Author : Maman Mama Category : Romantic Hausa Novels
ya dauko takardar
da take cikin aljihunsa ya ajiye mata a
gabanta sannan yace "this is not because
of Safiyya. It is because of you, halin ki da
yanzu duk muka tabbatar ba zaki daina
ba, ba zan iya zabawa yaya na uwa mai
hali irin naki ba. Ina yi miki fatan alkhairi".
Ta daga kai ta kalle shi, yayin da shi kuma
ya mike tare da yiwa iyayensu sallama ya
fita. Babu wanda ya tsayar da shi a cikin
iyayen nasu ballantana har su hana shi vin
abinda ta tabbatar ya riga ya aikata. Abba
ne ta tashi ya dauki takardar da take
gabanta ya karanta sannan ya mika wa
Daddy sannan yayi musu sallama tare da
fatan alkhairi sannan ya fita shima kamar
yadda dan na sa yayi.
Daddy ne ya sake mika mata takardar, ta
bude ta karanta rubutu kamar haka.
"Ni Muhammad Lawan Muhammad. Na
saki matata Safina Ibrahim saki daya. Ina
yi mata fatan alkhairi".
Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: Assalamu alaikum
Gaisuwa tare da fatan alkhairi.
Naga a lot of complains din ku akan kuna
son a kara tsahon labarin Safiyya. My
initial plan was to conclude the book in
the next three episodes. A yanzu dai bana
jin zan iya kara episodes, sai dai idan zan
dauki break of like two weeks in kammala
da was muhimman abubuwan da suke
jira na idan na gama Safiyya, in yaso in na
gama su sai in dawo mu cigaba.
So, kamar kowanne littafi na, wannan
karon ma zan bawa readers damar voting
yadda karshen labarin zai kasance.
1- in cigaba bisa yadda na tsara in
kammala in 3 episodes
2- in kara jan labarin a kara yawan
episodes amma zan dauki break din two
weeks.
Ya kuka gani????
Idan 1 kika zaba kiyi reacting 👍
Idan 2 kika zaba kiyi reacting 🙏
Any other emoji is invalid vote 😀
Za'a gama voting in two days.
[07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: Safiyya……
Falon yayi shiru bayan fitar Muhammad da
Abba. A hankali kuma sai sheshshekar
kukan Safina ya fara mamaye shirun.
Daddy ya sunkuyo da kansa yana kalion
ta, tana zaune kanta a kasa hawayen ta
yana diga akan farar takardar da take
hannun ta, takardar da ta yanke dukkan
alakar da take tsakanin ta da Muhammad.
Ya daga kansa yana kallon Mommy wadda
har lokacin kofar da Muhammad da
babansa suka fita daga ciki take kalla.
Fuskarta da wan irin yanayin da ya kasa
placing.
Sai kuma ta juyo a fusace tana kallon
Safina tace "zaki yi min shiru a gurin nan
ko sai nazo na shake ki kin daina
numfashi?" Bata yi shirun ba kuma bata
ce komai ba, sai ma kukan nata da ya
karu. Mommy ta mike da sauri tayi kanta
duk kuwa da maganar da Daddy yake yi
mata akan ta dakata, ta kai mata mari sai
Safina ta sunkuyar da kanta dan haka
marin ya sauka a saman kanta, sai ta
kwanta a gurin tare da kara sautin kukan
ta "dama haka kuke so ai. Gabakidayan
ku haka kuke so. Babu wanda yake so na.
