Author : Maman Mama Category : Romantic Hausa Novels
da ita har ma in Allah
ya albarkace su da yaya su hayayyafa.
Daga nan sai mission dinta ya chanja
daga neman samun soyayyar Muhammad
zuwa revenge, revenge on muhammad,
revenge for loosing everything to him.
Wannan ya sa ta koma gidan sa ta cigaba
da zama, tana kara gaya wa kanta cewa in
dai tana gidan to ba za'a aura masa
Safiyya ba. Daga Daddy har Mommy har
su ma nasa iyayen ba zasu yi wannan
hadin ba. Ba zasu yarda su hada su kishi
ba.
Amma hukuncin nata bai yi wa Mommy
dadi ba, tayi fushi sosai da ita ta kare
mata zagi tas sannan ta kwashe masu
taimaka mata ta bar ta ita kadai ga rashin
lafiya. Duk da haka bata saduda ba. Ta
daura aniyar ba zata bar Safiyya da
Muhammad su samu abinda suke so ba,
junan su. Mama ta aiko aka dauke ta zuwa
gidan ta, hakan yayi mata dadi first dan
maran tana da kirki sosai kuma zata kula
da ita sosal, amma a yan kwanakin da ta
take yi a gidan Maman sal ta fahimci ta chanja mata fuska sosal. Kamar tana
kulawa da ita ne dan dole.
Sal gabanta ya fadi, zuciyar ta ta raunana
sosal. Tsoro ya kama ta, Kar dai Mama ita
ma ta daina son ta, kar dai ita ma Safiyya
take so yanzu. Wannan ya sa ta gaya
mata abinda take tunanin ko da soyayyar
safiyyan ta fara kafuwa a ranta zai rushe
ta tun kafin ginin yayi nisa.
Ranar mama ta shiga dakin da take tayi
mata maganar lokaci yayi da ya kamata su
koma gidan su ita da Muhammad. Sai
kuma ta dora mata da nasiha akan hakuri
da kaddarar miscarriage da ta same ta.
Sai ta dago kai tana kallon ta tace
"Mama" Mama ta juyo tana kallon ta, tace
"kun san kuwa abinda ya hada mu rigima
a gida ranar da accident din nan ya faru?"
Mama ta cigaba da kallon ta bata ce
komai ba sai Safina ta cigaba da cewa
'"akan kanwa ta ne. Wai kanwata yake so.
Yace sai ya aure ta. Ba zaku aura masa ita
ba ko?" Mama ta dawo ta rike hannunta
tace "ki kwantar da hankalin ki. I already
know about it kuma na riga nayi masa
magana" Safina ta gyada kan ta "Nagode.
Nasan dama ba zaku yarda ba. Kawai ina
damuwa ne dan na san halin Safiyya. Ko
kun matsa masa akan rabuwa da ita ba
lallai ne ita ta rabu da shi ba
Zata makale masa Especially not after
what happened" cikin curiosity Mama
tace "what happened? Menene ya faru?"
Safina ta dago kai ta kalle ta sai ta mayar
da kanta kasa tace "she is trying to cover
up her past" ta danyi shiru sannan ta
dago kai ta cigaba "she have a bastard
child. Tazo garin nan karatu ta koma gida
da ciki. Har yau bata fadi waye uban dan
da ta haifa ba. Ina tsoron kar ta makala wa
Muhammad".
Mama ta zare hannunta daga nata
idanunta suna nuna tsantsar tashin
hankali. A razane tace "Safina? Me kike
fada ne? She is like a sister to you" Safina
ta girgiza kanta "she is never my sister.
Bata da tarbiyya ko kadan" mama ta mike
har lokacin hankalin ta a tashe. "Na shiga
uku" ta fada a hankali, ita Safina sai tayi
mamakin tashin hankalin Maman ta bude
baki sai Mama ta daga mata hannu "I
don't want to hear anymore. Wannan
issue din sirri ya kamata a tsakanin ku ku
family dinta. Bai kamata kina fadawa
mutane ba, Ina kuma fatan bayan ni ba
zaki gaya wa kowa ba" sai ta juya da sauri
ta fita daga dakin,
Salina ta bita da kallo cikin mamakin reaction dinta, sai kuma ta daga kafada
cikin nuna ko in kula. Sai dai zuwa dare ta
fara damuwa da reaction din maman
musamman sanda ta aiko a gaya mata ta
hada kayanta gobe zata koma gidan ta.
