Author : Maman Mama Category : Romantic Hausa Novels
told me ta san Safina, she
told me they are family friends, and dazu
maganar da Safina ta gaya min akan
Safiyya ta daga min hankali har na fara
mummunan tunani akan Gidado so l
called Hajjo and asked her a favor, nace
dan Allah ta gaya min duk abinda ta sani a
kan Safiyya step sister din Safina. Farko
kamar ba zata fada min ba, sai da ta
fahimci hankali na a tashe yake kuma na
gaya mata abinda yake tsakanin Gidado
da Safiyya da kuma abinda Safina tace
min akan safiyyan wanda har ya tayar min
da hankali nake neman gaskiyar lamari,
Sai ta saka nayi mata alkawarin ba zan
gaya wa kowa a duniya ba, har kai, sai da
nayi mata wannan alkawarin sannan ta gaya min komai".
Ga mamakin sa sai yaga hawaye yana bin
fuskarta, ta saka hannu ta share sannan
tace masa "na riga nayi mata alkawari, bana son in karya alkawarin da nayi mata. Amma abinda zan gaya maka shine yarinyar nan Safiyya ta sha wahalar da
ban taba gani ko jin labarin wadda ta sha
irin ta ba. Ta fuskanci kaddara mai zafi. Kaddara kuma irin wadda zata iya fadawa a kan kowacce ya mace" ta danyi shiru still idonta yana kasa sannan ta sake cewa
"ni mace ce, kuma ni uwa ce, watakila ku maza ba lallai ku fahimta ba amma ni na fahimta. Tunda har Allah ya sarke zaren kaddarar Gidado da na Safiyya har yanzu ta zamanto ita ce farin cikin sa, ni na amine kaje ka nema masa auren Safiyya ko dan mu samu ladan yarinyar nan sannan kuma mu samar da farin ciki ga dan mu".
Ya dan girgiza kai cikin mamakin maganar
ta yace "amma ba kya ganin this will be
too much for him? I mean mata biyu at his
young age? Kuma mata biyun ma
makusantan juna? Zai fuskanci crises
sosai a gidan sa" ta danyi murmushi
"wannan kuma zabin sane, zama da su
gabakidaya ko aka sin hakan zabin sa ne, mu namu shine mu sauke nauvin sa da Allah ya dora mana sannan muyi musu addu'a baki daya".
Tana gama fadar haka ta mike ta cire hijab
din jikinta ta rataye tare da hawa kan gado
ta fara gabatar da addu'ar kwanciya
bacci. Ya bita da kallo abubuwa da yawa
suna yawo a cikin ransa. Duk da cewa
shima tun dazu zuciyar sa ta fara karkata
zuwa da wannan barin amma bai dauka
tata zata chanja akala a lokaci daya ba.
Me Safina tace mata? Me kawarta Hajjo
tace mata? Baya son ya matsa mata har
ta gaya masa tunda tace alkawari tayi
cewa ba zata fada wa kowa ba har shi. Shi
kuma zai so matarsa ta kasance mai cika
alkawari.
Sai dai in dai har zai aikata abinda ta
ambata na aurawa Muhammad Safiyya, to
dole ne sai ya san abinda taki gaya masa
din, ko da kuwa ba'a wajenta ba ne ba.
Da maganar ya kwana da ita kuma ya
tashi, Da ita yaje office da ita kuma ya
tashi, Wannan ya sa daga office din bai
tafi gida ba sai ya gayawa driver dinsa ya
kai shi gidan Alhaji Adam Muhammad, Ya
san address din gidan ne sanda yana
bincike game da Safina lokacin auren
Muhammad. Mai gadi ya bude musu cikin sauri saboda gain kamalar sa, sai kuma ya tsaya yana kallon sa bayan ya fito fuskar sa tana nuna alamar ya gane shi,
ko kuma ace ya gane waye shi.
Ya kara gaishe shi cikin girmamawa sai ya
gaya masa cewa gurin mai gidan yazo.
Take ya ga fuskar sa ta dan saura cikin
yanayin jimami sannan yace "baya jin dadi
kam. Bashi da lafiya. Yau kuma kamar jikin
ya matsanta masa dan tun safe babu
wanda aka bari ya shiga gurinsa. Amma
bara in fada a cikin gidan na san zasu san
abinda za'a y" ya fada yana dosar
Hussein da ya fito daga cikin gida da key
din mota a hannun sa daga alama fita zai
yi, suka dan yi magana da Hussain sai
kuma Hussain din ya kalli Abba sannan ya
koma cikin gida da sauri.