Babu wanda yake son farin ciki na.
innaliliahi wa inna llaihir rajiun" Mommy ta
saka kata ta dake ta cikin dacin zuciya sal
kuma ta rike kafar tana cije baki "Daddy
ya dan daga murya cikin kokarin ganin
Mommy ta saurare shi "Sa'adatu. Kar ki
dake ta. Da me zata ji?" Mommy ta dawo
ta zauna tana rike kafarta yayin da Safina
ta cigaba da kukan ta, Mommy ta kama
fada, first time da tayi fada in days "ba ma
son ki din, na ce bama son ki din. Ya za'a
yi mu so ki alhalin ke ba kya son kanki? Ya
za'a yi mu damu dake bayan ke baki
damu da kanki ba? Da kina son kanki da
babu yadda za'a yi tun farko ki dama wa
kanki wannan salalar tsiyar. Da ba zaki
gina foundation din auren ki akan karya
da yaudara ba, da ba zaki zubar da
mutumcin ki da kimar ki a idon mijin da
zaki aura da kuma yan uwansa ba. Me
yasa ba zai sake ki ba? Me yasa iyayen sa
ba zasu goyi bayan ya sake ki ba? Me
yasa ba zai ki zabar ki a matsayin uwar
yayansa ba? Waye zai so mace mai irin
halin ki ta tarbiyyan tar da yayan sa?"
Safina ta mike zaune tace "Saboda
Safiyya ne Mommy, Wannan duk excuses
ne yake creating amma saboda Safiyya
ne, Ita ta saka shi ya sake ni.Shi ya gaya
min da bakin sa yace komai yake yi
saboda Safiyya yake y". Mommy tace
"idan ya sake ki saboda Safiyya sai me?
Ke saboda me kika aure shi? Ba saboda
Safiyya ba ne ba?" Satina ta fara girgiza
kai "ba zan iya rabuwa da shi ba Mommy,
Nina hakura zan zauna da Safiyya kuma
ba zan kara ce mata bazawara ba. Na san
akan hakan ta saka shi ya zo ya yaudare
ni ya saka nace na yafe masa sannan ya
sake ni. To wallahi ban yafe ba. Allah ya
isa na, Sai Allah ya saka min. Kuma wallahi
sai ya mayar da ni .....”.
Kuka take daga dukkan alama ma vata
cikin hayyacin ta, Mommy bata san sanda
ta mike ta sake rufe ta da duka ba. Sai da
Daddy ya danna intercom ya kira Hassan
da yake kusa sannan ya zo ya rike
Mommy wadda take ta fada a jikace, daga
ganin ta zaka gane ranta a matukar bace
yake, fadan ma da kyar take yi tana rike
kirjinta "so kike ki kashe ni Safina? So kike
in mutu ki huta tunda dama kince ba na
son ki ai. To wallahi gidan nan zaki bari. Ki
tattara ki koma gurin wadanda suka daura
miki auren tunda sune masu son ki sai su
mayar miki da auren tunda kin ce sai kin
koma, Sai in gani idan igiyar auren a
hannun su take ko a hannun ki ballantana
ku mayar da shi. Kuma wallahi kinji na
rantse, ko da yaron nan ya dawo da
kansa, in kika sake kika koma gidan sa
babu ni babu ke har abada sai dai ki nemi
wata uwar ba ni ba, kinga sai ki kara
tabbatar wa da cewa bana son ki,.…”
Hassan yayi ta kokarin rarrashin Mommy,
Yadda duk ta tayar da hankalin ta sai yake
jin nashi hankalin ya tashi. Dama daga shi
har Hussein tun ranar da Daddy ya zaunar
da su yayi musu magana akan auren da ya
daura wa Safiyya, mijin da ya daura mata
auren da shi da kuma dalilin da yasa yayi
haka suka san cewa wannan ranar zata
zo. And su babbar damuwar su da zuwan
anar shine mahaifiyarsu, suna sonta
sosai ba sa son bacin ranta kuma sun san
dole abinda ya shafi Safina ya shafe ta, su
ma kuma ya shafe su.
Cikin gida ya kama Safina ya shiga da ita
tana ta kuka da farar takarda a hannun ta.
