SAFIYYA BOOK COMPLETE MAMAN MAMA.txt

Author :  Maman Mama Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   96 / 113

285K to 288K   out of 336.6K words

son sa, me ya rage
mata to? Me zata zauna tayi a duniyar
kuma?

People have always love Safiyya more…...
Tun suna yara, hatta Mommyn ta ma da
ba ita ta haife ta ba gani take yi kamar tafi
son Safiyya a kanta. A makaranta ma anfi
son Safiyya duk kuwa da cewa tafi
Safiyyan hakuri da biyayya, Safiyya taurin
kai da tsaurin ido da rashin kunya da
shegen iyayi da manyance wanda Safina
take finding very annoying amma kuma
still an fi son Safiyya. Ko kawa tayi to
kuwa in dai har ta hada su da Safiyya sai
ta ga kawar ta koma ta zama kawar
Safiyya ita ta koma second choice.

Ballantana Daddy da baya boyewa. Daddy
bai taba hada Safiyya da kowa ko komai a
rayuwar sa ba. And that made her crave for a father's love duk kuwa da cewa yana
sauke musu dukkan hakkokin uba amma
tana kwadayin soyayyar da yake yiwa
Satiyya. Sail dai in Safiyya bata ambata ko
kuma ta nuna tana son abu ba to sai ya
samo mata shi sai dai in har abin mai
cutar wane. Wani lokacin Safina har
mamakin audacity din Safiyya take yi,
tana kuma jin haushin iyayen nasu akan
biye mata akan duk abinda ranta yake so,
tana ganin bata ta suke yi. A hankali ta
fara kallon Safiyya a matsayin marar
tarbiyya, ta kuma fara ganin kanta a
matsayin ita ce mai tarbiyya. And she
started wanting people to believe that.
Tun daga lokacin ta fara jingina duk wani
abu marar kyau zuwa da Safiyya, duk
wani abu mai kyau kuma zuwa gare ta.
Like, as the good girl that she is, she
deserves everything good. Mentally kuma
ta saka a ra ta cewa Safiyya will end up
bad, tunda dai tarbiyya bata ishe ta ba. Wannan ya sa duk wani laifi da akayi automatically zata jingina shi ga Safiyya. Ko menene gani take yi tabbas Safiyya
zata iya aikata shi tunda bata da tarbiyya
ba kuma ta tsoron kowa, to tsoron me
zata ji tunda ba hukuntata za'a yi ba? lya kaci Mommy tayi ta mata fada idan Safina
tace tayi wani abu, shima fadan daga
baya saboda rashin tarbiyya in Mommy
tana yi mata shi sai ta saka hannu ta
toshe kunnuwanta ma'ana ba ma zsta j
ba ballantana tayi aiki da shi, ta kuma rufe
idonta ma'ana ba ma zata gani ba
ballantana abin ya dame ta.
Wanna ba karamin bata ran Safina yake
yi ba, tana ganin Safiyya ta raina mata
uwa, wato ta mayar da ita mahaukaciya ko
kuma karyar da zata yi ta haushin ta ita
kadai. Dan haka ta cigaba da jiran that
bad thing da tasan tabbas tana nan
tahowa kan bad girl like Safiyya. And it
eventually happened. Rana daya
Mustapha da Daddy suka dawo da ita
daga Abuja, Mustapha kuma ya sanar
musu ita da Mommy cewa Safiyya ta fara
shaye shaye, wannan maganar ta taba
zuciyar Mommy sosai, it kuma Safina ba
zata ce tayi mamakin hakan ba dan dama
ita ta san karshen alawa kasa, duk kuwa
wanda ya sai rariya ya san zata zubar da
ruwa, a ranta kuma sai ta saka kan cewa
downfall din Safiyya ne ya fara, and more
is coming. Kamar kuma ta fada da bakin
Mala"iku sai gashi ta shiga dakin Safiyya
ranar nan ta ganta kwance male male a
cikin jini da kuma kwalin maganin zubar
da ciki a gee. Lokaci daya ta fahimci
abinda ya faru, Safiyya cikin shege tayi kuma ta zubar da shi.

