SAFIYYA BOOK COMPLETE MAMAN MAMA.txt

Author :  Maman Mama Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   94 / 113

279K to 282K   out of 336.6K words

iyayen
nasa, daga dukkan alama suna cikin
nishadi, yana shiga yaji Mama tace "au
Amir yaje? Dama yana gari? Yaushe rabon
da inga bawan Allahn nan" Abba yace
"nima ban san yana gari ba shi yasa ko
neman sa banyi ba, sai kawai ganin shi
nayi sun zo tare da Sultan. Zan kawo shi
gidan nan kuwa insha Allah kafin ya koma
Kaduna" Habib yace "ai Sultan ne ya biya
sadakj" Mama tace "haba? Ya riga Faruk
kenan" Faruk yayi dariya "ya fini baki ai.
Kin san yayan nawa ba'a kure shi a
magana, Yace lallai wannan aure shine zai
biya sadakin sa, dole na hakura na bar
masa, Amma ina nan zan bawa ango da
amarya gift instead of sadakin da ban
samu bayar wa ba".

A hankali Muhammad yace "sadakin wa?"
Duk suka juyo suna kalion sa, Habib ya
mika masa hannu yayin da Mama ta hade rai "baka iya sallama ba?" Uncle Hamza wan Mama yace "in yayi sallamar ma ai ba za kuji ba kuna ta hira, yau dai daya al a daga wa ango kafa kar ayi masa fada" ya
karasa maganar yana dariya amma
Muhammad kallon sa kawai yake yi. Ya
san za"a daura masa aure amma bai san
cewa za'a daura ba da sanin sa ba.

Ganin duk shi suke kallo dai ya karasa ciki
ya zauna a kasa, a tsakiyar su. Uncle
Habib ne yayi magana, "Kamar yadda
muka shawarta a tsakanin mu, bisa
la'akari da dalilai masu yawa sannan kuma
da amincewar ka, an daura maka aure
Muhammad, da Safiyya Adam Muhammad".

Wani murmushi ne ya taso tun daga
zuciyar Muhammad har zuwa kan
fuskarsa. Wani irin farin ciki yake ji yana
lissafin ina ma shi yaro ne ya tashi yayi ta
zagaye gidan a guje yana tsalle? Instead
sai ya rufe fuskarsa da hannayensa ganin
yadda iyayen nasa already suka fara
tsokanar sa, "Kaga marar kunya ko? Satin
nan gabakidaya a kumbure yayi shi kamar
zai fashe amma ji yadda yake murmushi
ko kunyar mu baya ji" Abba ya fada da
dariya a muryarsa, Daga jin muryasa ka
San farin cikin dan na sa ya saka masa
farin ciki shima, Faruk yace "ai kuwa dai tushi ya kare, ciwo ya kare, hada akwati a gudu daga gida a je a dauke yar mutane ya kare" ya fada yana dan jan kunnen Gidado kadan cikin tsokana. Gidado ya
sake jin sabuwar kunya ta rufe shi. Uncle
Habib yace "nauyi kuma ya karu ba. Ni
tausayin ka nake ji Gidado. Hada mata
biyu musamman masu kusanci da juna
irin wanna sannan kuma wadanda kake
musu mabanbantan soyayya sosai akwai
wahala. Akwai aiki a gaban ka sosai".

Daga nan sai suka koma yi masa nasiha
akan sauke nauyin iyali da kuma kwatanta
adalci. Suka kara nuna masa irin girman
da ya same shi da kuma jaddada masa
cewa suna tare da shi a duk kan
al'amurran sa, duk wata shawara ko wani
taimako zasu bashi in dai suna da hali. Sai
kuma suka gaya masa cewa idan an jima
bayan sallar magrib ya shirya ya kuma
nemi abokan sa su raka shi ya gaishe da
iyayen Safiyya, daga nan kuma su gano
amaryar.

Daga nan ya tashi ya shiga dakin sa. Yana
rufe kofa ya zarce straight yayi sujjada
dan nuna godiyar saga Ubangiji, har sai
da hawaye ya kawo cikin idon sa. Ya na
dagowa ya cigaba da neman Safiyya a
waya, amma still wayarta a kashe. Ya tura
mata message ta Whatsapp duk kuwa da yasan ba zata gani yanzu ba.