Sai Abba yaji babu dadi a ransa, tunda
bashi da lafiya bai kamata ya zo ya dame
shi ba, Wannan ya sa ya sake kiran mai
gadin ya gaya masa "zan koma kawai.
Allah ya bashi lafiya, Zan dawo gobe ko jibi insha Allah" mai gadin ya gyada kai cikin fahimta sannan
cikin girmama wa yace "zan gaya masa
insha Allah, da zarar na samu ganin sa zan gaya masa" driver din Abba ya bude masa kofa ya shiga sannan suka fita daga gidan a nutse kamar yadda suka shigo.
Hussain ya shiga cikin parlour da sauri,
Mommy tana zaune tana waya da sister
dinta da take aure a Kaduna "wallahi har
yanzu bai ce min komai ba Sakina. Na
rasa yadda zanyi. I tried all I can possibly
do amma babu wata amsa. Yau ma
gabakidaya ya kara rikicewa, ya ki ganin
kowa ya hana kowa ganinsa sai Dr
Ma'aruf. Shima kuma duba lafiyar sa kadai
yayi amma bai ce masa komai ba".
Tana cikin maganar Hussain ya shigo, ta
lura magana yake son yayi mata sai tayi
masa alama da hannu cewa ya fadi abinda
yake son fada, yace "baban yaya
Muhammad ne yazo, yana waje wai yana
son ganin Daddy" cikin sauri tace "Sakina
zan kira ki later" ta katse kiran tana kara
kallon Hussain da shima yake tsaye yana
jiran abinda zata ce "baban Muhammad
kace? Wanne Muhammad din?" Ya dan
bata rai "Muhammad din Safina mana,
Shine yazo gashi can a waje yace yana
son ganin Daddy, gashi kuma kinga
Daddy tun safe yace kar wanda ya shiga
gurinsa shine nazo inji me za'a gaya
masa?" Ta mike da sauri kamar zata fita waie sai kuma ta dawo da baya "je ka sake duba Daddyn naku ka ga ko ya bude kofar" ya fita amma bata iya hakura ba sai
ta bi bayansa tana jin dadi a ranta, at last iyayen Muhammad sun yunkuro da niyyar yin maganar da zata gyara auren yayan na su.
Sam bata jin dadin yadda Safina take
zama a gidan mijinta amma kuma ya zata
yi? Dangin mahaifin su Safinan sun yi shakulatin bangaro da su kamar ma basu san da su a duniya ba, babu abinda zata ce sun tsinanawa yaran tunda mahaifin su ya mutu sai auren da suka daura wa
Safina wanda a yanzu ba komai bane ba
illa alakakai.
Hussain ya dawo tun kafin ta karasa fita
yana cewa "ya tafi. Ina jin Baba Ya'u ya
gaya masa Daddy baya jin dadi. Har ya
tafi" ta dan dafe kanta da hannun ta cikin
nuna rashin jin dadin ta, ta so ace mazan
sun zauna sun tattauna, wata kila zaman
nasu ya samar wa da yarta ta mafita.
Ta juya ta koma parlor ta zauna tana sauke ajjiyar zuciya hankalin ta gabakidaya yana kan halin da marayun yayan ta suke ciki. Kwana biyun nan ko bacci bata samu tayi saboda damuwa da take ciki da halin da yayan nata suke ciki, hanya kawai take nema da zata bi dan ta gyara musu rayuwar su ta samar musu da farinciki. Amma bata san wacce hanya
bace ba.
Ta zauna tare da sake sauke ajjiyar zuciya tana tuna maganar da Safiyya ta gaya mata few days ago, maganar tayi mata zafi amma kuma gaskiya ce, cewa auren ta da Adam kawai pretending suke yi but
they are not happy with each other, because they lack the major ingredient of marriage, they lack love.
Ta tuna da yadda auren nasu ya kasance, Hajiya ce ta hada su a ganinta zasu cike wa juna gurbin da suke da shi a rayuwar su. Farko duk sunyi rejecting saboda tunanin auren junan su kamar in amana ne ga marigayiya Safiya, amma kuma a hankali bayan an shekara biyu ana jeka ka dawo akan maganar sai suka amince. Safiyya ce sanadiyyar amincewar ta su duk su biyun, Ita ce a tsakiya.