ita ta fada wa iyayen su, and da kyar ta iya
containing dadin da ya cika zuciyar ta
sanda ta ga Daddy ya dauki belt yana
tafka wa Safiyya, she deserves that, the
spoilt little bitch. And a ranta ta sake
cewa kadan ma kenan, More are coming.
A ranta tayi niyyar sanarwa da duk
kawayensu da suke bawa Safiyya more
importance than her, dan su san cewa
Safiyya is the bad one ita kuma ita ce ta
gari, amma sai Mommy ta kira su har daki
uta da Mustapha ta ja musu kunne da
manya manyan kalmomi akan duk wanda
a cikin su ya fitar da maganar waje to
babu ita babu shi har abada. Ta kuma
sake sealing bakunan su ta hanyar kara
tabbatar musu da kudurin ta na aura wa
Mustapha Safiyya. "Dan haka in kun fitar
da maganar ma nan gaba ku zata shafa
idan akayi auren" "amma Mommy in akayi
haka ba'a yiwa yaya Mustapha adalci ba,
wanna lalatacciyar yarinyar za'a aura
masa? Yarinyar da take shaye shaye ga
kuma cikin shege tayi sai kuma a makala
masa ita?" Mommy ta doke bakinta da
bayan hannun ta "kar in sake ji. Wallahi
Safina ki fita daga ido na, Kar in sake jin
kin fadi wadannan mugayen kalaman a
kan yaruwarki. Kaddara ce ta same ta
kuma babu wanda ya wuce wannan
kaddarar" Sai Safina ta juyar da kai tana hawaye. Me yasa su basa ganin abinda
take gani ne? Me yasa idon su yake
rufewa akan Safiyya ne?
Amma kuma dole tayi shiru din, dan ta
fahimci Mommy da gaske take sai ta
bala'in bata mata rai in dai maganar nan
ta fita tunda daga alama Mustapha ya
karbi maganar auren kuma ba zai fitar da
maganar ba. Dan haka ana jin maganar a
waje Mommy zata gane ita ce.
Amma kuma ta wani bangaren sai taji
dadin maganar auren Safiyya da
Mustapha. Hakan yana nufin a step
toward cikar muradin zuciyarta. Sai kuma
ta samu kanta da murmushi bayan ta
goge hawayen fuskarta. Muhammad will
soon be hers insha Allah.
Tun hutun Safiyya na farko bayan ta fara
MD University ta zo wa da Safina labarin
Muhammad. "Nayi saurayi Safina" ta fada
boldly kamar yadda ta saba yin maganar
ta direct, ko tayi maka dadi ko akasin haka
kai ka sani. "Malam Muhammadu. Malami
ne a MD" Safina tayi dariya, sunan sounds
like sunan tsohon lecturer mai fama da
tsohuwar mota. "Allah ya shire ki Safiyya.
Ke kuma duk iyayin nan naki akan lecturer
zaki kare?" Safiya tayi murmushi "ina son
sa a haka. Shima kuma yana so na sosai. Love is all that matters" ta fada tana juyi
akan gado dramatically. Safina ta girgiza
kai kawai a ranta tana jin downfall din
Safiyya yazo finally dan in dai tace tana
son abu to da wahala idan bata samu ba,
she will end up with tsohon lecturer
maybe ma mai mata da yaya, watakila ma
ya kusa retire.