Yana tafiya Daddy ua jawo kujerar sa
wajen Mommy yana kokarin kwantar mata
da hankali, ta girgiza kai "ba zan iya da
wannan abin kunyar na Safina ba. Katsina
zan mayar da ita gurin wadanda suka
daura mata aure ba tare da bincike ba. In
na barta a gidan nan watarana zan kashe
ta ko kuma ita ta kashe ni da bakin cikin
ta*. Ya girgiza mata kai "in kin mayar da
ita Katsina ta yaya zamuyi gyaran
tarbiyyar ta? Kina tunanin su zasu gyara
ta? Kina gani dai a gaban mu yaron nan
yay mana proving cewa akwai matsala a
tarbiyyar da muka bata. It is not too late.
We can help her" ta sake girgiza kai "ba
azo stage din da zamu taimaka matan ba
ai., A yanzu tana bukatar rayuwata fara
koya mata darasi kafin mu mu dora daga
inda rayuwar ta tsaya, The way she is
obsessed with yaron can zata iya daukan
mayafin ta ta koma gidan sa tace ta mayar
da kanta. Gwara tayi nesa da mu. Gwara
tayi nesa da shi".
Daga haka ta mike ta yi cikin gidan, ya
bita da kallo har ta shige yana jin tausayin
ta a ransa. Sunyi mistakes, gabakidayan
su sunyi mistakes, sai dai yana rokon
Allah ya basu ikon gyara mistakes din su
akan Safina da Mustapha kamar yadda ya
bashi ikon yi akan Safiyya.
Amma kuma a ransa bai ji komai ba gane
da sakin Safina da Muhammad yayi,
yanajin cewa hakan shine mafi alkhairi a
gare su baki daya. Zama da wanda ba ka
so ba karamin ciwo ne da shi ba, and
zama da wanda baya son ka is even more
painful.
Sai ya dauki wayarsa, yana lura da yadda
numfashi yake kara yi masa nauyi a cikin
kwanakin nan, and for the first time in
weeks yay dialing number din Mustapha.
Yayi nazari sosai akan case din Mustapha
da Safiyya, ya fahimci cewa Mustapha
yana da laifi kamar yadda su ma shi da
Sa'adatu suke da laifi a cikin lamarin.
Bata jima tana ringing ba Mustaphan ya
dauka, a hankali yace "Daddy" sai kuma
yayi shiru, Daddy ma yayi shirun, har
lokacin yana jin zafin abinda Mustaphan
yayi kokarin yiwa tilon yarsa, amma kuma
shima Mustaphan yana jin sa a ransa
kamar shi ya haife shi. "Ka zo gida...
Daddy ya fada "kazo gida akwai maganar
da zamu y". Daga haka ya katse kiran.
Sai bayan da yayi sallar magrib aka bashi
abinci yaci sannan Mustapha ya zo gidan.
Yayi sallama ya shigo dakin amma sai ya
tsaya a bakin kofa kansa a kasa yana
kallon kafafuwansa. Daddy ya bishi da
kallo, yayi baki, duk ya kara bushewa, duk
babu gayu da daukan wankan nan.
"Zo nan" Daddy ya fada masa with
authority, half expecting him to turn
around ya koma shima yace ai Daddyn ba
babansa ba ne ba kamar yadda Safina ta
fada dazu, amma sal ya ga ya taho din, ya
2o ya zauna a gabansa a kasa sannan
yace "Daddy barka da yamma" Daddy
yayi shiru yana studying dinsa. Tun yana
shekaru goma yake hannunsa, yanzu
gashi yana neman cike shekaru talatin a
duniya, and through all those years, ba
zai ce baya yi masa laifi ba tunda ya san
ko yayan da ya haifa suna yi masa laifi,
amma abinda ya sani shine yana yi masa
biyayya.
"Ina so muyi magana da kai. Ina so kuma
in na gama maganar ka bani amsar abinda
ka fahimta a maganar tawa da kuma
abinda kake tunanin zaka yi a matsayin ka
na babban da a gidan nan".