Tun sanda kasa ta rufe don Safiya bayan
Adam babu wanda Safiyya take yarda
dashi sai Sa'adatu, Tun Adam yana yakice
Safiyya daga jikin Sa'adatu musamman
sanda Hajiya ta fara yi masa maganar
auren sa'adatun har daga baya shi da kansa yake kai ta gurin ta ta dan rike masa ita idan zaije wani meeting mai muhimmancin da ba zai iya tafiya da ita
ba. Ta san cewa ya amince da auren ne ba
wai dan yana son ta ba sai don yana son
ya sama wa Safiyya uwa. Ita kuma a nata
bangaren ta amince masa ne dan ta samarwa nata yayan uba. So it was just a transaction a tsakanin su. Kuma over the years duk kanninsu sunyi iyakacin kokarin su wajen ganin sun sauke nauyin yayan da
yaje wuyan su. Duk d dai sun fuskanci challenges akan hakan dan Adam ya kasance mai matukar nuna soyayya ga Safiyya yadda baya hada ta da kowa baya
hada ta da komai. Hakan ya jawo musu matsaloli da yawa, a hankali kuma ta fahimci cewa sam bai
yarda da ita akan Safiyya ba, komai tayi
mata idon sa yana kai, sannan baya taba
neman shawarar ta idan zai yanke hukuncin duk da ya shafi Safiyya, kusan duk abinda ya shafe ta ma boye mata yake yi baya son ta sani,
Hankalin ta bai gama tashi akan hakan ba
sai da ya fara rashin lafiya, rashin lafiyar
da aka tabbatar musu da cewa bata da
magani. Few months after that sai gashi da theory din cewa kusan duk abinda ya mallaka mallakin Safiyya ne. Hakan ya sa tayi tunanin plan ne ya shirya dan ya
mallaka wa Safiyya komai, ita kuma da
yayan da ta haifa masa (twins) ko oho.
Ballantana kuma agololin da tazo da su gidan.
Tayi iyakacin kokarin ta dan gain an warware wannan kullin, har sai da ta tabbatar da cewa magana tabbas ce babu fashi sannan ta hakura. Amma kuma
wannan sai ya sanya tsoro a ranta, tsoro mai girma, idan har haka ne idan mai kasancewa ta kasance da Adam to ya zata yi da yaya hudu? Biyu ma ta kasa
rikewa a lokacin da take da kuruciva ballantana hudu a lokacin da girma ya riga ya zo mata?
Wannan tunanin shi ya dasa toro a ranta
shi kuma tsoron sai ya dasa wata idea a
ranta, idea din hada auren Safiyya da
Mustapha. Idan aka yi auren tabbas zasu
samu security yadda ko babu ran Adam
ba zasu tagayyara ba. Sai dai tun a bugun
farko Safiyya ta debi kasa ta watsa a
idanunsu tace bata so, Sai dai hakan bai
sage mata guiwar ta ba, kamar yadda
hakan bai hana ta zuwar wa Adam da
maganar saurayin da Safiyya take son
yazo gurinsa ya gaishe shi ba. Sai dai kuma taji dadin yadda yayi rejecting maganar tare da nuna cewa sai Safiyya tayi karatu mai zurfi sannan zata yi aure, a
ganin ta wannan wani hope ne na cewa Safiyya zata iya yarda da auren Mustapha kafin lokacin.
A haka kuma kaddara ta fada wa Safiyya,
ciki ya bayyana a gare ya, wannan
maganar ba karamin tayar mata da
hankali tayi ba, tayi takaici kuma tayi
bakin cikin kasancewar haka akan
Safiyya, ta kuma tausaya mata halin da ta
shiga lokacin da tayi niyyar zubar da cikin.
Sai dai kuma a kasan ranta wannan ya
kara mata hope, cikin Safiyya yana nufin
more chances for Mustapha to marry her.
Amma kuma cikin bai fita ba, sai ta boye
maganar kin fitar cikin daga kowa da
kowa, a ranta tana gayawa kanta cewa
tayi hakan ne dan ta hana Safiyya cutar
da kanta, dan kuma ta hana ta aikata
zunubin zubar da ciki, amma deep inside
of her tana ganin ta kara wa Mustapha
chances of marrying Safiyya. With dan
shege, dole na gida za'a aura mata dan a
rufa mata asiri. And who is better to do
that then Mustapha?