Ba kuma ta shigo tayi mata sai da safe ba
kamar yadda ta saba. Sai Safina ta samu
kanta da yin kuka, ta sake rasa wata
soyayyar, ta rasa Mama, Abba dama bata
san inda yasa gaba ba. Yanzu Daddy da
Mommy ne kadai suka rage mata, sai
kuwa Mustapha.
Ta koma gidan mijinta still hoping zaman
nata a gidan zai hana Safiyya shigowa,
still thinking iyayen nasu zasu so ta ko da
this ones ne. Amma sai dai sati guda da
yin maganar ta da Mama ta na zaune a
falon ta ita kadai kamar kullum tana jiran
ta ji shigowar motar sa, duk da ba lallai ne
in ya shigo ya leko in da take ba. A zaman
ne ta dauko wayarta tana chatting da
kawayenta, like always, tana ta zuba musu
karya akan Habibin ta, bayan sun gama
hirar ne kamar an ce mata ta duba status
sal ta duba,
Pictures ta ga ana ta saka wa kamar kuma
duk iri daya ne sai changing position. Yan
wwan Muhammad ne suke saka wa, few of
them da take da numbers dinsu, suma kuma ta karba ne tun lokacin bikin su a
gurin Mutida, tun bayan bikin kuma ba
wata magana suke yi ba. Na Mufida ta
fara budewa dan gain da tayi kamar
Muhammad din ta ne a jiki, gabanta yana
muguwar faduwa.
Ai kuwa hoton yana gama budewa sai
ganin ta tayi ta rikito kasa ba tare da
tasan sanda ta fado din ba. Muhammad
ne rungume da Safiyya kamar zai tsaga
kirjinsa ya saka ta ciki. Fuskarsa dauke da
murmushin da bata taba ganin yayi irin sa
ba, ita kuma shegiyar safiyyan ta
kwantarda kanta a kirjin nasa tare da rufe
idonta. A kasa Mufida ta rubuta
"alhamdulillah. I can't contain my joy. My
Hamma is finally happy"
Next kuma dan short video ne na lokacin
da safiyyan ta taho ta shige cikin
budaddun hannun Muhammad shi kuma
ya rufe da ita yana dan bubbuga bayan ta
kadan tare da rada mata wata magana a
cikin kunne. Shi kuma Mufida tayi
captioning da "an daura an daura, Safiyya
is finally Hamma's",
Then another picture da ya saka zuciyar
Satina ta kusan barin kirjinta, still shina a
gurin ne, gurin da yanzu Safina ta gane da
talon gidan Daddy. Suna tsaye dai still ya
unkuyo da fuskarsa ita kuma ta dago tata, fuskokin su dat dana juna, A cikin
idanuwansu kana iya hango tsantsar
soyayyar junan su.
"Shegiya karuwa" Safina ta fada cikin
karaji. "Wayyo Allah na" ta karasa tana yar
da wayar tare da dora hannayen ta duk
biyun a bisa kanta. Ba zata iya kwatanta
abinda take ji a zuciyarta ba kamar yadda
ba zata iya bada labarin yadda ta fita
daga gidan har taje gidan su ba. Burinta
kawai ta ganta a gaban Mommyn ta, the
only person da take ganin ta rage mata a
cikin masu sonta. Tana son Mommyn ta
rarrashe ta ta gaya mata karya ne abinda
ta gani.
"Mommy zuciya ta zata fashe, Mommy
zan mutu. Wayyo Allah na. Wayyo
Muhammad. Wayyo Abba na".
But instead of rarrashi, sai maruka ta
samu daga Mommyn na ta,
Her🧕🏻
Na jima ina kallon Safina ina kuma
sauraron kalaman ta. Abu daya kalaman
nata suke tunamin, ranar da aka daura
auren ta da Muhammad, halin da na shiga a lokacin da naga hotunan su ita da Muhammad. Furucin da muka yi kusan iri daya ne ni da ita sai dai banbancin
Mommy da ta kira ni kuma a kira Daddy.