Yayin da ita kuma Safina zata samu prince
charming dinta. Ta rufe ido tana lissafo
kamannin sa a ranta, dogo, fari tas,
masculine, kyakkyawan gaske with a true
red lips that she so much likes. Mai
matukar sonta kamar ya chine ta. Very
romantic wanda zai ke kashe ta da
kalamai da tarairaya da kulawa. And also
very rich, mai hawa manyan motoci da
saka suturu masu dan karen tsada. Tayi
murmushi, Safiyya can go with her Malam
Muhammadu. Ita kam ta riga ta gama
picturing irin mijin da take so and they will
live happily ever after, while Safiyya's
marriage will probably crumble saboda
rashin tarbiyyar ta.
Wanna buri da ta dora akan irin kalar
mijin da take so shi ya hana ta kula
samari, samari da yawa suna nuna suna
sonta, duk da dai most of them ba sa iya fuska, amma kat cikin su babu wanda yayi
fitting dream husband dinta, Shiga jami'ar
da tayi ita ma anan kano ya kara mata
yawan masu cewa suna sonta, ciki kuwa
ranar nan har da wani malamin
makarantar ta su da har ya bata dariya
ma, ta yaya ma zata kula shi? Sai kace
wata Safiyya. So take ta kere Safiyya a
miji kamar yadda ita kuma ta kere ta a
komai banda tarbiyya.
A haka har Safiyya ta sake dawowa next
hutu, a lokacin ne take gaya mata already
"malam Muhammadu" ya fara yi mata
maganar aure. "Kin san kuma Daddy ya ja
min kunne akan yin soyayya, tsoro na ke
j'"' sai Safina tayi dariya "ke ce fa Safiyya,
da kin yi wa Daddy kuka shikenan zai aura
miki Malam Muhammadun ki" amma sai
Safiyya ta girgiza kai "no, ba zai yi ba. He
is very serious about it". Wannan kuma ya
saka Safina wondering why? Me yasa
Daddy zai hana Safiyya samari amma ita
bai ce mata komai akan hakan ba?
Sai kuma ta samu amsa dinta a ranar 20th
birthday din Safiyya. Ranar da Daddy ya
tara su tare da wadansu mutane da suka
sha suits, ya shirya musu tatsuniyar cewa
kusan duk abinda ya mallaka mallakin
Safiyya ne. Ranar yadda Safina taga rana haka taga dare. How? Why? Ta yaya
Safiyya zata samu wanna abin, she do
not deserve it. Ita ma kamar Mommy,
daga farko ta dauka son zuciya ne kawai
ya saka daddyn fadar haka dan ya san ya
fara rashin lafiyar da bata da magani
kuma in ya mutu gadon Safiyya bashi da
yawa, sauran duk na Mommy ne da twins,
amma daga baya ita ma sai ta fahimci da
gasje maganar haka take. Abin ya kona
mata zuciya sosai. Sannan ya dasa mata
wani abu a zuciyarta game da Safiyya
bayan kiyayya. Hassada.
Bata tashi kara raina kanta ba sai da ta
fahimci '"malam Muhammadu" fa is not
someone she pictured him to be. Ba
tsoho bane ba, and he is far from being
poor. Ba wai ganin shi tayi ba amma daga
yadda suke zama suyi ta waya da Safiyya
da kuma irin kalaman da Safiyya take
furta masa ta cikin wayar a matsayin
amsar maganganun sa ta fara fahimtar
hakan. And then one day she saw a
glimpse of him sanda suna video call da
Safiyya. Sai da ta dafe kirjinta ta shiga
ban daki ta rufe kofa tana mayar da
numfashi. He looks exactly like yadda
take picturing prince charming dinta. And
she fall instantly in love.
Har ta sake fitowa basu gama wayar ba, bata jin me yake cewa saboda ear piece
ne a kunnen Safiyya din amma daga
yadda take ta zabga murmushi tana
lumshe ido ya tabbatar wa da Safina cewa
kalaman da yake gaya mata are exactly
irin kamalan da take so prince charming
dinta ya ke gaya mata.
Ranar har sai da tayi kuka. Wani irin zafi
zuciyar ta take yi mata. How can Safiyya
have that? How can she have everything
that she wanted for her self? As the good
girl that she is, ita ta cancanci everything
good ba wai Safiyyan da babu wanda ya
isa ya gaya mata magana ta ji ba. Sai dai
kuma bata san ta yadda zata bullowa
lamarin ba. Ba ta san me zata yi ba. Daga
nan ta ajiye duk wasu burikan ta a gefe,
dukkan rayuwar ta a gefe ta koma living
and breathing for Muhammad. Hanyar
duk da zata bi ta same shi ita take so.

Har wata rama tayi a cikin kwanaki kadan,
har sai da Mommy ta tambaye ta in akwai
abinda yake damun ta amma tace babu
komai dan tasan Mommy ba zata taba
goya mata baya ba wajen cimma burinta.
Daga nan soyayyar Muhammad ta fara jan
ta, ta fara daukan wayar Safiyya with
every chance that she gets dan ta kalli hotunan Muhammad, and the more she
looks at him the she fall deeper in love
with him.
Komai na shi yayi mata exactly irin yadda
take so, his smile, ya subhanallah! Bata jin
akwai abinda ba zata iya sadaukar wa ba
just to have him look at her and give her
that smile. Or kiss her with those lips. Or
even.…...... Bata jin akwai abinda ko wanda
ba zata iya rabuwa da shi ba to get
Muhammad. Especially Safiyya.
A haka Safiyya ta koma makaranta, taking
all the links to Muhammad with her.
Wannan semester din hauka ne kawai
Safina bata yi ba. Ta yi iyakacin neman da
zata yi masa a social media ta rasa shi. Ko
mai kama da shi bata gani ba. With him a
zuciyarta gani take yi dukkan maza kamar
dodanni ne. Bata da wani abu da ta sani
game da shi sai sunan sa, Malam
Muhammadu, what kind of name is that?
Sai dai bata da wanda zatayi shawara da
shi idan ba zuciyar ta ba. Zuciyar tata
kuma a cike take da soyayyar sa, dan
haka zuciyar tata ta bata shawarar da
take ganin ita zata kai ta ga samun
muradin ta. Wannan yasa Safiyya tana
sake dawowa wani hutun ta dauki wayarta
la nemo number din sa a ciki. “Pyar💕” la ga any saving, ta gane shine amma