Kuma cikin ikon Allah sai gashi Adam ya karbi maganar, amma Safiyya ta rufe idonta tace bata san zance ba. Har ma daga karshe ta zabi Mukhtar akan Mustapha din, shi kuma Adam as always, ya bi bayan yarsa.
Ta sauke ajjiyar zuciya. Wannan abin ya
kona mata ranta sosai, ta san cewa sun
fahimci dukiyar su take so musamman
yadda suke ta boye mata abubuwa, wai
shekara da shekaru kayan Safiya da
sarkokinta suna cikin gidan amma Adam
bai taba gaya mata ba. Ita ma kuma tasan
ba zata ce ta so Safiyya kamar yadda take
son Safina ba, amma tabbas ta so Safiyya
kuma har gobe tana son ta. Bata taba
cutar da ita ba kuma bata jin ko nan gaba
zata cutar da ita. Amma kuma tana son
yayanta sosai, tana kuma son securing
future din su da tata.
Sai dai yanzu duk abubuwa sun rikice
mata, har bata ma san ta inda zata kamo
zarurrukan rayuwar yayan na ta ba
ballantana ta tabbatar da ingancin sakar
su. Safiyya taki auren Mustapha, ga
Safina can kuma yana shan wahala a
hannun mijinta saboda Safiyya, Safiyya…..
Safiyyan kuma da a yanzu babu abinda
zata iya yi mata dan tun daga ciyarwa har
komai nasu ita da yayan ta ita ce take yi musu.
Ta juya ta kalli hanyar dakin Daddy jin ana
kiraye kirayen sallar magrib, tun jiya da ta
yi masa sallama taje ta kwanta bata kuma
saka shi a idonta ba dan tun asubar fari a
rufe kofar sa ya ce babu wanda yake
bukatar gani a ranar. Hatta Ahmad da
yazo sai juyawa yayi ya koma ba tare da
ya ganshi ba. Hatta yar lelen nasa Safiyya haka ta gama knocking kofa da kiran sunansa ta hakura
ta koma sama ita ma ta rufe kanta.
Ita dai bata san me ya same shi ba, tana
kuma fatan ba wani laifin aka ce wani a
cikin yayanta ko ita sunyi ba. Ya kori
Mustapha yace babu shi babu shi har
abada, saura kuma wa? Saura Safina? Ita
ma yace babu shi babu ita?
Ta mike tayi hanyar dakin tana addu'a a
ranta, ga mamakin ta tana buga wa sau
daya sai gashi ya bude mata shi da kansa,
Ta shigo sai tuka wheelchair dinsa ya
koma ciki ba tare da ya ce mata komai ba,
Ta zauna tana kallon sa, kafin tayi magana
yace "ina Hussain. Yazo ya taimaka min
inyi alwala" ta dauko wayarta da sauri
"bara in kira Hassan, Hussain ya fita" sai kuma ta ajiye wayar "ko inzo invi maka to ni?" Bai ce mata komai ba sai ta wyce ta dauko buta da bowl din da taga suna yi
masa alwalar a ciki, tazo ta fara zuba masa ruwan tana kuma wanke masa gabobin alwalar sa harta gama yi sannan ta mike tana kallon sa.
Tabbas akwai wani abu mai girma da yake
damunsa, amma tana tsoron tambaya kar
yace tazo ta bar masa gida irin yadda
yace ranar da ya kori Mustapha. Ta saka
towel tana rage masa damshin ruwan a
jikinsa yadda ta ga yaran suna yi. "Dazu
kayi bako. Mahaifin Muhammad yazo yana
son ganin ka sai aka ce masa baka jin
dadi" kallon da yayi mata sai ya saka ta
tunanin in akwai abinda ta fada mai zafi,
kamar ba zaiyi magana ba sai kuma yace
"me yace? Da wacce maganar yazo?"
Tace "bai ce komai ba. Amma ina tunanin
maganar Safina ne. Kasan fa har yanzu
tana gidan surukan bata koma gidan ta
ba. Maybe zuwa yayi ya bada hakuri akan
abinda yaron yayi sannan a nemi sulhu a
tsakanin yaran",
Ya juya kujerar sa ya kalli gabas sannan ya
tayar da sallah ba tare da yace komai ba,
Kafin ya idar ta fita, Ya juya yana kallon hanyar da tabi sannan ya daka hannu ya kuma daukan wayarsa da take gefen gadon sa, a hankali ya sake playing video din da ya kalla ya kai sau goma a cikin daren jiya da kuma wunin yau. Ya saka camerar din ne dan Safiyya, dan tana acting weird tana kuma boye masa abubuwa da yawa da yake son sani. Amma kuma bai taba tunanin allura zata tono masa garma ba.