Na sauke ajjiyar zuciya sannan na juya zuwa dakina, a hankali na furta "Karma is a real bitch"
Maman Maama✍🏻[07/01, 10:46 pm] +234 906 816 1960: ❤️🩹Safiyya❤️🩹
Episode Sixty Three: Sai da na jima a
zaune a daki katin Aunty Hajjo ta dawo, na
lura duk zuciyar ta a dagule take sanda ta
shigo sal kawai ta zauna tana kallo na
sannan tace "Allah ya ji kan Safiya" a
hankali nace "Ameen" sai ta sake yin shiru
sannan tace "ko zaki zo mu tafi gida tare?
Maybe you will feel more comfortable
there" na girgiza kaina ina murmushi a
raina nace, this is my father's house, I am
not going anywhere, in na bar gidan mu to
gidan miji na na nufa.
Ta sake yin ajliyar zuciya "but be careful
kinji? Be kind to Sa'adatu. Kar kuma ki
kula Safina har kuyi hayaniya kinji? Take
very good care of yourself because akwai
wadanda suka damu da ke sosai, your
father, your husband and junior" ta karasa
tana murmushi, nima dan murmushin nayi
sai kuma nayi sauri na daina dan kar ta
gani, ta sake cewa "da kin yarda zaki bini
da kin ganshi ai. Yana nan yana kokarin
fara rarrafe" jin dai ba xan kula ta akan
maganar sa ba sai ta koma nasihar da
take yi min kafin mu fita gurin Safina akan
hakkokin miji akan matarsa da kuma
hanyoyin da zanbi cikin sauki in sauke
wadannan hakkokin har ma da karin kyautatawar da zata kuma kara min martaba a idonsa, Ni kuma a raina ji nake yil can do all that and more to
Muhammad. Bata yi min zan cen zama da
Safina a matsayin kishiya ba ni ma kuma
naji dadin da bata yi min maganar ba cos I
wasn't ready for that. Ranar farinciki na
ce gwara a barni inyi farin cikin without
kishiya talks, kishiyar ma kuma Safina,
Daga baya sai Abdul ya kira ya a waya
yace tazo su tafi gida, tace min "zan tafi,
amma zan dawo gobe muyi maganar
gyaran amarya, duk da basan lokacin da
zasu saka na tariya ba amma bana jin zai
dauki lokaci tunda alhamdulillah akwai
masu maganar a dukkan bangarorin " ta
karashe tana dariya. Murmushi kadai nayi
sannan nayi mata godiya ta kuma raka ta
zuwa bakin kofa na dawo ciki dan bana
son mu hadu da Abdul ya tsokane ni.
Ina komawa daki a fada kan gado na tare
da lumshe idona ina jin dadin silence din,
in assessing tare da accepting situation
dina, Matar aure, matar Muhammad. Na
danyi dariya kadan sai kuma hawaye ya
biyo bayan dariyar, tun suna fitowa kadan
kadan har suka fara fitowa a guje suna
wanke duk wan sauran bakin ciki da
bacin ran da ke zuciyata dangane da issue din Muhammad, Sal na tashi na kara gyara mayafin jikina sannan na yi sujjada a kasa ina godewa Allah tare da cigaba da zubar da hawaye na akan sallaya ta.
Tabbas na dandana rayuwa, na dja wahala
irin wadda ko makiyi na bana yi wa fatan
ya sha irin ta, amma Allah ya kasance a
tare da ni every step of the way, shi ya
rike hannuna yayi guiding dina tare da
haska min hanyar da nabi, shi ya kasance
tare da ji a lokacin da nake tunanin na
rasa komai, shi ya taya ni zabin abinda
yake shine alkhairi a gare ni sannan kuma
ya juya lamari na in the most simplest way
possible. A cikin ikon sa da rahamar sa
yanzu kusan duk abinda na rasa sun dawo
gare ni, abubuwan kuma da ba zasu dawo
ba sai ya saka min hakuri da dangana a
zuciyata tare da fatan hakurin zai zama
kaffara a gare ni.
Na dago zaune daga sujjada ta ina goge
sauran hawaye na, ni na san wannan ba
shine fadan karshe a rayuwa ta ba, ni na
san wannan Mabudi ne kawai na wata
sabuwar chapter a rayuwa ta, ni na san
jarabawa ta bata kare ba for as long as I
am alive, amma kuma bana jin tsoro ko
kadan dan na tabbatar as long as zan
kasance tare da Allah shima zai kasance
tare da ni, zai kuma yi riko da hannayena
ya taya ni fighting battles dina, battles din
na tabbatar zany wining tunda ina tare da
Allah na.
