SAFIYYA BOOK COMPLETE MAMAN MAMA.txt

Author :  Maman Mama Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   92 / 113

273K to 276K   out of 336.6K words

na gyada mata kai
amma ban kara komal akan hakan ba

Bayan mun gana mun jera komai a dining sai na koma sama zan shirya ita kuma ta fara hidimar gyaran gida, sanda na kuma saukowa duk mutanen gidan sun tashi,
muka wuce dakin Daddy na fara gaishe
shi tare da kissing cheeks dinsa sannan
na bi su twins duk nayi kissing dinsu na
koma kan Mommy ita ma nayi mata kuma
na rungume ta, ta janye ni tana kallon
fuska ta da alamar tambaya amma sai na
share. A lokacin ma sai da na kara yi wa
Daddy maganar Mustapha, twins suka
taya ni rokon sa and he said he will
consider it. "Zai dawo, amma ba yanxu
ba. Akwai abinda nake jira", Mommy tana
kallon mu bata ce komai ba.

Ranar haka na wuni da murmushi a fuska ta Muhammad a makale da ni a waya yana ta yi min nacin yana son gani na amma na gaya masa babu dama, tunda na gaya wa Daddy cewa na rabu da shi bana son yin wani abu ko yaya ne da zai nuna wa Daddyn cewa karya nake yi. Kuma a wani bangaren na zuciya ta har yanzu ina tunanin kallon don Muhammad after maganganun da muka yi ranar nan. Da yamma sai ga Uncle Ahmad, ya shigo ciki muka gaisa sannan ya shiga gurin Daddy suka jima suna magana sannan ya fito shima da murmushi a fuskar sa, "God is really amazing" ya fada a lokacin da yake yi mana sallama. Muka bishi da ido ni da Mommy har ya fita sannan Mommy ta tabe baki "ba dai za'a taba chanjawa tuwo
suna ba, komai gyaran da za'a yi masa kuwa".

Ranar na zo kwanciya bacci sai ga
message from one of my guards
"Mukhtar was seen lurking around this
area. Be careful". Na alive wavar tare da
yin ajiyar zuciya. Mukhtar bashi da hankali
tabbas, yana kuma son ya kure nawa
hankalin. Sun riga sun san abinda zasu yi
in suka kama shi, dan haka ban sake
maimaita musu ba.

Haka kwanaki suka yi ta wucewa, babu
wanda aka cewa komai a cikin mu daga ni
har Muhammad, shi na fahimci hankalin
sa a kwace yake amma ni sam nawa ba'a kwace yake ba except idan muna waya da Muhammad. Gani nake ba Muhammad ne Daddy ya zabar min ba, gani nake yi Muhammad is too good to be true with me dan ni na saba da bad news, bad news na sani tun kafin haihuwa ta dashi na saba dan haka good news din sounds weird to me.

Kwanaki biyar bayan zuwan Abba sai ga
Uncle Sufyan yazo gidan mu, nayi murnar
ganin sa sosai na gaishe shi sai kuma nayi
ta kalion bayan sa ko zan ga Aunty Hajjo
ta shigo, sau yace min "ba tare muka z0
ba aj" sai naji kunya ina fatan ba wai yana
nufin Junior nake nema ba, ni kuma har
ga Allah Aunty Hajjo nake nema,
maimakon ita sai Abdul naga ya shigo da
leda a hannun sa, na gaishe shi shima sai
gaishe da Mommy tare da miko min ledar
hannunsa sa "tsaraba" yace yana
murmushi, na karba nayi masa godiya sai
suka wuce gurin Daddy.

Na bude ledar, kayan ciye ciye ne kawai iri
iri, exotic biscuits and chocolates. Na
mika wa Mommy "gashi Abdul ya kawo
min" ta tabe baki "ni kika ga ya bawa?"
Sal naji babu dadi, na cigaba da tsaiwa da
ledar a hannu na sai tace "abinda vasa
aka kala wa Mustapha wani sharrin kenan
aka kore shi, Abdul ake so a dawo da shi.
Kuma na san wanna duk hadin Ahmad ne, Dan dan sa dan akuya ne ya san ba za'a mayar masa da ke ba shine ya kwaso Abdul. Ai shikenan". Na juya ban ce mata komai ba na koma sama, bana son obsession din Mommy akan hada aure tsakani na da Mustapha,
wannan obsession din shi ya rufe mata
ido gabakidaya. Ya kamata ace ta gane
bana so ne kawai kuma hakan baya nufin
bana son ta ko yayan ta, baya nufin kuma
zan daina kula da su. Auren Mustapha ne
bana so and there is no amount of nagging da zata yi da zai saka in chanja.

