Author : Maman Mama Category : Romantic Hausa Novels
bukatar dalilin da zai gaya
wa kansa da kuma ita sannan da iyayen
su a matsayin dalilin rabuwar aside her
being Safiyya's step sister.
Wannan ya sa ranar asabar din da za'a
kawo Safiyya ya bi umarnin Mama yaje ya
yi wa Safina siyayya, akwati guda uku ya
cika mata da kayan sawa masu kyau da
sauran kayayyakin amfanin mata, sannan
ya biya ta gurin siyar da mota ya siya
mata mota yar daidai misali aka biyo shi
da ita zuwa gidan,
Yana shiga ya saka mai gadi ya shiga da
kayan cikin falonta ya ajiye, sannan ya
shiga, bata falo, amma yaji motsinta a
cikin dakin ta, ya je kofar dakin ya tsaya a
bakin kofa yana kallon ta, hannayensa a
cikin aljihunsa. Ta hargitsa dakin gabaki
daya, ya kasa gane gyarawa take yi ko
hargitsawa take kara yi. Ita kanta a
hargitsen take. Ta juyo tana kallon sa,
fuskarta gabaki daya kamar ba tata ba,
har wani duhu ya ga tayi.
"ango" tace tana yi masa wani murmushi
da shi kansa ya san ba na gaskiya ba ne
ba. "miji na kuma mijin kanwa ta. Wannan
shine kirarin da zan ringa yi maka daga
yau" ya juya kansa gefe yana kokarin
hana kansa gaya mata wadda zata hana
ta bacci yau. Ta cigaba "ita kuma daga
yau sunanta kanwata kuma kishiya ta.
Maciya amana, daga kai har ita".
Ya danyi murmushi yace "daga mu har ke
mun san cewa she didn't marry your
husband, you married her boyfriend.
Wannan shine cin amana" ta matso
gabansa "really? Kuna da shaidar da zaku
nuna min kan cewa na san kai saurayin ta
ne sanda na aure ka? Kuna da shaida?"
Bai amsa ba sai yace "me yasa kika
dawo?" Ta danyi murmushi mai ciwo tace
"me ya sa ba zan dawo ba? Ka manta kai
mil na ne Habibi?" Ta fada tana kai hannu
fuskar sa ta shafa sajensa ya danyi taku
daya baya sai tace "kai miji na ne kuma
ina son ka. No matter how much you hate
me hakan ba zai cire min sunan matarka
ba har sai ka sake ni da kanka. And you
cannot do that saboda iyayen ka, shi yasa
kaji dadi da na tafì gida ko ta kaina baka
sake bi ba, a ranka kana murnar cewa na
tafi na baku guri zaku ci amarcin ku son
ranku ko? Ni kuma shi yasa na dawo, dan
a raba amarcin da ni. Kar ka manta kwana
uku ne, bazawara ce, dan ma dai at least
ka dandana budurwar kaji dan haka yanzu
zaka fi banbancewa sosai, zaka ware aya
daga cikin tsakuwa, in ka gama kwana
ukun sai ka dawo dakina, watakila zuwa
lokacin ka fahimci gaskiya, in ma kuma
baka fahimta ba ina bukatar ka dawo din
ko kallonka ne in saka ka a gaba inyi tayi".
Bai amsa duk wadannan maganganun
nata ba sai ya juya ya koma falo yace "ki
zo ina son magana da ke". A gaban kayan
da mai gadi ya ajiye ya tsaya, ta fito sai ta
tsaya itama tana kallon kayan tana kuma
kallon sa, ya nuna mata kayan da hannun
sa. "ga kaya nan. Mama tace ana yi a
al'ada" ya ciro key din motar ya dora akan
kayan "ga wannan, it is a gift from me to
you. I know we have been on a wrong foot
throughout our days together amma ina
fatan maybe watarana we will forgive
each other". Ya daga kai yana kalion ta, ga
mamakin sa sai yaga hawaye suna bin
fuskar ta, ya danyi gyaran murya yace
"akwai abinda kike bukata?" Ta dago kai
tana kallon sa tace "abinda nake bukata?
Kamar me fa?" Ya dan daga kafada
"foodstuff, cleaning things, anything dai"
ya juya kanta tace "what of mijina? Idan
miji na nake bukata kuma fa?" Ya sauke
ajjiyar zuciya bai ce komai ba, ta tako
zuwa inda yake "ba'a kawo ta ba ai, dan
haka yanzu ma a dakina kake, me zaka yi
idan nace kai nake bukata a yanzu?".