Daga nan kuma sai na tashi na gabatar da
sallar ishain da ban yi ba. Ina cikin sallar
Esther ta shigo ta ajiye min abinci ta
zauna tana jira na har sai da na idar
sannan na juyo ina kallon ta. Fuskar ta
kamar anyi mata albishir da Jesus dinta
ya zo "Madam! Congratulations. Ina cikin
murna sosai. Mijinki mai kyau mai kyau
mai kyau. I cannot tell you how happy I
am for you" nayi murmushi "thank you
Esther.
And I don't know how to say this to you
but just know that kinyi matukar kokari
gurin tabbatuwar wannan maganar" ta
dan bata rai tana tunanin kokarin da tayi
sai kuma ta sake washe baki "the pepper
soups! Guda uku nayi. Da na naman rago,
dana kaji da kuma na kifi"., Nayi murmushi
kawai bance komai ba sai ta sake cewa
"dazu na ban san angwayen zasu zo ba
banyi musu komai ba, sai ga Alhaji Ahmed
nan ya kawo snacks da yawa yace in kai
musu da drinks" na gyada kai kawai "ya
kyauta. Ya kyauta sosai'",. Ta nuna min tray
din da ta shigo dashi "white rice na dafa
miki da sauran fish pepper soup din dazu
Na san kina so. And I made your
timoothie!" Ta fada with excitement. Na dauki cup din a zuka through straw din
da yake saman sa yayin da ita kuma ta
zuba min ido tana kallona har na ajiye
sannan nace "duk kamun kafar ki dai ba
zan tafi da ke ba. Kina nan gidan" ta bata
rai "haba madam haba madam" nayi
dariya "sai abinda Mommy tace, kin san
dai ba zan dauke mata ke ba ko?" Ta
gyara zama "shawara Madam, na yarda a
kawo wasu masu aikin, and then in kin
tashi tafiya I will just say tunda akwai
wasu ni zan biki, kinga ba zata ce komai
ba" nayi shiru bance komai ba sai ta sake
cewa "please!'" Nayi ajjiyar zuciya "okay.
Shikenan. Get them. Guda uku, Sai mu
gwada su mu gani" ta mike da sauri tana
murna "na gode, thank you Madam".
Tana fita na bude abincina na ga yadda ta
kawata white rice din with vegetables.
Pepper soup din ma daga gani ba wai
saura bane ba sabo ne tayi min, duk kuma
na san na kamun kafa ne. Sai na samu
kaina da cin abinci na cikin nishadi,
abubuwa da yawa suna yawo a kaina,
plans nake making iri iri, in saka in
warware in girgiza kai a inyi murmushi
duk ni kadai. Sai a lokacin na tuno da
cewa tun rana waya ta a kashe take, Allah
kadal ya san sau nawa Muhammad ya kira ni a yau din nan, To dama ya lafiyar kura?
Na dauko wayar bayan na gama cin
abincin na kira Esther tazo ta kwashe
kayan. Na kunna, messages suka shigo
min sosai, na sa na fara nema kuma shi na
fara budewa na karanta.
"I am yours, and you are mine. Forever
and ever"
Nayi murmushi na sake karantawa sannan
na kara karantawa. "Ina sonka sosai
Muhammad" na fada a hankali. At a point
na fitar da rai completely da auren
Muhammad. A lokacin da na zabi Mukhtar
da kaina na dauka na rabu da Muhammad
har abada. Na dauka kuma zan zauna da
Mukhtar har abada. Amma ashe Allah
yana nasa plans din.
Naji ina son kiranshi inji muryarshi, for the
first time as his wife, dan na san shi yayi
ta kira na wayar a rufe, amma sai na samu
kaina da kasa yin hakan. So nake ya fara
kirana, ajin nan dai ba zan sake shi ba sai
na ja abina. Sai dai shiru bai kira ba. Har
na tashi na dan motsa jikina saboda
abincin da naci yayi min nauyi na kuma
gyara gurin kwanciyata tare da rage kayan
jikina nayi shirin bacci amma bai kira ba.
Sal na kwanta akan gado a fara karanta sakonnin da aka turo min.