"I am yours, and you are mine. Forever"

Daga nan sai ya fada akan gado yana yar
dariyar murna, babu abinda yake son gani
a lokacin sai fuskarta, ya zata ji? Ya zata
yi? Sai kuma ya dauko wayar sa ya kira Ya
Amen, yana dauka yace "kai an daura fa"
Al'ameen yayi dariya "amma yaron nan ka
cika marar kunya wallah, ni ba yayanka
bane ba kake ce min wai an daura"
Gidado yayi dariya cikin nishadi "watanni
ne fa kawai, ko goma basu kai ba"
Al'ameen yace "ko kwana goma ne dai na
girme ka kuma dole ka bani girma na"
Gidado yace "a da kenan, yanzu nine
yayan ka in gaya ma" Al'ameen yace "la
ila. Da gaske yaron nan ka raina ni fa.
Kana gaya min kana da mata biyu ko?
Dole Ayaan yaji maganar nan kuwa" suka
cigaba da hirarrakin su cikin nishadi,
Al'ameen ya gaya masa cewa dama
Mammy ta gaya masa maganar auren
Gidadon amma Abba ya hana a gaya
masa yana son ya gani if he will still do
the biyayya without knowing wadda za'a
aura masa din. Gidado yayi murmushi
kawai suka yi sallama bayan ya sanar
masa maganar zuwa gidan su Safiyya in
an jima,

Sai kuma ya fara lissafin wadanda zai kira
a abokan sa, daga baya kawai sai ya fasa
yace Al'ameen da sauran kannensu na
family sun ishe shi sai abokinsa Usman
wanda already ya san Safiyya. A haka ya
hada team din sa, Al'ameen, abdulshakur
dan aunty Amina, Baffa second child din
Uncle Habib, Haidar, sai kuma Usman.

Al'ameen ne duk ya gaya musu, ai kuwa
nan da nan suka zo gidan suna ta
hayaniya da tsokanar Gidado wai ya girmi
har iyayensa yanzu, ya zama mai mata
biyu. Matan ma sai gasu suna ta zuwa
Allah ya sanya alkhairi, gida ya cika kamar
ana taron biki, Mama kuwa taji dadin
zuwan nasu dan ta samu sun cinye
abincin da ta girka wa yan daurin aure dan
basu ci ba haka suka bar mata kayanta
suka ce sun ci abinci a can. Nan da nan
aka cinye abincin tas har sai da aka dora
wani. Kowa ya kalli Gidado ssi ya tsokane
shi saboda yadda yake washe hakora
kamar gonar auduga, kana kallon sa
kasan cewa yana cikin farin ciki mai tarin
yawa.

Sai da suka yi sallar magrib sannan suka
fara shirin tafiya gidan su Safiyya, ya
shiga toilet yayi wanka, yana fitowa ya ga
Kaya akan gadon sa a ajiye, ya san Mama Ce ta ajiye masa, yaji wani sonta yana karuwa a ransa, ya dauki kayan yana dubava, yadi ne fari kal mai laushi a
hannu da kyalli a ido, anyi masa dinki itin
na zamani da zare off white mai kyalli
wanda ya dace da hula da kuma takalmin
da ya gani a gefe duk size dinsa, sai
karshi suke yi wanda ya san mix ne na
turaruka kala kala, Sai kuma dan karamin
box dauke da agogon rolex sabo fil,
"Mamana" ya fada a hankali yana jin dadi
a ransa.

Ya saka kayan ya shirya tsaf sannan ya
tsaya yana kalion kansa a madubi, ya tuno
maganar Safiyya "You will wear white, You
will look so good in white" yayi murmushi
sannan ya ciro agogon daga cilkin kwalin
sa ya saka, Ya ji an danyi gyaran murya
daga bayan sa, ya juya yaga mama a
tsaye ta jingina da jikin bango, ya danyi
kokarin rage murmushin fuskar sa amma
sai ya kasa instead sai kawai yayi dariya
tare da karasa wa gurin ta da sauri ya
rungume ta har da dan daga ta ya raba ta
da kasa, ta dan dake shi a katada tana
dariya ita ma "ajiye ni kai. Marar kunya*,
¡ajiye ta ta ja dogon hancin sa "kayi kyau sosai Muhammad Gidado" yay kissing
goshinta tare da kama hannun ta ya rike a cikin nasa “thank you Mama. I mean thank you for everything” ta gyada kai "Allah ya baka ikon sauke nauyin da ya
dora maka, Allah yayi muku albarka
gabakidaya", Yace "Ameen" sannan ya
wuce ta ya fita.

