, amma in dai Mama tayi kira to
babu sauran jira. Sawun giwa ya take na
rakumi. Kan motar ya juya ya chanja titi
zuwa wanda zai kai shi gidan su.
Bayan ya shiga sai ya tsaya a harabar
gidan yana kallon motocin da suke wajen,
kusan duk iyayen sa maza suna nan har da motar uncle dinsa yayan mama dake Kano. Ya fito sai mai gadin su ya karasa da sauri yana watse baki hannun sa rike da goro da alawa yace "ranka ya dade
munji abin alkhairi, Allah ya sanya alkhairi
ya sa abokan arzikin juna ne ku" gabansa
ya fadi, ya kalli fuskar mal gadin ya kuma
kalli goron hannun sa sannan yace " meen" sal ya shige cikin gida da sauri.
Tun daga waje yake jiwo dariyar