Sal na lura da yawa yan uwan mu na Kano
sun samu labarin daurin aure na ashe,
duk sun turo min sakon taya murna,
Salima da Salim ma sun turo min, salima
ta ce ta kira wayar a kashe amma zata zo
gobe. Sai kuma wani message from
unknown number
'"Ina miki son da ba zan taba iya hakura da
ke ba Safiyya, ina miki son da zan iya taba
bari wani ya same ki ba bayan ni Safiyya.
Especially not him"
Na mike zaune tare da sake karanta
message din. Tabbas na gane wanda ya
turo sakon duk da ba number dinsa bace
ba kuma bai rubuta sunan sa ba. A take
nayi wa security na forwarding message
din tare da number din. Minti biyu suka yi
responding. "An sauke layin. But we will
be at alert. Be careful". Har na ajiye wayar
sai kuma na dauka da kira chief of the
security din nace masa "in kun ganshi
anywhere around this house or around
me, ku harbe shi a kafa ku mika wa police
shi. You still have the restriction order?"
Yace "yes boss, just lock your doors and
windows. We will get you a gun tomorrow"
Na katse kiran tare da dafe kaina ina jin
raina yana matukar baci. It hurts me a lot
idan na tuna da Mukhtar din da na sani,
Mukhtar din da na tashi together with,
sannan kuma na tuno wannan ranar, na
tuno abinda yayi min wannan ranar, Bana
jin da ace wani ne daban abin zaiyi min
ciwo irin haka, ko da kuwa ace Mustapha
ne.
Sai da na tuno da Mustapha sannan na
tuna da cewa naga sunansa as I was
scrolling through messages, amma ban
dauki wayar ba sai na tashi na rufe kofa ta
na kuma tabbatar dukkan tagogin dakin
da kuma na toilet a rufe suke. Na kuma
tabbatar wuka ta tana nan a inda nake
ajiye ta sannan na koma na kwanta.
Mukhtar ba zai kuma taba ni ba, har
abada.
Message din Mustapha na nemo,
"Naji abinda kika yi. Kin kyauta"
Ban bashi amsa ba kawai na fita ina jin
nadamar budewa, suna so su bata min daren farin ciki na. Gashi Muhammad din ma yaki kirana. Amma sai naki bawa kaina damar yin bacin rai, not tonight. Instead, sal na dauko chats din mu da Muhammad nayi ta karantawa ina murmushi tare da dariya at the same time, a haka har bacci ya dauke ni,
Cikin baccin naji wayata tana kara, na bude idona da kyar sannan na lalubota, sai lokacin ma na fahimci ko fitilar dakin ban kashe ba bacci ya dauke ni. Sunan
Muhammad na gani, na duba time naga 12:45, na dauka na dora akan kunne na amma bance komai ba sai yace "kar dai kice min bacci kike yi" na juya idona kamar yana kallo na sannan cikin muryar bacci nace "to me zanyi idan banyi bacci ba? Tunda babu wanda ya damu da ni ballantana ya kira ni yay min hira" ya. danyi dariya "amma kin bani mamaki. Ni da na dauka yau kwana zaki yi kina rawa da murnar farinciki burinki ya cika?" Na san tsokana yake ji da ita nima cikin tsokanar nace "ashe abinda kake yi kenan shi yasa baka kira ba? Kana can kana rawa da murnar burin ka ya cika. Na san fa yadda ka mace a kaina baka ji baka gani" yace "ohh da gaske. In na mutu a soyayyar ki ma ai tare muka mutu ni da ke. Har da kuka fa dazu saboda murna. Murnar kin samu santalelen bafulatani kama ta" nayi dariya ina jin baccin yana barin ido na nace "shi yasa naga ai har nayi baccina amma kai ka kasa bacci sai da ka kira kaji murya ta. Dan in baka ji ba ba zaka iya bacci ba" yace "wannan kuma kin fadi gaskiya. Ba zan iya barci ba sai naji muryar ki. Sai yanzu na shigo gida tun dazu ban samu privacy ba. Ina ta fama da baki. Bayan bakin kuma sun tafi sai muka zauna da Abba da Mama muna ta magana. I told them all about you. But sai na fahimci sun san some parts of the story" na lumshe idona na bude ina jin girmansu yana karuwa a zuciya ta for accepting me the way I am kuma ba tare da wani bata lokaci ko wasu conditions ba.
Ya cigaba "Abba was a bit concerned
about all the ...….. He was concerned
about the..........." Na karasa masa "about
the wealth" yace "yeah,