Ya zaro ATM card ya ajiye a kusa da key
din motar yace "dan kina bukatar wani
abu ki cira kudi ki siya, 2728 shine pin
din". Daga haka ya juya ya fita ya bar
gidan, bai sake kuma waiwayar gidan ba
duk kuwa da kiran da take ta zabga masa
a waya kullum sai yau, three days later.
Yana shiga gidan yayi packing yana amsa
gaísuwar da maigadi yake yi masa sannan
ya fita ya shiga bangaren sa, ya tsaya
yana karewa dakin na sa kallo, thinking
about a lot of things, thinking about
abinda ya kamata ya dauka a dakin da
kuma wanda baya bukata. Sai dai bai
dauki komai din ba, ko zai dauka ba yanxu
ba. Ya zauna akan study yabl6din da yake
dakin ya dauko wata takarda sannan ya
dauki biro yayi rubutu a cike sai ya ninke
ya saka a cikin aljihunsa sannan ya dauki
wayarsa ya kira number din Abba suka
danyi magana kadan sai ya kashe ya mike
ya tafi bangaren ta.
Ya tarar da ita tana ta gyara gyare, da
alama deep cleaning take yi wa gidan, ya
yi sallama sannan ya tsaya a bakin kofa ya
saka hannayensa a cikin aljihu, mai aikin
ta ta gaishe shi sannan ta shiga ciki da
sauri, ba'a jima ba Safina ta fito tana
gyara dankwalin kanta. Yayi mata
murmushi, sai yaga mamaki ya bayyana a
fuskar ta. Maybe bai taba yi mata
murmushin gaskiya ba.
"Sannu da zuwa" ta fada indicisively, "I
thought ba zaka z0 ba. Nayi ta kira baka
dauka ba" ya daga kafada, "You didn't
need to keep calling" ta karasa shigowa
tana kallon fuskar sa da take dauke da
murmushi da kuma annurin da ya kasa
boyewa, kowa ya kalle shi sai yaga
annurin angonci a tare da shi,
"I thought ba zaka zo ba shi yasa nayi ta
kiran ka. I thought I need to involve our
parents…." "Cut the threats" ya fada,
"sit. Magana na zo zamuyi" ta zauna
kamar yadda ya bukata akan kujerar
zaman mutum biyu tana kallon sa,
yanayin da ta fuskanci yana ciki shine
abinda tayi burin samu a rayuwar auren
su, shine kadai abinda take son samu,
not mota ko kudi.... Was it too much to
ask?
Sai ya karaso, and ga mamakin ta sai ta
ga ya zauna akan kujerar da take zaune
akai, it was the closest they get tun da
aka daura musu aure except for that
night. And to top it all sai ta ga ya kama
hannun ta ya rike a cikin nasa, still with
that smile on his face yace "Safina,
Magana nake so muyi. Please ina bukatar
attention dinki. Ina son muyi first
reasonable magana as a couple. Ina son
mu samu understanding, Ina so mu samu
matsaya a auren mu" ta daga kai ta saka
idonta a cikin nasa, within the first second
ta gana narkewa, duk wasu makaman
yakinta suka zube daga hannun ta suka
barta ita kadai, daga ita sai zuciyarta sai
kuma wadannan idanuwan nasa da yake
kallonta da su.
"Can we talk, please" ya fada a kokarin
dawo da ita cikin nutsuwar ta. Ta saka
daya hannun nata ta kara rike hannun sa
da ya rike nata da shi, ji take kamar za'a
saka hannu a zare mata shi, ji take kamar
in ta sake shi zai bace ya barta ta cigaba
da miserable zaman da take vi ita kadai a
rayuwar da ko kallo bata ishe shi ba. Ta
gyada kan ta da sauri gain still jiran
amsar ta yake yi.
Yayi ajjiyar zuciya "Okay. Here is the
thing. We have started on a totally wrong
foot a cikin auren mu, kuma akan wrong
feet muka yi ta tafiya har yau kuma akai
muke. I want to change our relationship.
Dan wannan da muke kai babu inda zai vi
leading din mu to sai destruction. Haka
ne?"
Ta sake gyada kai tana jin kamar a cikin
kwakwalwar ta yake yi mata maganar,
kowacce kalma ta sa tana samun guri
tana zama a cikin kanta, Ya cigaba "okay,
Tunda mun amine muna bukatar chanji
then next thing shine thing shine mu yi
letting go of the one we have tunda mun
fahimci babu inda zai kai mu sai wahala.