Yana fita matan da suke gurin suka fara
rangada guda, shi kuma sai washe baki
yake yi. Aka zo akayi ta daukan pictures
da shi sai da kyar Abdulshakur ya jashi
suka fita. A hanya ma haka suka yi ta raha
har suka je gidan, a lokacin ya kara
tabbatar wa da cewa bayan Ya Amen da
babu wanda ya san alakar da take
tsakanin Safiyya da Safina, tunda basu je
gidan Daddy ba a lokacin auren Safina,
dan haka as far as danginsa are concern
Safina yar Katsina ce kamar yadda ta
tabbatar musu da kanta. A gidan suka samu tarya daga wani mutum mai cikar kamala da kwarjini
wanda daga baya Muhammad ya fahimci
shine Uncle Sufyan din da Safiyya ta gaya
masa, shi ya shigar da su har wajen
Daddy suka gaishe shi, suka same shi
tare da uncle Ahmad, shi dai Muhammad
yana ta sunkuyar da kai baya son hada
ido da Daddy, Daga nan kuma aka dawo dasu parlor suka gaisa da wadda ya gane a matsayin Aunty Hajjo. Sai tace su jira a kawo musu amarya, tun daga nan ya
mayar da hankalinsa kan hanyar da yaga
ta bi. Yana jin sauran samarin wajen suna
ta hirarrakin su amma sam hankalin sa
baya kan su, ita kadai yake so ya gani. Sai
yaga kamar sun dade da yawa, me suke yi
ne wai?

A sanda ya dora idonsa a kanta kuwa ji
yayi babu wani sauran birbishi na damuwa
da ta rage masa a duniya, with Safiyya as
his wife, yana maraba da dukkan
challenges na rayuwa.

Ya lura da kallon da tayi wa Haidar,
sannan a take ta fara neman fuskarsa a
cikin mutanen gurin. Ya fahimci cewa
ganin Haidar da tayi ya saka ta gane da
shi a ka daura. Suna hado ido ya mike
tsaye tare da bude mata hannayensa, not
minding Aunty Hajjo ballantana sauran
samarin da suke gurin, ba ta watsa masa
kasa a ido ba kuwa ta zo ta shige mazaunin ta, cikin kirjinsa and they had their first halal hug, or maybe he should call it their first hug dan wancan na ranar
nan was done a cikin tashin hankali dan
haka babu wani feelings a cikin sa.

Yana jin hayaniyar mutane amma duk
baya jin abinda suke cewa, bugun zuciyar
Safiyya kadai yake saurara, tare da dumin
jikinta da kuma kamshin da yake tashi
daga gare ta. "It is okay. You are okay.
Muhammad Gidado is here" ya fada mata
a cikin kunnen ta. Ta gado da niyyar
kallon fuskarsa yayin da shi kuma yake
kallon kasa a kokarin sa na ganin tata
fuskar wannan ya saka fuskokin su duka
zo dab da juna. Tayi saurin mayar da tata
kasa shi ma ya dauke tasa gefe because a
yadda yake jin zuciyar sa a kanta anything
can happen.

Ya lura tunda tazo gurin ake musu hotuna,
Aunty Hajjo ta fadi sakon da iyayensu
suka bayar sannan ta juya ta tafi ta bar su,
daga nan Safiyya ta fara kokarin janye
jikin ta daga nasa, maybe sai yanzu ta
fara jin kunyar mutanen gurin, ya dan
sake ta kadan sannan ya jata suka zauna,
tana ta kara lullube jikin ta da katon
mayafin da ya kai mata har kasa. Suna
zama ya kara riko hannunta yana kokarin
leka fuskarta, ta dan harare shi da
kumburarrun idanunta, ya fahimci ta
dauka ba dashi aka daura ba, Allah kadai
ya san yawan kukan da tayi , sai yaji ya
hakan yayi masa dadi sosai, it feels so
good to be loved by the person you love

A hankali yayi mata introducing wadanda
suka zo da su, kowa yana tsokanar ta

"yau dai munga Safiyya"

"daga yau dai mun huta da labarin
Safiyya. Daga ina kake Safiyya, ina zaka je
Safiyya, me kake yi Safiyya"

"Har mafarkin Safiyya fa yake yi, cikin
dare zaku ji yana kiran sunan ta"

Muhammad yace "ban da sharri kuma.
Wannan dai kazafi ne"

Abdulshakur yace "a kira Ayaan a
tambaye shi ranar nan a UK idan ba sunan
ta kake kira mana cikin dare ba". Duk suka
yi dariya banda Safiyya da taji kamar zata
nutse a gurin., Haka suka yi ta raha suna
duke dauken pictures yayin da Esther ta
shiga hidimar cika musu gabansu da
snacks da drinks, sam ta kasa rufe bakin
ta tun da taji abinda ya faru saboda
murna. Safiyyah ta lura cewa Abdulshakur
yafi kowa surutu da tsokana, yayin da
Al'ameen yake zaune kawai yana kalion su
yana murmushi, sal jefi jefi zaka ji yayi
magana a hankali, Sai da suka fara shiri
taliya ne Al'ameen din yazo gurin su yace mata "amarya congratulations, Yanzu dai
za'a bar min zucivar dan uwa ta huta" a hankali tace ba tare da ta dago kal ta kalle shi ba "thank you Ya Amen. A gaida Humaira da Mammy" sai yayi murmushi aransa yana jin cewa tabbas dan uwan
nasa ya samu chanji.

