SAFIYYA BOOK COMPLETE MAMAN MAMA.txt

Author :  Maman Mama Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   95 / 113

282K to 285K   out of 336.6K words

zasu
aikata, Kuma alhamdulillah Alhaji Adam,
dani da iyali na bama cikin jahilai, kamar
yadda na tabbatar kaji a cikin maganganun Muhammad".

Daddy ya dago kai yana kallon sa yace
"me kake nufi?...." Abba yace "ina nufin
ina nemawa dana Muhammad auren
Safiyya a gurin ka. In dai har kana ganin
zaka iya bashi ita duk kuwa da alakar da
take tsakanin ku da matar sa ta yanzu".

Daddy yayi shiru yana kallon sa sannan ya
maimaita masa maganar da ya tabbatar
yaji a cikin hirar su Safiyya "Safiyya ta na
da da, wanda ta haifa ba tare da aure ba.
Ka tabbatar a haka kake so ka aura wa
danka ita?" Abba ya gyara zama yace "na
tabbatar, dalili na na farko shine ina da ya,
kwanan nan na aurar da ita, na tabbatar
kuma cewa har yau har gobe bata wuce kaddarar da ta fada kan Safiyya ta fada mata ba. Babu wani a cikin mu da ya isa ya wuce jarabawar sa. Dalili na biyu shine
ban taba ganin soyayya irin wannan da na
gani a tsakanin wadannan yaran ba, zan
iya cewa daga ni har kai munyi kuskuren
barin su suyi zurfi irin wannan, Allah ne ya
kare mana su but they are too close. Yarinyar nan ita ce farin cikin Muhammad, a matsayi na kuma na mahaifin sa zan yi iyakacin kokarin gain na samar masa farin ciki in all the halal ways. Tambaya ta
anan ita ce, zaka iya aura wa yarka mijin
step sister din ta?" Daddy yayi shiru yana dan juyi akan wheelchair dinsa, fuskarsa duke da
murmushi kamar mai tunani, sai kuma
yace "ni uba ne. And it is very okay for
parents to be selfish sometimes when it
comes to their kids. Parents have to be
selfish sometimes" Abba yace shima yana
murmushi "not sometimes, parents are
selfish all the times when it comes to their
kids. Haka din kuma dai da ne. As long as
their selfishness bai zamo shiga iyakar
ubangiji ko danne hakkin wani ba. Then it
is okay 1 am ready to be selfish if you are"
Daddy ya mika masa hannu suka yi musa biha, fuskokin su duk da murmushi, wani bond mai karfi yana creating kansa a tsakanin su.

Abba yace "abu daya ne ya saka ba xan
daura wa Muhammad aure da Safiyya a
yanzu ba. Shine mahaifiyata da yan uwa
na. Bama taba yanke wani babban
hukunci ba tare da mun sanar wa da junan
mu ba. Zan je in same su muyi magana,
zan gaya musu iyakacin abinda nake
ganin ya kamata su sani. Zamu tsayar da
rana cikin satin nan zamu dawo a daura
musu aure"

Bayan sun rabi Daddy ya kira Sufyan ya
sanar masa, sannan ya kira Ahmad shima
ya sanar masa da abinda ake ciki, dukkan
su sunyi murna kuma a take Sufyan ya
shirya suka taho Nigeria shida iyalinsa
dan yana son ayi komai da su, musamman
bayan yayi magana da Hajjo kuma ta
tabbatar masa da cewa ta san mahaifiyar
Muhammad din kuma sunyi maganar
Safiyya da ita few days ago. Dasu akayi
shirin komai, Daddy ya roke su akan kar
su fada wa kowa har sai maganar ta
tabbata, baya son attention din mutane
akan maganar, bayan son attention din
mutane akan Safiyya. Bai gayawa Mommy
ba saboda bash da tabbas din yadda
zata vi reacting to maganar. Ya san kuma in dal ta sani to sai Safina ta sani, duk da yasan hakan ba zai hana faruwar auren ba dan babu mai saka wa ko hana wa a cikin su amma ya san hakan zai iya janyo
unwanted attention din da baya so.

Ko a ransa bai ji cewa yayi wa Safina ba
dai dai ba musamman bayan zargin da
yake yi na cewa ita tayi wa Safiyya
kwacen saurayi, plus mugayen karerayin
da ta fada akan Safiyya dan ta bata ta a
grin Muhammad.