But before that, ni dai personally, ina so in
gaya miki cewa duk abubuwan da kika yi
min, wanda na sani da wanda ban sani ba
idan da akwai, na yafe miki. Duniya da
lahira. Kuma on the other hand, ina
neman yafiyar ki ta abinda ni navi miki
intentionally ko unintentionally" ya sake
fadada murmushin sa,"na san navi miki
abubuwa da yawa, some of them I am
even ashame of them. Ina fatan zaki yate
min, ko da ba yau ba, ko watarana ne" ta
danyi shiru tana studying, ta kasa placing
kalamansa at the exact spot da ya kamata
ta saka su. Abinda dai is clear to her shine
Muhammad ne, Habibin ta, a zaune a
gabanta hannunsa rike da nata da kuma
murmushi akan fuskar sa yana rokon ta
gafara akan abinda yayi mata, that is
more than abinda take roka a cikin
addu'arta.
Ta yi masa murmushi "a lot of things have
happened. Most of which nice na jawo
su. Kuma ko a lokacin ma in ka tuna ai ina
gaya maka cewa na yafe maka, saboda
ina sonka, na sha gaya maka ba zan iya
rikon ka a raina ba dan bana son Allah ya
kama ka a kaina" ta fada tana shafa gefen
fuskarsa da hannun ta daya, dayan still
yana rike da hannunsa. Yace "yes, da
farko kenan. Amma daga baya nayi
manyan laifuka ai, avoiding your bed,
slapping you, and the baby......... Na san it
wasn't entirely my fault but da ace ban
bari emotions dina sun rufe idona ba
maybe the accident wouldn't have
happened. Kiyi hakur'" ta sunkuyar da
kanta tana jin hawaye yana taruwa a cikin
idonta, taso cikinta kamar ranta, rashin
cikin nan was the saddest thing that has
happened to her a rayuwar ta. Ta daga kai
ta kalle shi tace"Allah bai yi da ma zai zo
duniya ba. But yanzu ka yarda cewa naka
ne? Ka yarda kai kadai na sani ban san
kowa ba?" Ya gyada kansa yana jin
zuciyar sa tana breaking ace "Na yarda.
Ko a lokacin ma na yarda. Na fadi
maganganun ne cikin bacin rai.
Kiyi hakuri" ta yi murmushi, a ranta tana
kara tabbatar wa da kanta abinda zuciyar
ta ta gaya mata tun farkon shigowar sa, ya
banbance tsakanin aya da tsakuwa, ya
gama chasing tsakuwar ya dawo gurin
ayar "na hakura" ta fada tare da ajjiyar
zuciya, tabbas komai yayi farko zai yi
karshe. "Na hakura, Allah ya bamu wasu
masu albarka" yayi murmushi yace
"Nagode sosai. This really means a lot
kuma ba zan taba mantawa ba". Suka yi
shiru suna kallon juna kowa da abinda
yake zuciyar sa, sai ta daga kanta tana
kokarin hade bakin su.
Ya dan matsa kadan sannan ya mike
tsaye. "Get your veil. Zamu je wani guri
yanzu" ta mike tana kallon sa, gabanta
yana faduwa amma bata gane ina yake
nufi ba. Basu taba fita outing as a couple
ba, maybe wani guri zai kai ta, maybe
kasuwa suyi siyayya, maybe gidan abokin
sa, maybe...…. Alot of maybes.
Sai kuma ya kalli agogon sa yace "bara
inje inyi Sallah, Ki same ni a mota", Itama
sallar tayi. Amma hankalin ta baya tare da
ita. Babu abinda take yi sai juya
maganganun sa a ranta, Amma zuciyar ta
taki barin kwakwalwar ta tayi digesting
maganganun ballantana ta fitar da amsa.
Tarin soyayyar sa ta rufe reasons a
tunanin ta.