Yayi shiru yana kallon Safiyya da
Muhammad a cikin screen din wayarsa,
yana kallon su kuma yana sauraron
maganganun su, yana kuma sauraron
satin kukan safiyyan da yake ratsa ko'ina
na jikin sa. Babu abinda yake so a duniya
sama da ita. Babu kuma abinda ba zai
bayar ba dan ya samar mata da farin ciki
mai dorewa. Dan ya tabbatar cewa
wannan kukan nata shine na karshe a
rayuwar ta. Amma ya zaiyi....? Abinda take
so din is close to impossible.
Ya fahimci abubuwa da yawa a cikin video
din, ciki kuwa har da cewar Safiyya ba
zata taba samun mijin da zai so ta kamar
Muhammad ba, shi bai ma taba tunanin
akwai soyayya mai karfin irin wadda
wadannan yaran suke yiwa junan su ba.
Babu kuma abinda ba zai iya bayarwa a
yanzu dan yaga sun auri junan nasu, ko
da kuwa sauran numfashin da ya rage masa a duniya ne. Amma auren Muhammad ba zai yiwu ba sai da
amincewar iyayen sa. Iyayensa kuma baya
jin zasu aura masa Safiyya musamman
idan suka ji kaddarar da ta fada mata.
Shi kuma a matsayin sa na uban ta ba zai
je ya roke su ba. In yayi hakan ya karasa
zubar mata da guntun mutuncin ta a idon
su. Zai jira ... Zai kuma yi addu'a. Addu'ar
kuwa yayi yanzun ma, addu'ar Allah ya
zaba wa safiyyan sa abinda yafi mata
alkhairi a rayuwa. Yana shafawa Malam
Ya'u ya shigo, ya gaishe shi sannan ya
tabbatar masa da abinda Sa'adatu ta fada
dazu "baban mijin Safina yazo dazu, na
ga kamar maganace mai muhimmanci
yazo da ita amma na gaya masa ba ka jin
dadi sai yace a rabu da kai amma insha
Allah gobe zai dawo ya ganka in ka ji
dadin jikin ka" ya fada cikin girmamawa.
Daddy ya sauke ajiyar zuciya tare da
dawo da video din baya ya cigaba da sake
kalla sannan a hankali yace "gobe? Allah
ya sa muna da rabon ganin goben. In yazo
goben zan ganshi insha Allah"
Maman maman✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️🩹Safiyya❤️🩹
Episode Fifty Nine : Chosen
Her🧕🏻
Na saki labulen tare da komawa baya a
hankali ina kuma rufe bakina da tafin
hannuna. Tabbas Abban Muhammad ne.
Amma me yazo yi gurin Daddy? Me yazo
vi gidan mu? Me ya sani menene kuma bai
sani ba?
Na koma kan gado na na dauki waya ta
and for uncomfortable time na kira
number din Muhammad. Tana ringing, har
tayi ta katse bai dauka ba. Tun safe haka
nake fama. Nayi kiran nayi message din
amma ya share ni. Jiya haka na kwana
ban vi bacci ba kuma a jiyan wayar ta sa
ma bata shiga sam, yau kuma tun sate
tana shiga amma baya dauka.
Na fahimci fushi yake yi da ni, na kuma
san laifina kuma da mana san ransa zai
baci in ya fahimci abinda nayi amma nayi
wa kaina alkawarin kamar yadda nayi
masa alkawari shima wanna insha Allah
zai zama bacin ran mu na karshe, Bani da
tabbas din plan dina zsi tafi smoothly
amma abinda nake da tabbas akan sa shine addu'ar da nayi a kan lamarin, ina da tabbas din Allah zai amsa kuma zai warware mana komal cikin sauki kamar
yadda ya zaba min Mukhtar sanda na roke
shi kuma daga baya ya warware min
aurena dashi cikin ruwan sauki,
Na bude Whatsapp da sauri na tura masa
message din da nake ganin zai dauki
hankalin sa ya kula ni ko da kuwa bai huce
da ni ba, in dai na samu ya kula ni ni
nasan yadda zanyi ya huce din.
"'Abba yazo gidan mu yanzu. I think gurin
Daddy yazo".
He saw the message kamar yadda ya ga
guda goma sha dayan da na tura masa so
far. Na ga