Amma kuma a ransa yasan cewa baiyi wa
Sa'adatu dai dai ba na kin fada mata da
yayi. Sai dai ita mutum ce da ba'a gane
kanta, shi kuma a yanzu da yake gab da
cimma burin sa na gyara kurakuren da
yayi akan Safiyya, baya jin zai iya daukan
risk.

Present day…..


Bayan angwayen sun fita daga gabansa
sun koma babban falon gidan, sai Daddy
ya dauki waya ya kira number din Mommy
kamar yadda ya shirya zai yi. Ya gaya
mata ta same shi a dakin sa amma ta biyo
ta barandar sama dan akwai baki a falon
kasa, sai da ta zo ta zauna sannan yace
mata yana zuwa. So yake kawai ya ga
tuskar Safiyya a lokacin da taga Muhammad a matsayin angon ta. Sai da ya gani din kuwa, and murmushin da ya gani a kan fuskar ta was worth all the
risks he took to put it there. She said
"thank you" to him, he gave her a thumbs
up sannan ya koma cikin dakin sa inda
Mommy take zaune tana jiran sa.

Ya shiga ya rufe kofa sannan ya zauna
suna kallon juna na was seconds sannan
tace "kace inzo zamuyi magana. Kace
kuma akwai baki, bayan dazu babu irin
tambayar da banyi maka ba akan bakin da
za'a yi kaki gaya min su waye. Su waye
bakin? Wacce magana zamuyi?" Ya
cigaba da zama a inda yake, a ransa yayi
hakan ne dan kar tace zata fita wajen
bakin ta basu kunya a cikin surukai.

Ya sauke ajiyar zuciya yace "dazu da
yamma. Na daura auren Safiyya da
Muhammad".

Farko zama tayi kawai tana kallon sa
kamar bata fahimci abinda yace ba, sai
kuma da tsananin mamaki tace "what?
Adam me kake cewa ne haka? Wanne
Muhammad din? Mijin Safina?" Ya gyada
kansa a hankali still idon sa a kanta yana
kokarin studying dinta. Shi da whatever zata yi baya son ta fita falon nan,

Amma sai yaga ta cigaba da yin shiru tana
kallon sa, sai kuma a hankali hawaye suka
fara bin ion ta. Ya fara driving kujerar sa
zuwa gare ta sai ta daga masa hannu.
"Don't! Kar kazo nan. Kar ka gaya min
komai. Bana son jin komai. Ka bani hanya
in wuce. Kwana daya ba zan kara a gidan
ka ba. Yau nayi nadamar shekarun da na
bata tate da kai. Dama na riga na san cewa kai mutum ne mai son kanka amma ban tana zaton ka
kai haka ba sai yau" sai kuma ta koma ta
zauna tare da rushewa da kuka mai kona
zuciya.

Bai ce komai din ba ya cigaba da zama a
bakin kofa. Sai da tayi mai isarta sannan
ta dago tana kallon sa ta sake maimaita
abinda ya gaya mata, maybe dan ta kara
tabbatar wa ba wai ji ne bata yi daidai ba.
"Mijin Safina fa kace ka daura wa aure da
Safiyya. Mijin Safina fa. Kana cikin
hayyacin ka kuwa?" A hankali yace "yana
sonta, kuma tana son shi. Sannan ba
haramun bane ba" ta girgiza kai cikin
dacin zuciya "ita kuma duk abinda take so
Sal ta samu kenan, Ko da kuwa abin ba
nata bane ba na wata ne sal ka kwace ka bata kenan. Wannan wanne irin son kai ne?" Sai ya maimaita mata maganar da suka yi da Abba. "Parents are at times
selfish when it comes to their kids. And
thst is okay. In dai har ba'a shiga hakkin
wani ba".