ta ga any saving, ta gane shine amma
kuma wani irin kishin safiyyan taji tana ji,
da kyar ta lallashi zuciyarta ta hana kanta
fasa wayar dan takaici. Ta dauki number
din kawai tayi saving a tata wayar da
"Habibie"
Tabbas tana jin labarai iri iri a social
media, labarai akan halin maza da yadida
basu da amana. Sau nawa saurayi yana
soyayya da ya zai fasa ya dawo kan
kanwa? Sau nawa saurayi zai hada
kawaye biyu yayi soyayya da su a lokaci
daya? Sau nawa saurayi zai auri kawa
daga baya yazo ya sake auran aminiyarta?
Dan Muhammad yana soyayya da Safiyya
hakan ba ya nufin cewa ba zai so ta ba ita
ma. Musamman tunda dai itana ta a da
kyawun ta dai dai gwargwado kuma tafi
Safiyya tarbiyya. Har a gurin malamai
kuwa taji cewa maza babu abinda suke so
irin mace mai biyayya. Basa son mai
taurin kai. Safiyya and taurin kai kuwa are
five and six, dan haka kwace saurayi a
hannun ta ba zaiyi mata wahala ba.
Wannan ya kara mata kwarin gwiwa sosai.
Ta kuma yi addu'a akan Allah ya bata
nasara akan sa, sannan ta zauna ta tsara
kalaman da zata gaya masa. Sai da ta
gama duk shirin ta sannan ta shiga daki ta
rule kofa ta kira shi, Bai dauka ba. Sai da tayi masa five missed calls sannan ta
hakura tare da gaya wa kanta cewa yana
wani uzuri ne, sai kuma ta yanke hukuncin
zata rubuta message ta tura masa, amma
kuma tana tsananin, tsananin son jin
muryarsa.
Ga mamakin ta tun kafin ta tashi daga
gurin sai gashi ya kira ta back, sai da
zuciyar ta tayi wata bugawa mai karfi
ganin sunan Habibi yana yawo akan
screen din ta. Ta lumshe ido ta bude tare
da sauke ajiyar zuciya sannan ta dauka.
Tas taji muryarsa ta fito ta cikin wayar,
with his fulani accent, "hello, who is
there?" Ta sake sauke wata ajjiyar zuciyar,
muryar sounded exactly like yadda tayi
tunani, sannan a hankali ta sake tata
muryar kasa ta fara gaishe shi, tun kafin
ta karasa ya katse ta "I missed calls from
this number, wacece? how can I help
you?" Tace "wata zuciya ce da ta kasa
controlling kanta har sai da ta kira ka dan
tayi maka fatan alkhairi tare da shaida
maka cewa tana cike da muradin.......
." Ya
dakatar da ita "thank you for the call and
the care, But I am not interested" and
then a sound na katse kira.
Ta jima da wayar a kunnen ta ta ma kasa
sauke ta kasa, Wani irin daci take ji a ranta, dacin da har sal da ya sauko da hawaye daga idonta zuwa kuncin ta, Shikenan? Just two seconds na muryar sa
shine reward din soyayyar ta?