Sai ya bashi labarin komai akan alakar da
take tsakanin Safina, Safiyya, da
Muhammad. Ya ga alamar ran Mustapha
ya baci "ni ba haka ta ce min ba Daddy,
ba haka Safina ta gaya min ba. Cewa tayi
min a gurin dinner dinta suka hadu kuma
tun daga nan suke in a relationship, tace a
wayar ta ma Muhammad din ya dauki
number din Safiyya" Daddy ya daga
kafada yace "karya ta yi maka.
Tana da karya sosai tun yarinta har karyar
ta zama habit din ta, Yanzu ma akan halin
ta na karya ne mijin ta ya sake ta" suka yi
shiru sai Daddy ya kara da cewa "me kake
tunanin za'a yi akan lamarin ta?"
Mustapha ya danyi tunani sannan yace
"ta ce kowa baya son ta har Mommy. A
barta ta je Katsina ta kwana biyu sai ta
gane ma'anar so din, zata dawo da
kafafuwan ta za kuma ta gane gata ake yi
mata. Yanzu idon ta ya rufe da soyayya ba
zata ji reasons ba. Sannan aje a kwashe
kayanta daga gidan Muhammad as soon
as possible, dan a tabbatar mata da cewa
ba zata koma ba. Duk randa Allah ya sa ta
dawo daga Katsinan ta kuma gane
gaskiya sai ayi mata afuwa a karbe ta, a
kuma mayar da ita makaranta ta karasa
karatun ta. Hakan zai taimaka mata wajen
moving on. Hakan kuma zai bude mata
kofar wasu chances din".
Daddy yayi shiru yana kallon sa. Sai kuma
yayi ajiyar zuciya. Shi bai fiya son
tarbiyya ta hanyar horo ba, ya fi gane
tarbiyya ta hanyar soyayya da kuma jan
yaro a jiki. Amma kuma kamar sun fi shi
gaskiya. She needs to learn her mistakes
by herself. Amma kuma yana tsoron kar a
hure mata kunne a can, kar maimakon
gyaruwa ta kara lalacewa a can. Amma sai
kawai ya hakura, "Okay. Shikenan. Allah
yasa hakan shi ya fi alkhairi. Ta shi kaje".
Sal dal kuma sai Mustaphan ya kasa tashi
ballantana ya tafi din. Ya cigaba da zama
idanunsa a kasa, "Daddy " ya ambata tare
da dago kai yana kalion Daddy, "Daddy
ban san abinda nayi ba. Ban san abinda
aka ce nayi ba, Daddy ko me nayi dan
Allah kayi hakuri",. Daddy ya sake yin
shiru, ya riga ya yafe wa Mustapha abinda
yayi din, amma har yanzu yana jin zafin a
ransa musamman idan ya tuna cewa da
ace Safiyya ta yarda, maybe da matarsa
kawai zai mayar da ita a gidan har sai
randa asiri ya tonu. Ya dauko wayarsa
yana danne danne har ya binciko video
din da ya riga yayi saving. Sai ya juya
wayar ya nuna wa Mustapha. "Dan taya ni
ganin wanna video din".
Mustapha ya karba a ransa yana tunanin
ko menene, sai yaga abinda bai taba
tsammani ba, ya kuma ji abinda bai taba
tsammani ba. Cikin sauri ya danna power
din wayar ya katse videon tare da kashe
wayar gabakidaya, as if yin hakan zai
goge maganar daga memory din Daddy.
Sai kuma suka yi shiru, Mustapha yana
fatan kasa zata tsage ya shige cikin ta.