Tace "hakki? Shiga hakki fa kake magana
akai. You just destroyed Safina's marriage
just so that Safiyya can get married to
mijin Safina da ta gani tana so. Kuma kake
min maganar shiga hakki?" Yay driving
kujerar sa zuwa inda take yace cikin
sassanyar murya "kin taba tambayar
Safina yadda suka had da Muhammad?"
Ta goge hawayen fuskarta "menene hadin
wannan da auren da ka hada?" Yace "it
has everything to do with it. Kin taba
tambayar ta?" Yadda taga ya sassauto da
muryar sa ya saka ta baci amsa duk kuwa
da wani irin haushin sa da take ji daga shi
har yar lelen yar tasa. "Na tambaye ta
tunda ni na damu da ita, kai da baka
dauke ta yar ka ba ai ko maganar ba ka yi
mata ba. Da tace min friend request ya
tura mata a social media sai suka zama
abokai daga baya suka fara soyayya, sai
da incident din ranar dinner dinta ya faru
iyayensa suka zo nan sai na fahimci akwai
wata a kasa, dana sake tambayar ta sai ta
gaya min cewa a social media taga hoton sa ta fara son sa, sai tayi cigiyar ko akwai
wanda ya san shi ya hada su, shine
kanwar sa ta hada su" Daddy yayi ajiyar
zuciya yace "bani da tabbas din gaskiyar
haka ko rashin gaskiyar hakan. Abinda
nake da tabbas a kan sa shine
Muhammad shine yaron da Safiyya ta
saka kika yi min maganar sa shekaru biyu
da suka wuce, shine yaron da suke tare a
garin nan sanda tana karatu, shine yaron
da muka dauka shi yayi mata ciki ita kuma
ta ki gaya mana waye shi saboda ta san
ba shi bane ba. Wannan dalilin ne ya saka
ta yanke jiki ta fadi ranar da aka dura wa
Muhammad aure da Safina. Ina kyautata
zaton hoton auren ta gani a waya. He was
Safiyya's before he became Safina's. Dan
baka ba abin Safina na kwace na bawa
Safiyya ba. Yes, I am selfish, amma ban
shiga hakkin Safina ba".

Tayi shiru tana tunani, and she
remembered wani dare a Berlin da Safiyya
ta farka tana ihun kiran sunan
Muhammad. Shine Muhammad din?

Ta dago kai tana kallon Adam, not
knowing what to say or feel, Sai tace "tun
yaushe kasan hakan? And you never think of telling me? Saboda me? Saboda kana ganin bam isa ba dan bani na haifi Saliyya ba? Saboda kana ganin ban isa kayi shawara dani a duk al'amurra da suka
shafi Safiyya ba? Ba ka taba yarda da ni
akan yarinyar nan ba and it hurts me more
than anything. Ba ka taba gaya min komai
da ya shafe ta, ita ma kuma ba ta gaya
min. Me yasa a matsayi na na uwar ta tun
da taga Muhammad din ba zata same ni
ta gaya min ba?"

Yayi shiru yana kallon ta, and she truly
looked hurt, da alama abin yayi mata ciwo
sosai. Jin bai ce komai ba ta cigaba da
amayar da abinda yake ranta "misali
maganar kayan Safiya, wai ace ka ajiye
kaya a gidan nan kusan shekaru ashirin
amma minda nake matar gidan ban san
suna cikin gidan ba. Sannan yaron nan da
ta haifa, da ga kai har ita babu wanda yayi
min maganar yaron nan sai a gidan biki na
ganshi" Sai yace "Safiyya have her own
reasons da yasa ba ta gaya miki magana,
Ni ma kuma ina da nawa daban. This may
hurt you amma na tabbatar kin san
gaskiya ne. Kina da son abin duniya
Sa'adatu. Kina da son kudi sosai ta yadda
har ba kya iya boyewa. Ni da ke duk
munsan dan su kika aure ni. Safiya have told me a lot about son kudin ku jokingly dan haka tun sanda na aure ki na san halin ki" tayi shiru ranta yana kara
baci akan abinda yace, amma kuma a
kasan ran nata ta sam gaskiya ce. A bitter
truth.

Ya cigaba "it is hard to know where a
person stands with people like you. Ba'a
gane soyayyar ku ta gaskiya ko akasin
hakan. Yanzu misali tun ranar da na gaya
miki cewa almost all of my wealth belongs
to Safiyya sai kika tattara ni kika watsar,
duk wata kulawa da da sanda nake
hidimar fita dake kasashen duniya for
vacations kike yi min yanzu kin daina. Ita
dukiya tana da santsi ko da a gurin wanda
bai damu da ita bane ba, yo ina ga wanda
yake son ta ido rufe? Dan me ba zan ke
boye miki abubuwa ba?".