Amma kuma bayan na koma daki na bude one of the biscuits ina ci sai wani tunani ya fado min, what if Abinda Mommy ta fada akwai gaskiya a ciki? What if Abdul Daddy ya zaba not Muhammad? Na fito
da biscuits din bakina da sauri na zubar a waste bin sannan naje toilet na wanke bakina ina kallon kaina ta mirror, "Ya Rabbi" na fada a hankali. Tun daga nan
kuma sai hankali na ya tashi,

A gidan suka karasa wunin ranar, har sai da suka ci abincin dare sannan suka tafi. Banji dadin yadda na hadewa Abdul rai ba duk kokarin da yayi na ganin munyi hira sanda na sauka gurin Daddy, na ga kuma
shima bai ji dadin hakan ba a fuskarsa amma kuma I couldn't help it. Ya zanyi idan maganar Mommy ta kasance. Ranar sai da nayi kuka kafin inyi bacci amma
ban yarda na nuna wa Gidado ba duk
kuwa da yaso ya fahimci ina cikin damuwa, Washegari Friday sai ga Uncle Ahmad da sassafe muna breakfast ya shigo da kansa yana tambaya ko akwai
abinda ake bukata na cefane a gidan, yace za'a yi baki ne in an jima bayan sallar juma'a. Mommy ta tambaya su nawa ne vace bai sani ba kawai dai ayi abinci da
yawa kuma na fita kunya. Bata ce masa komai ba amma da aka jima sai gasu sun dawo shi da yaya da ledoji cie da kaji da vegetables ta fruits. Sai kuma kwalayen lemuka na alfarma.

Mommy ta tashi ta shiga gurin Daddy sai
kuma ta fito ranta a bace ta hau sama.
Hakan ya sa na fahimci ba zata yi girkin
ba, dan haka na cire hijab dina muka
shiga kitchen nibda Esther muka kama
aiki, muna cikin aikin Hussain ya shigo
shima na tisa keyarsa zuwa kitchen din na
bashi aiki, Hassan ya shigo shima na jawo
shi, tun suna bata rai har suka saki jiki
muka yi ta aikin muna hira Hassan har da
kunna kida yana rawa. Sai da muka ci
karfin aikin sannan muka sallame su dan
kar su makara masallaci mu kuma muka karasa

Abinci kam munyi shi, friend rice da taji
Kayan hadi da kuma hanta, sai mandi rice
Ita kuma de aka hada ta da gasashshen
naman ragon da yayi laushi sosai, sai
kuma muka yi brown superghetti da kuma
cheese macaroni, sai tuson shinkafa
miyar zogale sannan sakwara da miyar
agushi, Sa peppered chicken da salad,
Sannan fruits. Mun yi aiki kam mun gaji
sosa), dan ma kowanne variety ba wai da
yawa muka yi sosai ba amma munsan zai
isa tunda abubuwan da yawa, Muka gama
juye komal a warmers, muka ware na
abincin gida muka Esther ta kai dining ta
jera ni kuma na fara kokarin hawa sama
sai gata ta dewo tana cewa wai ai bamu
gama ba tunda bamu yi farfesu ba,
*Abinci baya zama complete sai an hada
da pepper soup" na harare ta, ssi kiyi tayi,
ni dai ba inji bace ba kuma na gaji, ke kika
ce ba kya so a kawo miki mai taya ki aik™️"
La dega kafada "indai farfesu ne yanzu
kuwe zanyi, akan sa za'a hada ni da wata? Ai kuwa gwara in kwana ina yin farfesu, kala biyu zanyi ma ko uku. Haka kawai?” ta koma kitchen tana mita ni kuma na girgiza kai kawai na koma daki.