Tana gamawa ta kara gyara jikinta sannan
ta saka mayafin ta ta gayawa mai aikin ta
cewa zata je unguwa ta dawo. A mota ta
same shi yana waya. Tana shigowa ya
karasa wayar sannan ya tayar da motar
suka tafi. Ga mamakin ta sai taji yana
mata hira a hanya, yana nuna mata gurare
da kuma bata labarin da ya shafi gurin,
har da dariya yayi mata. Sai da suka yi
nisa sannan ta gane inda suka dosa,
gidan Daddy. "Me zamuyi a gidan
Daddy?" Ta tambaye shi "zamu hadu da
iyayen mu ne muyi magana akan
relationship din mu" tayi shiru tana
digesting maganar "I thought mun gama
maganar dazu" yace
"yes, but they need
to know, ko ba haka ba?" Ta girgiza kai
"we are not kids. Bama bukatar gayawa
kowa komai akan auren mu. Besides,
Daddy ba babana bane ba. Ni baba na ya
mutu" ya juyo da sauri ya kalle ta sai ta
dauke kai gefe, bai kara cewa komai ba
dan bayan gudun kar ta fadi wata mai zafi
akan Daddy har ya kai ga mayar mata ya
bata duk shirin da yayi,
Jin bai yi magana ba sai ita ta cigaba
"baya so na, Ya zabi yarsa a kaina, Idan ya
dauke ni ya babu ta yadda za' ayi ya aura
maka Safiyya. Ya kori yaya Mustapha ma
daga gidansa after all the years da ya
dauka yana bauta masa. Bai damu da
bacin ran Mommy ba. Bai damu da mu
ba" ta karasa tana dan daga murya. Still
bai ce komai ba, har suka je suka yi
packing, kamar yadda yayi tsammani, ya
ga motar Daddy a gurin shima. Ya fito
yace mata tazo su je, ya lura gabakidaya
ta rasa composure din da ta samu sanda
suka yi magana a gida, amma sai ta samu
kanta da binsa suka shiga ta kofar waje
zuwa falon Daddy, ta ga Abba a gurin
sannan Mommy, ko kallon ta Mommy bata
yi ba, dama tunda ta koma gidan
Muhammad ko ta kanta bata bi ba ko ta
kira ta a waya bata dauka, a gurin Safina
sai take gain fushine kawai Mommy tayi
zata huce ne daga baya.
A bangaren Mommy kuwa tun ranar da
Hajiya ta gaya mata Maman Muhammad
ta turo da yan'uwan ta sun bada hakuri
sun kuma gaya mata cewa su basu san
cewa Safina tana gida ba, Muhammad bai
fada musu ba, sannan kuma sun nemi
tafiya da Safina, Hajiya taso ta hana
Safinan komawa, taso a bari a gama bikin
Safiyya sannan iyaye su hadu aji makomar
auren Safinan amma sai Safina ta dauki
mayafi ta ce ita komawa zata yi. Mommy
tayi niyyar binta a ranar ta jawo ta ko da
kuwa a kasa ne ta raba ta da gidan, amma
daddy ya hana ta, a cewar sa Safina
needs to learn on her own, idan suka
tirsasa mata rabuwa da Muhammad zata
ce su suka raba ta da shi dan basa son ta
sun fi son Safiyya. Dan haka ta ja gefe
take jira, kamar yadda sauran iyayen
suma suke jira, sai yau da Daddy yace
mata abban Muhammad yace zasu zauna
akan maganar Safina da Muhammad
sannan ta zo ta zauna din dan taga yadda
lamarin zai kare.
Muhammad ya gaishe su daya bayan
daya, sai Safina ita ma tayi haka. Daga
Muhammad din har Safinan Mommy ba ta
amsa musu ba. Suka zauna a kasa yayin
da iyayen suke akan kujeru. Sai kuma
Muhammad yaji ya rasa me zai ce har sai
da Abba yayi magana "kace mu zo kuma
kayi shiru" Muhammad yayi dan gyaran
murya yace "uhmm. Dama muni magana
ne da Safina, Mun samu fahimtar juna
kuma mun yafe wa juna duk abubuwan da
suka faru a baya, Muna so mu sake bawa
relationship din mu second chance mu ga
yadda Allah zaiyi da mu. Shine muka z0
mu gaya muku",
Sal ya ga kowa ya saki baki yana kallon
sa, har ita kanta Safinan, dan da taga
sunzo nan har ta fara sarewa akan abinda
yake shiryawa. Abba yace "Muhammad,
Look at me. Are you sure? Duk maganar
da muka yanke yanzu anan ita ce final. Ka
fahimta?" Muhammad ya gyada kai "na
fahimta Abba. Nima ba zan kira ku ba idan
har ban tabbatar da decision dina ba" ya
juya yana kallon Safina da take ta zabga
murmushi kanta a kasa.
Sai kuma ya cigaba "a ganina everyone
deserves a second chance, I mean Safina
tayi laifuka kamar yadda nima nayi, idan
har zata iya yafemin nima me zai hana ba
zan yafe mata ba? A bisa alkawarin cewa
ba zamu sake maimaita laifukan mu ba.