Zuciyar ta bata sake breaking ba sai
washegari da ta sake gwada kiran sa taji
cewa yayi blocking number dinta. Tana
shiga dakin Safiyya kuma ta tarar da ita
tana ta dariya a waya kuma ta san da
shine. "I miss You too. Soon zan dawo
ai…..." Safina ta juya da sauri zuwa nata
dakin ta fada kan gado ta kama kuka.
Kukan da tayi na farko a kansa, not
knowing it is just the beginning.
To add to her agony, bayan ta kuma
samun damar daukan wayar Safiyya da
niyyar sake dubawa ko zata samu wata
number din sa ko kuma social media
handles dinsa, ko dai wani abu da zai yi
linking dinta da shi, sai ta tarar safiyyan ta
chanja password din watar tata daga
wanda ta sani, tayi ta kokarin guessing
amma ta kasa bude wayar, daga baya ma
sai wayar ta rufe kanta, takaici ya kara
rufe Safina ta tashi ta fita. A haka har
lokacin komawar Safiyya makaranta yayi,
bata samu wani abu da zai sake linking
dinta da shi ba. A lokacin ne kuma ta lura
da hoton da Safiyya ta chanja na kan
screen din ta da shi. Hoton su ne shi da ita a gaban motar ta, motar da aka siya
mata saboda gata duk kuwa da cewa a
hostel take zaune amma ita aka ki siya
mata aka ce ta ringa amfani da motocin
gidan. Daga alama Safiyya ce ta dauki
hoton ta hanyar selfie, yana sanye da
kananan kayan da suka kara fito da kirar
jikin sa, ya dan hade ransa kadan
hannayensa a cikin aljihun wandonsa
yayin da Safiyya take dariyar da take
bayyana kyawawan hakoranta, daga
alama tsokanar sa take yi. Safina taji wani
kishi ya kara sarkafe zuciyarta, ta saka
hannu ta toshe fuskar Safiyya ta bar tasa
shi kadai tana imagining fuskarta a inda ta
safiyyan take. Tabbas ba karamin kyau
zasu yi ba. Tabbas ba karamin dacewa
zasu yi da juna ba.
Sai kuma wani tunani ya zo mata, ta daga
wayarta ta bude camera sannan ta saita
wayar safiyyan ta dauki screen din wayar
a hoto bayan tayi zooming ta tabbatar
yayi clear sosai. Ta ajiye wayar safiyyan
sannan ta koma kan hoton da ta dauka a
wayarta tayi cropping ta cire Safiyya ta
bar shi shi kadai. Sai taga ya kara yi mata
kyau sosai, ta jima tana kallon sa sonsa
yana karuwa a cikin zuciyarta kamar zai
fasa kirjinta ya fito. A take zuciyar tata ta
sake bata wata shawarar, ta dauka ba tare
da musu ba, ta juya zuwa dakinta ta zauna tare da hawa Instagram ta nemo
blog din da ta kanga ana posting irin
abinda take so, ta tura hoton tare da
rubutu kamar haka.
"Salam malama, Hide my ID please. Dan
Allah ina cigiyar wannan bawan Allahn ne.
Allah ya saka min soyayyar sa a cikin
zuciyata kuma na rasa a inda zan same
shi".
Ta tura sannan ta zauna zaman jira. Ranar
da wayarta ta wuni ta kuma kwana a
hannun ta amma malama bata yi posting
ba, washegari ma haka. Daya washegarin
ma haka. A ranar ne kuma Safiyya ta sake
komawa makaranta. Sai a daren ranar ne
ta ga anyi posting request din nata. Nan
da nan aka fara comment, masu fada
mata bakar magana nayi masu zagin ta
nayi, yayin da wasu kuma suka fara
yabawa da halittar gwarzon nata suna
nuna suma suna so. Babu wata
takamaiman amsa dai har bacci ya dauke
ta. Da safe tana yin Sallah kan wayarta ta
koma ko zata ga wani sabon comment, a
lokacin ne kuma ta gani daga wata da ta
kira kanta da kanwar sa "laaah, wannan ai
Hamma ne. Poster kina ruwa".
Babu bata lokaci ta shiga dm din yarinyar da daga baya ta fahimci sunan ta Mufida,
la gaya mata ita ce mai cigiyar wannan
bawan Allahn, tana so ta taimaka mata ta
hada ta dashi. A take Mufida ta gaya mata
ba zal yiwu ba, yana da budurwar da yake
so sosai kuma bayan ita baya kula kowa.
Amma duk da haka bata kyale ta ba, ta
ringa yi mata naci. Kira, message, kira,
roko Allah da Annabi. Daga baya dai ta
bata number din sa tace ta gwada sa'ar
ta. Number din dai data dauka a wajen
Safiyya ce, amma bata gaya wa Mufida
yayi blocking already ba, sai ta sayi wani
sim din musamman ta sake kiran sa da
shi. Wannan karon ko dauka bai yi ba, ta
tura masa message, da aka kwana biyu ta
sake kira sai taji shima yayi blocking. Still
bata hakura ba, ta koma ta ringa bin
followers din Mufida tana nemansa har sai
da gano shi.

"Muhammad Gidado" ta karan ta sunan
shi a fili tana jin sunan ya zauna a dukkan
gurbin zuciyar ta, Sai dai account dinsa
private ne, ta tura masa friend request,
request din da har yau bai amsa ba,
Ta yaya? Ta yaya zai so Safiyya ita kuma
ya ki ta? Me yasa? A zuciyar ta sai take
ganin dan dai kawai bai bata chance bane
ba. Shi namiji ne fa ita macece, kuma ba, Shi namiji ne fa ita macece, kuma
macen da take da komai

96 / 113