Dana shiga sai na tsiri aikin gyara kayana ina kokarin Cire zuciya ta daga tunanin bakin Daddy, su Waye? Me kuma ya bata ran Mommy haka? Sam bana jin dadin bacin ranta. Sai na fita na tafi dakin ta na tarar da ita a falon ta na sama a zaune tana waya, “wallahi sakina na gaji da halin mutumin nan. Allah hakurin da nakeyi ba kowacce mace zata iya irin sa ba. Sam Sam baya ganin daraja ta da kima ta, dani da babu duk daya. Kawai daga tambayar su Waye bakin da zasu zo sai ya fara neman gayamin magana……” sai na juya na koma ba tare de na karasa shige ba,

Ina komawa dakin sai kawal na cigaba da
gyaran kayan da na fara, amma still zuciya
ta tayi min nauyl, ban gama ba kuma sai
na barshi na shiga toilet nayi wanka na
fito ina tunanin kiran Muhammad ko naji
muryarsa inji dadi amma kuma sal na
tahimel lokacin masallaci ne, dan haka sai
na barshi na shiga closet dina na dauki abaya mai dogon wando na saka ba tare da na yi wata kwalliya ba except for mai da turare, lokacin na san an gama fitowa daga masallaci, Amma still ban kira Muhammad ba sai na tayar da sallah, sai dai banjima da tayar wa ba naji alamun motoci suna shigowa gidan mu, nayi kokarin yin sallah ta a nutse sannan nayi addu'a na shafa sai kuma na mike na daga labulen
tsegumi na na leka waje. Bakin motoci na
gani guda uku, Ban san ko daya daga ciki
ba. Sai motar uncle Ahmad da ta uncle
Sufyan. Na ci gaba da kalion motocin ina
jin faduwar gaba a karshe ma kawai sai na
koma na zauna a bakin gado ina kallon
hoton Ammie rungume da ni. A hankali
nace "Hey Ammie".

Wayata naji tayi kara alamar shigowar
sako, na dauka da sauri ina tunanin ko
Muhammad ne amma sai naga alert ne
daga banki na, personal account dina,
bana expecting wani kudi da zai shiga ciki
dan haka na bude, na tsaya ina kallon
kudin, sannan na kalli sunan wanda ya
turo min kudin "Abbakar Sadiq Abdallah"
ban taba jin sunan ba tun da nake, sai
kuma na kalli caption din "sadaki".

Gaba na yayi wata irin faduwar da sai da
na zamo daga kan gadon na zauna a
kasa, Abbakar Sadiq Abdallah? Waye
wanna kuma ni Safiyya? Na shiga uku.
Kar dal ace Daddy aure na ya daura da
wanna mutumin da ban ma taba jin sunan sa ba.

Karar waya ta ce ta dawo da ni hankali na,
na dan zabura kadan saboda tsoratani da
karar tayi, tun kafin in dauka na san
Muhammad ne, wayyo Muhammad,
innalillahi wa inna ilaihir rajiun. Amma
kuma sai nayi tunanin bara in dauki kiran
nasa inji yana ina, watakila zan samu wani
bayani daga gare shi.

Na dauka na saka a kunne na ban ce
komai ba sai naji muryarsa fes a kunne na,
kamar ma a hanya yake "hey sweetling.
Kin ganni yau a kafa na tafi masjid saboda
in samu lada" na dan dake nace "kana ina
yanzu?" Yace "ina hanyar komawa gida,
are you okay? You sound not okay" sai
kawai na katse kiran tare da ajiye wayar a
gefe na. Ina jin shi yana cigaba da kira na
amma ban dauka ba. Waye wannan
Abbakar Sadiq din? Menene dalilin Daddy
na hada ni da shi? Da gaske an daura min
aure da shi?

Na cigaba da zama a gurin kamar gunki
har adadin mintuna ko awannin da ban
sani ba, Sal kuma naji anyi knocking kotar
dakina, automatically nace "shigo" ba
tare da nayi tunanin waye ba, kamshin
turaren da naji ya saka na juva, Uncle Ahmad ne, ya ci kwalliyar sa cikin manyan kayan da daga gani sabon dinki yayi ga hular sa ya saka da tayi matching da
kayan sa, fuskarsa kamar gonar auduga,
kallo daya nayi masa na dauke kai, kowa
ma haushi yake bani.