Shi ya hada kan kannen nasa ya kora su
waje, ya kuma ce ya bawa Muhammad
minti biyu idan bai fito da zasu tafi su
barshi sai dai amaryar tasa ta kai shi gida. Suna fita Muhammad ya kara karfin rikon da yayi wa hannun ta. Sannan yayi kokarin daho fuskarta da daya hannun. "Amaryar Muhammad" ta kara sunne kanta gefe
tana jin kunyarsa "wai kunya ta kike ji? Ni
fa" ta juya fuskarta dayan gefen, da gaske
kunyar ta sa take ji musamman yanzu da
aka bar su su biyu, Ya danyi dariya "lallai
da rabon yau zan kwana a gidan Daddy
kenan. Ta yaya zan tafi ba tare da na kalli
cikin idon ki ba?" Ya fada yana daga
hannun ta da yake cikin nasa ya kai bacin
sa tare da hura mata iska a fatar hannun.
Tayi kokarin janye hannun amma sai ya
kara rikon su tare da fara kissing knuckles
din ta one after the other. Ta juyo da sauri
ta dora manyan idonta akan sa tace cikin
rada "CCTV" yayi saurin sakin hannun
yana rarraba ido, sai ta mike da sauri ta
bar inda yake tare da cewa "goodnight" yana ta rarraba ido amma da murmushi a
fuskarsa yayi mata alamar tazo su je waje
da hannun sa. Ta makale kafada, ya hade
hannayen sa alamar roko, ta sake makale
wuya. Ya kankantar da idonsa a kanta irin
kallon da yasan yana saka ta jin kunya sai
ta ja mayafin ta ta kara rufe fuskarta.
A lokacin aka bude kofa aka fito daga part
din Daddy. Duk suka juya suna kallon
wadda ta fito din, Mommy ce, fuskar ta

jage jage da hawaye, ta kalli Safiyya da
tayi saurin sunkuyar da kanta kasa sannan
ta kalli Muhammad shima ya janye idonsa
daga nata suna adawa, babu wanda ya
iya gaisheta a cikin su ballantana yace
mata wani abu, ita ma bata ce musu
komai ba sai ta wuce ta hau sama. Suka yi
shiru gabakidaya babu wanda ya sake
magana. Haidar ya dawo yace "Wallahi Ya
Amen yace zamu tafi mu barka" Gidado
ya gyada kai, kafin yace komai Safiyya ta
juya ta bi hanyar da ya ga ta fito daga ciki.

Haka ya tashi ya fita, bai ji dadin ganin
hawaye a idon Mommy ba amma shi kam
yau babu abinda zai saka wa farin cikin sa
shamaki,

Suka shiga motocin da suka zo a cikin su
sannan suka fita cikin nishadi kamar yadda suka shigo.

Daddy...
One week ago....

Ya dago kaga kai yana kalion bakon nasa
wanda shi da kansa ya ce a shigo da shi
har cikin dakin sa. Suna hada ido sai yaga
yanayin bakon nasa ya chanja gabaki
daya, lokaci daya yayi wani irin sanyi
wanda da bai shigo da shi ba. Maybe
kuma hakan yana da dangantaka ne da
yanayin rashin lafiyar da yake ciki da
kuma injinan da suke zagaye da shi.

Yayi masa maraba tare da nuna masa
kujera "bismillah". Abba ya zauna yana
cigaba da kare wa dakin kallo wanda ya fi
masa kama da dakin asibiti. Daddy ya
danyi murmushi yace "forgive all the
medical tarkace, Safiyya ce duk ta cika
min daki da shirgi, ni kuwa na san duk
yawan machines din da zata siya lokaci
yana cika zan tafi"., "Me yake damunka?"
Abba ya tambaya da Hausar sa mai
accent din fulani irin na Muhammad
Gidado, Daddy yace "ALS" sai Abba ya
cigaba da kalion sa da rashin fahimta,
Daddy ace "neuromuscular disease ne
da yake paralysing muscle, thereby
restricting movements. Ba zan cika ka da
medical jargons ba amma already na wuce time din da doctors suka yi tunanin ba zan kai ba" Abba ya girgiza kansa "ba su suke bada rai ba. Ba kuma su zasu
dauka ba" Daddy ya gyada kai "you are
right, I am a living testimony. But I am
sure ba wai kazo dan jin labarin rashin
lafiya ta ba ko? What brings you to me?"