Ta sunkuyar da kanta kasa hawaye suna
cigaba da zuba a idonta tace "na so
Safiya, in kuma son Safiyya" yace
"sannan kuma kina son dukiyar su. And it
is okay kamar yadda na fada wa Safiyya
sanda ina kokarin convincing dinta ta auri
Mustapha, Life is mostly trade by batter.
Maganar Safiyya kuma dalilin da yasa ba
ta gaya miki gaskiyar abubuwan da suka shafe ta shine saboda mentally ta riga ta saka a ranta cewa ko ta gaya miki ba zaki yarda ba" ta dago kai tace "saboda me? Ita tace maka haka?" Ya girgiza kai,
"Kwanan nan na fahimci hakan. Saboda
tun suna yara in ta gaya miki magana ba
kya dauka kin fi yarda da abinda Safina
tace miki a kanta" ta bude ido "kuma kace
ba ita ta gaya maka ba" yace "ba ita ta
gaya min ba. Maganar naji suna vi ita da
Mustapha, bai musa ba kuma, kamar
yadda bai musa cewa yana shiga dakinta
for years yana neman ta ba".

Wata zabura Mommy tayi ta tashi saura
kadan ta fadi sai ta fada kan kujera, ya
zagayo tare da mika mata hannu duk da
ba iya taimaka matan zai yi ba. Nan take
muryar ta ta cigaba da rawa, hawayen
idon ta ya dawo,. Yace "wannan pain din
shi na gudar miki shi yasa na kasa fada
miki. Yanxu ma ina gaya miki ne kawai dan
ki fahimci maganar sosai kar ki fahimce ta
a bai bai ki yi abinda zai raba min kan
iyali" tace "duk wanda ya gaya maka
wannan maganar karya yake yi. Ko
safiyyan ce ta gaya maka karya take yi
masa, so take kawai ka kore shi dan bata
son auren sa. Wallahi sharri take yi masa"
ya girgiza kai yana dan murmushi "kamar yadda na gaya miki, parents are all selfish when it comes to their kids. Already har kin goyi bayan sa, Kuma again kamar
yadda na gaya miki, babu wanda ya gaya
min, ni na gansu suna maganar, na kuma
ji duk abinda suke cewa" ya dauko
wayarsa "kina so ki gani?" Ta bishi da
kallo kawai ta kasa cewa komai sai yace
"na saka cctv a gidan nan ba tare da kowa
ya sani ba, saboda rashin lafiya tayi
limiting yadda zan saka ido tare da kula
da iyali na, Ta haka na gansu suna
maganar, basu san ina jin su kuma ina
ganin su ba, so it's pure truth. Ya jima
yana so ya lalata ta, innkika je dakin ta
kika duba zaki tarar da wukar da ta ajiye
saboda tayi masa barazana dan ya shigar
mata din, wanna shine dalilin kiyayyar ta
gare shi. Wannan shine dalilin kiyayyar ta
ga auren sa. Wannan kuma shine dalilin
da ya sa na kore shi",

Ya fada yana cigaba da mika mata wayar.
Bata karba ba sai ta kife fuskarta a jikin
kujera tana kukan takaicin halin yayan ta,
ya dora hannun sa a bayan ta cikin shigar
lallashi yace "kiyi hakuri, Babu iyayen da
suke perfect. Ni da ke duk munyi
mistakes gurin raising yayan mu. We
should have separate Mustapha from
Safiyya tun sa da suka balaga dan ba
muharraman juna bane ba. We should have listened more to their small complains and act on them, we should have investigate magana idan suka gaya
mana ba wai mu yarda da su blindly be.
Amma lokaci bai kure ba, we are still alive
and we can fix their lives, wannan shine
abinda nayi ga Safiyya. The biggest
mistake I made a rayuwar ta shine not
listening to her sanda ta ce ta samu
wanda take so zata aura. Da tana gidan
mijinta da maybe duk abinda ya faru da
ita bai faru ba". Ta dago kanta "yanzu to ni yaya zanyi, ta ina zan fara? Me zanyi akan Safina?" Yace
"that is where maganar investigate ta
shigo ciki. We will investigate, mu tace
karya daga cikin gaskiya a maganganun
da Safina ta fada yadda mu zamu samu
fahimtar maganar sosai. Sauran kuma ya
rage na mijin ta. Amma ni in kika tambaye
ni zan ce miki chances are very high that
Safina ta san Muhammad shine saurayin
Safiyya. A tunani na hoton da tayi talla
dashi a social media a wayar Safiyya ta
dauka"

Mommy ta fara girgiza kanta sai ya sake
yin murmushi yace "kamar yadda na gaya
miki, parents are naturally selfish when it comes to their kids"

Daga waje yaji karar bude gate sannan
yaji ana shiga motoci, ya san bakin ne
zasu tati, Sai ya sauke ajiyar zuciya ya
tuka kujerar sa zuwa wajen kararrawar
kiran nurse dinsa, it has been a long day,
yana bukatar yayi bacci kuma,

Ganin haka ya sa Mommy ta mike, still not
knowing what to think or do. Zuciyar ta
tana yi mata zafi, abubuwan sun
cunkushe mata a kanta, bata san menene
zata dauka menene ba zata dauka ba.
Bata tashi fahimtar zurfin bacin ranta ba
sai da ta fita falo tayi mugun gain Safiyya
da Muhammad, ba tare da tace musu
komai ba ta wuce su zuwa sama sannan a
tsaya a bakin window tana kallon motocin
da suka fita daga gidan.