Ya shigo sosai ya zauna akan kujerar da
take dakin tana kallon gadona shima yana
kallona yace "Safiyya" na daga kai na
kalle shi na mayar da kaina kasa, yace
"kinga sako kenan?" Na gyada masa kai
kawai, sai ya sake yin murmushi yace
"yaya ya gaya min cewa kin bashi wuka
da nama, kince kin amine ya zaba miki
koma wanene yake gain shi ya dace da
ke. Ya kuma zaba din, nima kuma na
aminta da zabin na sa bayan yayi min
bayanan dalilin yin zaben. Na shigo ne
yanzu in gaya miki an daura miki aure
yanzun nan" yayi shiru muna jin alamar
fitar motoci daga harabar gidan. Yace
"Allah ya sanya alkhairi ya yi miki albarka"
sai ya mike tsaye, nayi sauri nace "uncle
waye...….???" Sai kuma na kasa karasa
tambayar, ya karasa min "waye angon?
Kar ki damu, zai zo in an jima da daddare
sal ku ga juna, Ina so ki saka a ranki cewa
duk duniya babu wanda yake son ki sama
da Adam kuma ba zai taba zaba miki
abinda zai cutar da ke ba" ya kai bakin kofa na sake tambayar sa "uncle an gaya wa Mommy?" Ya daga kafada "mijin ta ne ya yanke wannan hukuncin, shine kuma zai gaya mata da bakin sa. Ni ba za'a ji
mutuwar sarki a baki na ba". Na bishi da kallo ina kokarin digesting maganar sa. Kiran da ya shigo wayata ya katse min tunanin na dauko wayar ina kallon sunan Muhammad ”pyar💕” sai kawai na katse kiran tare da kashe wayar gabakidaya na ajiye ta sannan na tashi na gabatar da sallar la'asar din da ake tayi a
masallaci, ni dai ba zan iya cewa ga abinda nake ji zuciya ta ba dan wani irin zafi da zugi take yi min.

Da na idar da sallar ma sai na kasa yin
addu'a mai tsaho kamar yadda na kasa
yin kuka, kawai na zame na kwanta a kan
sallayar na lukluba da hijab din jikina ina
jin sanyi yana ratsa kasusuwa na. Anan na
cigaba da kwanciya har aka yi sallar
magrib, babu wanda ya leko gurina nima
kuma babu wanda na nema, naji ina
missing Ammie sosa da sosai, wai aure
aka daura min yau.

-Na tashi duk da sanyin da nake ji na je
nay alwala na dawo nayi sallar magrib
sannan na cigaba da zama akan sallayar
ina ta kiran sunayen ubangiji da niyyar ya kawo min dauki ko ya kawo min sassauci a zuciya ta. Ina nan zaune naji an sake turo kofar an shigo tare da sallama, na juya da sauri jin muryar da nayi kamar
daga sama, Muryar Aunty Hajjo, na bita
da kallo har ta karaso cikin dakin ta kunna
fitila tana kallona da murmushi a fuskar ta
"amarya" na sunkuyar da kaina ina fatan
hawaye zasu zo ido na ko zan samu sanyi
a zuciya ta, na kasa ko da gaishe ta ne, ta
zo gaba na tare da kamo hannuna ta rike
a cikin nata tace "k gaishe ni ba zaki yi
ba? Ke fa kika ce kin ba da zab'" ta fada
cikin tsokana, na bude bakina da niyyar
gaishe ta amma muryar taki fitowa sai na
mayar da kaina kasa, tace "ki tashi ki
shirya ga angwayen can sun zo zapsu
ganki" na sake dago ido da sauri na kalle
ta sake yi min murmushi sai nayi sauri na
girgiza kaina "ni ba zan je ba. Ni bana son
zuwa. Ni ban san shi ba. Ni bana son shi"
sai na ga ita dariya ma abin ya bata. "Ya
akayi kika san ba kya son sa bayan ko
ganin sa baki yi ba?" Ni dai ban ce mata
komai ba amma na san ko waye shi ba
zan so shi ba dan babu wani space a
zuciya ta da Muhammad bai cika ba.