Abba ya danyi shiru yana tattaro tunanin
sa waje daya, ganin Daddy ya taba
zuciyar sa sosai. Muhammad bai taba
gaya masa cewa bashi da lafiya ba. Ya
danyi gyaran murya sannan yace
"hmmm.... I don't know ko kasan ni
waye" Daddy yace "baban Muhammad
ne, mijin Safina. Kuna kama sosaj" Abba
ya dan yi murmushi tare da shafa gefen
fuskarsa sai kuma yace "haka ne. Amma
ba maganar Safina bace ta kawo ni. Nazo
ne farko ina so inji ko kana da masaniya
akan alakar da take tsakanin Muhammad
da Safiyya?".

Daddy ya danyi shiru kamar mai tunani
sannan yace "na jima da sanin cewa
akwai wani yaro da Safiyya take so, in
fact, tayi ta kokarin ganin cewa ta kawo
min shi ya shigar da maganar auren ta ni
kuma na hana ta saboda burin da na dora
akan ganin tayi karatu mai zurfi, saboda
wasu dalilal nawa. Daga baya kaddara ta gifta wadda tayi sanadiyyar rabuwar su. Amma ban san cewa shine Muhammad din da kannen mahaifin Safina suka daura
mata aure da shi ba sai kwanan nan. So your answer is yes, na sani".

Abba ya danyi shiru yana digesting
wanna amsar sannan kuma sai ya sake
yin wata tambayar "and what do you think
about their relationship. Menene
matsayar ka akai" Daddy yace "nace wa
Safiyya no. Na gaya mata cewa ba zan
aura mata shi ba duk kuwa da a fahimci
soyayyar da take yi masa, na hana ta
auren sa saboda kasancewar sa mijin
Safina. I don't know ko kasan relationship
din da yake tsakani na da mahaifiyar
Safina?" Abba ya gyada kai "na sani.
Babu wanda ya gaya mana hakan a
danginta, amma mun binciko hakan sanda
muna bincike akan auren ta".

Daddy yace "good. I raised her like my
daughter. Ba zan ce na so ta kamar yadda
nake son Safiyya ba but I did my best.
Sun tashi kamar sisters. Wannan ne
abinda ya kara bata min rai sanda na hana
Saliyya alaka da Muhammad amma taki
jin magana ta ta cigaba da ganin sa
behind my back. Na tambaye ta kuma
dalili ta kiyi min cikakken bayani illa cewa tana son sa. I got scared, I am a sick father unable to guide and protect his only daughter, Wannan ya saka na saka
cctv a dukkan bangarorin da suke gidan
nan except for bedrooms. Na saka ne dan
ita. Dan in san duk wani move dinta in
kuma yi kokarin discharging fatherly
duties dina. She told me cewa zata rabu
da Muhammad kamar yadda na bukata
tunda ta ga raina baya so. She invited him
in, suka zauna, and they had this conversation" ya fada yana mika wa Abba wayar da take hannun sa. Ya kara da cewa "ka kalla tun daga farko har karshe
sannan sai kai ka gaya min abinda kake
tunani a game da alakar ta su"

Abba ya taso ya karba, fuskar Muhammad
din sa ya gani da ta yarinyar da ya jima da
sanin sunan ta amma sai yau ya fara ganin
tata fuskar. Daddy ya kara da cewa "duk
abinda zaka ji ta fada, gaskiya ne, abinda
ya faru da ita kenan".

Abba yayi shiru yana sauraron
maganganun Muhammad dana Safiyya da
suke fitowa tas ta jikin speaker wayar.
Sanda ya gama gabakidaya a razane
yake. Hankalin sa ya kai makura wajen
tashi. "Ina yake?" Ya tambaya "shi
Mukhtar din ina yake? Da gaske kun
barshi? Kun kyale shi?" Daddy yace "da gaske mun barshi da Allah. Mun kyale shi shida Allah, Muna nan muna jira. A haka ma da muka rufe maganar Safiyya is
about to lose the person she loves very
much, me kake tunanin zai faru da ita idan
muka fito da maganar? Bata aikata laifin
komai ba but most people will run away
from hada zuriyar su da ita....." Abba yace
"then most people da kake magana a kai
a jahilai. Wannan abu ne da jahilai

94 / 113