Daddy yayi magana "ka bani mamaki
Mustapha. Har bragging nake yi cewa ba
ni da matsala da kai. Har kokarin tursasa
yarinyar nan ta aure ka nayi ina ganin
kamar kai ne kafi kowa dacewa da ita. Ka
gaya min idan da akwai wani laifi da nayi
maka da zaka yi min wanna cin mutuncin
a cikin gida na. Ka gaya min" ya karasa
yana kokarin daga muryarsa da bata
fitowa sosai. Mustapha ya san da Daddyn
da ne da yanzu maybe jikinsa yayi tsami,
Amma sai ya kasa daga ido ya kalle shi, to
da wanne idon zai kalle shi ma? Instead
sai ya fara girgiza kansa, amma kuma
bakin ma ya kasa yin motsi ballantana ya
bada hakuri, to mai zai ce masa? Wannan
wanne irin abin kunya ne haka. Ya lura da
video din cctv ne, ya kuma fahimci cewa
ba Safiyya ce ta tona masa asiri ba.
Kamar yadda ya fahimci cewa ba kwace
mijin Safina tayi ba. Ya fahimci Safiyya
bata da laifi, sai ma tarin kaddarori da
suka yi ta saukar mata one after the other.
And he didn't do anything to help her
matters at all.
Daddy ya cigaba da magana "ita Safiyyan
da kayi kokarin zalinta, ita ce mai roko na
kullum akan in yafe maka in dawo da kai
gidana, tace ba ka da wani gida sai
wannan. Yace nan ne gidan ku. Amma kai
ba ka dauke ta kanwa ba. Da ka dauke ta
kanwa da ba zakayi niyyar aikata mata
wanna mummunan abin ba" Mustapha
yayi magana at last "Daddy ba yanzu ba
ne ba wallahi. Wallahi ba yanzu bane ba.
Dan Allah ka fahimta Daddy. Ban san me
zance maka ka fahimta ba. Wallahi nayi
nadama tun dadewa, Dan Allah Daddy
kayi hakuri" shiru Daddy yayi sannan yace
"a hakura ai, Da ace ban hakura ba da ko
gate din gidan nan ba zaka sake gani ba.
Yanzu ka debo kayanka ka dawo dakin ka.
Sannan ka ajiye wannan girman kan ka je
ka karbi aikin da Safiyya ta baka. Ka kuma
hada kan kannenka ka rike su ka gyara
tsakanin su. Sannan ka kula da mahaifiyar
ka. Tashi ka tafi".
Mustapha ya mike, not knowing what to
think, ya kusa fita Daddy ya kira sunan sa,
ya juyo amma still bai kalli Daddyn ba sai
yace "kuma ka samo mata kayi aure. As
soon as possible".
A bangaren Muhammad tun sanda ya fita
daga gidan sai ya dauki hanyar gidan su,
ya san dole yana bukatar suyi maganar
shida iyayen sa, amma kuma hankalin sa
gabakidaya yana kan Safiyya da ya bari a
gida. Bai jima da yin packing a gidan ba
Abba ya shigo shima. Sai ya jira shi yayi
packing sannan suka shiga cikin gidan a
tare, Kamar yadda suka yi tunani Mama
tana ta akin jera musu abincin dare, tayi
wa mijin nata sannu da zuwa sannan ta
juya ta na kalion Muhammad da ya
sunkuyar da kansa kasa yana shafa
gashin kan sa, ta san akwai magana. Ya
gaishe ta amsa tare da tambayar sa
lafiyar Safiyya da kuma Safina "lafiya lau"
kawai ya amsa mata yabi bayan Abba
suka fara shirin alwalar sallar magrib.
Bayan ya gama alwalar ya kira wayar
Safiyya, tana ta ringing bata dauka ba.
"damn it" ya dan fada a hankali. Sai ya
tura mata message "Babe ......... call me
please" sannan ya bi bayan Abba suka
tafi masallaci. Suna fita waje Haidar yana
shigowa, shima sai yabi bayansu suka tafi
tare.