Ta matsa wai lallai sal na tashi na shirya na chanja kaya, na tubure mata taga ina neman inyi mata dan karamin hauka sai ta rabu da ni tun da ta lura kayan jikina ba wai sunyi muni bane ba, amma sai ta
kwaso turare tayi ta fesa min har sai da
naji yayi min yawa a kaina, sai kuma ta
nemi mayafi mai dan girma ta lullube ni da
shi ta kama hannu na muka fita. Muna fita
daga dakina na juya ina kallon hanyar
shiga part din Mommy, a hankali nace da
aunty Hajjo "Mommy fa?" Ta kalli kofar
tace "tana gurin Daddyn ki" daga haka ta
ja hannuna muka sauka kasa. Ni dai ina
kankame da hannunta jikina sai rawa yake
yi kaina a kasa har muka sauka, naji alamar akwai mutane kuma maza a falon saboda maganganun da suke yi kasa kasa amma muna gama saukowa suka yi shiru, ban daga kai na kalle su ba sai ma sake
shigewa jikin Aunty Hajjo na yi wadda ita
naga kamar ma abin dariya yake bata, da
kyar ta jawo ni daga bayanta ta tsayar
dani a gabanta sannan a hankali kamar
mai rada tace min "ta yaya zaki ga angon
naki idan baki daga idon ki ba?",

A hankali na daga idon na nawa, zasu kai
su shida ko bakwai a falon duk da ban
tsaya kirga su ba. Na fara kallon su daya
bayan daya, duk da murmushi akan
fuskokin su, a fuska ta biyu naga Haidar,
yana kallona da murmushi a fuskar sa, najl
zuciya ta ta buga da karfi, a take na bude
luska ta sosal a fara baza idon neman sa, and then I saw him, smiling brightly from ear to ear, hasken hakoransa yayi matching da hasken fararen kayan jikinsa wadanda suke kyalli da sheki kamar
yadda fatar jikinsa take yi. Sai na ga
kamar gabakidayan sa ya zama tamkar
farin wata dan daren goma sha biyar. Ya
mike tsaye idanunsa suna kyalli, reflecting
the love he has for me, sannan a hankali
ya bude min hannayensa.

Na saki hannun aunty Hajjo, ba tare da na
jira komai ba, ba kuma tare da na damu
da tarin mutanen da suke gurin ba, na
wuce straight zuwa kirjinsa sannan ya
mayar da hannayen ya rufe ni a ciki. A
take na saki kukan da nake ta fatan zuwan
sa tun lokacin da aka daura auren.

Ina jin yadda gabakidaya falon ya rude da
hayaniyar da take nuna murna.
Maganganu suke yi hade da dariya
gabakidayan su a lokaci daya amma bana
jin abinda suke fada, bana jin komai sai
sound guda biyu a lokaci daya, daya na
bugun zuciyar shi da nake jin ta kamar a
cikin kunnena take bugawa, dayan kuma
na murmushi mai sauti da yake fitarwa
wanda nake jin sa tamkar a cikin
kwakwalwa ta yake yinsa, sai naji wannan mix na sautuka tamkar shi ya fi kowanne sauti dadin sauraro.

Ya kara matse ni a jikinsa da hannu daya,
sannan ya saka daya hannun a hankali
yana bubbuga baya na dashi alamar
rarrashi, sannan a cikin kunne na yace "it
is okay. Ya isa haka. Muhammad Gidado is
here. You are okay kinji?"

Na daga kai a hankali na kalli fuskar sa
kamar mai tabbatar wa da cewa shi din ne
ba wani ne ba, ya sunkuyo da kansa
shima muka kalli jina cikin ido sai kuma
nayi saurin mayar da tawa fuskar kasa ina
jin kamar numfashi na zai dauke, we have
never been this close, I have never been
this close to any man.

Aunty Hajjo ce tayi gyaran murya, sai naji
kunya ta kama ni kamar zan nutse a kasa,
da sauri na kara jawo mayafin jikina na
kara rufe fuska ta dashi, tace "wanne rufe
fuska kuma zaki yi? Ni da kika manta da ni
ma? Babu komai ai yau na san matsayi
na" mutanen gurin suka yi dariya, nima
nayi tare da kara sunne fuskata a kirjin
Muhammad, tace "babu komai mu hakan
da ma muke fata, Sako ne dama na zo isar muku da shi inji parents din ku. You are a reward to each other for being good kids. Fatan su kawai tare da mu gabaki daya shine ku cigaba da zama yaran kirki. Allah
kuma yayi muku albarka".

Gabakidaya

92 / 113