Sai dai motocin ba su jima ta fita ba wata
taxi ta tsaya a kofar gidan sannan wata
mata ta fito daga ciki, ssi da ta shigo gate
sannan Mommy ta gane ta Safina, duk ta
fita daga hayyacin ta kamar mahaukaciya
sabon kamu. Da sauri Mommy ta fito daga
dakin ta sa sauko daga stairs din a dai dai
lokacin da Safina ta shigo falon, idanunta
jage jage da hawaye.

"Mommy zuciya ta zata fashe, Mommy
zan mutu, Wayyo Allah na., Wayyo
Muhammad. Wayyo Abba na",

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Satiyya❤️‍🩹


Episode Sixty Two: Unloved

Not Edited…

"Mommy zuciya ta zata fashe, Mommy
zan mutu. Wayyo Allah na. Wayyo
Muhammad. Wayyo Abba na".

Kuka da hun Safina ya cika gidan
gabakidaya. Babu wanda bai ii ba har
Safiyya da Aunty Hajjo da suke dakin
safiyyan. Suka fito da sauri a lokacin da
Mommy ta fito ita ma ta sauka kasa da
sauri. Sai suka tsaya akan barandar suna
kallon yadda Safina ta zube a tsakiyar
falon tana wani irin kuka.

"Yaya za'a yi min haka a gidan nan. Ta
yaya za'a aurawa Safiyya mijina. Mommy
how can vou let them do this to me?
Wannan wanne irin son kai ne? Wannan
wanne irin rashin adalci ne? Ba zan iya
ganin ta da mijina ba, Mutuwa zanyi
Mommy".

Mommy ta karasa gurin da sauri kamar
zata kifa, ta saka hannu daya ta kamo ta
ta dago ta sannan ta sauke mata wani gigitaccen mari da dayan hannun, Kartin marin ya saka Satina ta sake kifewa a wajen tare da rushewa da wani sabon
kukan. Mommy ta sake kamo ta ta kara
sauke mata wani a dayan side din fuskar.
Nan da nan fuskarta ta kara ja saboda
kuka da kuma zafin marukan, Mommy ta
saka kafa ta dake ta, hakan yasa ita kuma
tayi baya saira kadan ta fadi Aunty Hajjo
da tayi saurin saukowa ta rike ta.

"Sa'adatu menene hakan? Zaki ji mata
ciwo ki jiwa kanki ciwo kema"

Mommy ta nuna Safina cikin dacin zuciya
"ba mutuwa taxe zata yi ba? Gwara in
kashe ta da hannu na akan ta mutu
saboda namijin da bai damu da ita ba.
Gwara in kashe ta da hannuna akan bakin
cikin da take kunsa min akan da baya son
ta. Namijin da ta lalata alakar ta da yar
uwarta saboda shi" ta fada tare da
kwacewa daga hannun Aunty Hajjo ta
koma ta damki kunnuwan Safina duk
biyun ta sske dago ta zaune, Safina tayi
karar azaba tana jin kamar zsta ski fitsari
a wando, Mommy tace "dan ubanki ki
gaya min gaskiya, kin san saurayin ta ne
kafin ki kai masa tallan kanki ko baki sani
ba? Shi yasa kika tafi da shi Katsina dan
ba kya son ya ga Daddy ya gane? Dan ubanki ba zak| gaya min gaskiya ba?"

Aunty Hajjo ta banbare hannun Mommy
daga kunnuwan Safina, ita kuma tayi sauri
ta rike kunnuwan tana jin kamar Mommy
ta cire masa su, ta ma daina kukan yanzu
dan abinda take ji a zuciyar ta yati karfin
kuka, the last person da taje tunanin zata
goya mata baya ta debi kasa ta watsa a
idanunta. Wani irin bakin ciki take ji da
take gain gwara mutuwa akan sa. Yanzu
ne ta kara tabbatar wa cewa kaf duniya
babu wanda yake

95 / 113