Bayan sunyi Sallah ya dauka zaman ba zai
yi tsaho ba, amma sai yaji magana ta
mika, Abba ne yayi wa Mama bayanin
abinda ya far da kuma hukuncin da
Muhammad din ya yanke, "Allah ya sa
haka shi yafi alkhair'" kawai tace tare da
tashi ta fara zubawa mijin na ta abinci. A
ranta tana jin feelings dinta blank akan
abinda ya far, a wani bangaren ma
godiya tayi ga ubangiji da yasa babu rabo
a tsakani, tana kuma fatan wannan ya
zamo karshen wahalar dan nata a
bangaren aure, ya samu nutsuwa shima
ya samu farin ciki, ko burinta zai cika na
ganin ya zama abin alfahari ga kowa.
Ta zubawa Muhammad abincin shima, ya
dauka ya fara ci yana ta kallon agogon
hannunsa, da sauri ya cinye abincin yana
son yayi musu sallama sai yaji sun dauko
wata maganar kuma. Maganar sabon aikin
da ake nemawa Haidar da kuma filin da
aka siya masa za'a fara gina nasa gida,
Abba so yake Muhammad ya tsaya akan
abin sosai dan shi ba zai samu dama ba.
Sai kuma maganar tafiyar da Abba da
Mama zasu yi Abudabi nan da next week
dan su huta saboda sun sha hidima
kwana biyu sun gaji. Haidar ya fara
tsokanar su cewa da shi zasu yafi, wai a
hannun wa suka barshi? Tunda
Muhammad da Mufida suna gidajensu.
Har yana cewa wai honeymoon su Mama
zasu tafi. Mama ta rankwashe shi akai "ka
koma gidan su Baffa idan ba zaka zauna
anan ba" ya girgiza kai yana kallon
Muhammad "ni na san inda zanje"
Muhammad ya bude ido "kar kace gida
na. Bani da space" Abba yayi dariya "kaji
fa Haidar. Wato wasa tare ci banban. Yar
shinkafar da zasu sammaka a gidan su ita
ce zai yi maka rowa" Haidar ya kai lomar
abinci yace "kuma ni ba ma cin abinci ne
dani sosai ba. Dan kadan ya ishe ni"
Mama tayi dariya "wa yaga rijiya gaba
dubu. Ai ina bayan Gidado, a cikin sati sai
ka talauta su. Duk kayan garar nan sai ka
cinye tas" Haidar ya bata rai "dama ai na
san matsayina a gurin Mama, dadin ta ma
Abba yati so na" Muhammad yace "a'a,
Abba yafi son Mufida", Dariya suka cigaba
da yi suna hirar su, a karshe dai bayan
Haidar yayi kamun kafa da Mama sai aka
yarda cewa zai je gidan Muhammad din,
Sai bayan sallar isha sannan Muhammad
ya samu ya zame daga gurin family dinsa
ya dauki hanyar gida, ya kira number din
Safiyya yafi sau adadin da zai tuna amma
taki dauka, babu irin abinda baya saka wa
a ransa, zuciyar sa kuma tana gaya masa
cewa tana can tana kuka tana tunanin ya
tafi gurin Safina ne. Ai kuwa abinda ya
tarar kenan sanda ya shiga gidan ya kuma
wuce directly har bedroom dinta.
Tana zaune akan gadon ta ta juyawa kofa
baya ta kifa kanta akan cinyoyin ta. Ya
tsaya a bakin kofa yana kallon ta, ya san
tana da kishi sosai, shi kuma kishin nata
burgeshi yake yi most of the times, yana
kara tabbatar masa da soyayyar ta a gare
shi, amma kuma baya son wannan kukan.
Ya danyi gyaran murya sai ta dago kai da
sauri ta juyo ta kalle shi. Ya ga relief a
fuskar ta sosai.
Amma kuma sai ta sake juya fuska ta
daina kallon sa, jan aji, ajin Safiyya yana
daga cikin abinda yake kara masa sonta a
kullum, Ya karasa gabanta ya tsaya yana
kallon ta da murmushi a fuskar