Misali, ni yanzu nayi alkawarin cewa ba
zan sake wulakanta Safina ba, ita kuma
tayi alkawarin cewa ba zata sake yin karya
da kazafi da munafunci ba" ya fadi haka
yana kallon Safina da ta dago tana kallon
sa ita ma yace "ko?" Ta kalli iyayen su da
suke kallon ta sai ta gyada kai, amma
hakan bai ishe shi ba sai ya sake
maimaitawa yace "kinyi alkawarin ba zaki
sake yin karya, ko kazafi, ko munafunci a
cikin auren mu ba?". Jikinta ya bata cewa
something is wrong, amma ya nannade ta
da jijiyoyin jikinta dan haka tace "eh. Nayi
alkawari" yayi murmushi "shikenan. Muna
neman a saka mana albarka mu koma
gida. But before that I just need to ask
Safina one question. Safina, did you or
did you not know cewa ni saurayin Safiyya
ne kafin ki tura picture dina blog?".
Tambayar ta zo mata a bazata, and her
whole world came crashing down on her
head. Ta dago kai tana kallon sa "what?"
Ta tambaya, a take ya maimaita mata
tambayar "did you or did you not know
cewa ni saurayin Safiyya ne kafin ki tura
picture dina blog?".
Tayi shiru tana kallon sa sannan ta fara
bin iyayen su da kallo, interestingly
gabakidaya ita suke kallo suna jiran amsar
ta, a take ta fahimci trap Muhammad ya
haka mata, already kuma ta fada a ciki,
yanzu so far bai sake ta ba saboda bashi
da wani laifin da zai makala mata yace
shine dalili, shine yake so ya binciko
wannan maganar a gaban iyayensu a
kuma sake ta saboda ita, ita kuma ba zata
bar hakan ta faru ba. Never. And she
automatically gets into her defensive
mode.
"Muna jin ki" Mommy ta fada, maganar ta
ta farko tun da suka shigo, maybe yanzu
da ta fahimci cewa sakin ta za'a yi shine
ta fara murna. Safina ta kalle ta sannan ta
kalli Abba tana girgiza kai, ta san shine
way out dinta a wajen tunda Mama bata
zo ba, ta san muhammad baya taba
kaucewa maganar iyayen sa "ni wallahi
ban san saurayin ta bane. wallahi bata
taba nuna min shi ba. Bata taba hada mu
ba" Muhammad yace "nasan wannan. Ita
kanta Piya......
.. Uhmm I mean Safiyya ta
gaya min bata taba nuna miki ni ba, kawai
dai tambayar ki nake yi ko kin taba ganin
hoto na a wayarta, ko kin dauki hoto na a
wayarta. Or something like that?"
Direct ta amsa "wallahi ban taba ganin
hoton ka a wayar ta ba. Wallahi....
"Ya
daga mata hannu, "Magana ta kare, bani
wayarki" ta juya ta kalli Mommy sannan ta
kalle shi, "waya ta kuma? Me zaka yi da
wayata?" Ta fada cikin mamaki, bai amsa
mata ba sai ya miko mata hannu, ta dauko
wayar daga cikin jakarta ta bude ta mika
masa, a ranta tana lissafin cewa in dai laifi
yake nema ya makala mata ba zai samu
ba, dan babu wani abun laifi a cikin
wayarta.
Muhammad ya fara scrolling through
tarkacen hotunan da suke cikin wayar, ba
shi da tabbas din me yake nema amma a
ransa yana jin cewa zai samu, bai san
wanne hoton bane ba and it has been
more than two years but a yasan how
obsessed Safina is with him, baya jin zata
¡ya rabuwa da hotonsa a cikin
wayarta.
Ya jima gana scrolling, yayin da su kuma
suka cigaba da kallon sa suna jiran suga
abinda yake nema. And he saw it bayan
har ya fara fitar da rai. His picture, a tsaye
a jikin motar Safiyya a cikin makaranta,
hannayensa a cikin aljihunsa. Ya na ganin
hoton ya tuna shi. Safiyya ce ta dauke su
selfie tare shi da ita. Yayi murmushi yana
tuno da yadda ta so hoton a lokacin, ya
tuna har saka shi tayi a matsayin screen
saver din wayarta for a while. Sai kuma ya
kara kallon hoton and he realized
something, hoton ya nuna cewa an dauke
shine a jikin screen din wata wayar
sannan aka yi cropping, akayi cropping
out Safiyya from the picture.
Ya girgiza kansa sannan ya mika wa
iyayen su hoton. Kamar yadda ya gane
suma haka suka gane, har da date da
time gashi nan ya fito a jikin hoton. A
hankali yace "like I said. She didn't marry
your husband, you married her boyfriend"
ta sunkuyar da kanta kasa tana jin hawaye
yana bin fuskar ta sai