Author : Maman Mama Category : Romantic Hausa Novels
sai kuma yayi sauri ya kalli side din da aka rike hannun nasa.
Yarinya ya gani yar karama wadda ba zata fi sa'ar Mufida ba. Ta karkata kai side daya tana kallon sa fuskarta dauke da murmushi. Yayi sauri ya saki hannun ta yana yarfar da nasa hannun "You? Who are you? Where are your parents?" Ya karasa maganar yana duddubawa around them. Sai dai bai ga kowa da yayi kama da iyayen ta ba, kusan ma inda suke zaunen basu da yawa.
Ya sake dawo da dubansa kanta yace "where are your parents?" Direct tace "my mother is dead. My father is in Manchester yana jirana" ya koma ya zauna sosai "are you telling me ke kadai aka sako a jirgin nan daga wata kasar zuwa wata?" Ta daga kafada tace "there is nothing to it really. Uncle Ahmad ya kawo ni airport ya danka ni a hannun cabin crew, they will take care of me har mu sauka and my Dad will be waiting" ya tsaya kawai yana kallon yadda take zarar magana yace "awwn, rich kids, yayan Daddy da Mommy. Now if you don't mind i need to sleep. Ki koma wherever it is that you came from. I don't want any trouble".
Ta gyara zama. "i won't trouble you. I prefer sitting here" ya bata rai irin yadda yake yiwa Mufida "ke! Bar gurin nan nace miki" amma maimakon tabi umarnin sa kamar yadda Mufida take yi sai ta kyalkyale da dariya tare da kwaikwayon yadda yayi maganar "ke! Bar gurin nan nace miki" ta sake wata dariyar sannan tace "fillo". Yaji wani takaici ya kama shi kamar ya rufe ta da duka, amma maimakon haka sai ya mike tare da ɗaukan headphone dinsa da niyar bar mata gurin.
Sai dai yana mikewa jirgin su ya shiga turbulence. Ya koma ya zauna da sauri tare da mayar da seatbelt dinsa, sai da suka fita daga turbulence din sannan ya lura cewa ya kuma rike hannun ta da hannayensa biyu. Ya sake cika ta yana gyara zamansa. Tace "you have aerophobia you cannot help it. There is nothing to be ashamed of"
Ya bata rai a ransa yana tunanin wannan wacce irin yarinya Allah ya hada shi da ita yau. Yace "wai ke parents din ki basu warning dinki not to talk to strangers ba?" Ta gyada kai da sauri tace "Mommy did" yace "you just told me mamanki ta rasu" tace "yes, Mommy is my step mom. But she is more like a mother to me because she loves me so much" yace "ohh, shi yasa ba kya jin maganar ta kenan ko?" Ta yi shiru tana kallon sa da alamr bata gane me yake cewa ba.
Yace "she told you kar kiyi magana da strangers, amma gashi kina yi min magana ni" ta girgiza kai "saboda you won't harm me" ya bata rai "ya akayi kika san hakan? You don't know me" ta daga kafada tace "I don't know how I know, i just know" yadda tayi maganar yasa yayi murmushi, sannan yace "you are too smart for your own good, zaki iya cigaba da zama anan, amma kar ki dame ni da surutu" ta yarda da hakan, amma kuma bata cika alkawarin ba dan for the hours da suka dauka suna tafiya sam bata barshi ya runtsa ba, labarai dai kam ya sha su, duk yan gidan su babu sunan wanda bai ji ba, Mommy, Daddy, yaya Mustapha, Hassan, Hussain, Safina har zuwa kan yan aikin gidan su.
And he held unto her hands sanda jirgin su zai sauka. Sai bayan sunyi landing sannan yace mata "kim fada min sunan kowa a gidan ku amma baki fada min naki ba" tace "Safiyya. Sunana Safiyya Adam Muhammad. Amma yan gidan mu suna ce min Fiyya. I don't know why"
"Piya?" Ya maimaita
Tayi dariya "Fiyya. With an F and double y"
"Piya" ya sake maimaita wa
Tayi ajjiyar zuciya "fillo" ya bata rai, tayi dariya.
"In kace Piya kana nufin something totally different from my name" ya bata rai yace "me Piya din yake nufi?"
Tace "love ko beloved, in India" ya gyada kai yace "ohh"
Tace "and ina da wata super power, I can tell you your name. You are Muhammad Auwal Muhammad" yayi sauri ya kalleta da mamaki, sai ta daga masa flight ticket dinsa da ya fadi kasa bai sani ba. Tace "har ka ji tsoro, da wata farar fuskar ka anan".
****. ****. ****. **** ****. ****
Ina yan kasuwar mu wadanda suke son samun more visibility for their kasuwanci? ina masu neman followers a social media pages din su? To ga dama ta samu. Ku sani cewa mai talla shi ke da riba. Come and advertise with me and I assure you that you will get value for your money. No matter how big your business is, dole kina bukatar advertisement dan samun cigaba a kasuwancin ki. Kar ki manta, hatta manyan companies irin su CocaCola, Apple, Dangote etc kullum suna cikin tallan hajar su so why not you….
Duk wanda yayi sponsoring episode zan yi masa tallan business dinsa in the episode which will be posted on whatsap, facebook, intagram and wattpad, zan kuma saka number dinsa da kuma links na social media accounts din business din sa, zanyi posting pictures and links din on my whatsaap, facebook and intagram stories for 24h. Kar ku manta, the advert on the pages will last for as long as social media exist, that means forever. I will come up with a method da zan tabbatar you get value for your money, in sha Allah.
For sponsorship,
contact 0704 203 0419 on whatsap
or
send a dm to my Instagram page
https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ==
Save my business number
0704 203 0419
and say hi on whatsap dan inyi saving naku.
Please, dan Allah, abeg, ban da kira
[07/01, 10:41 pm] +234 906 816 1960: ❤🩹*Safiyya*❤🩹
*By*
*Maman Maama*
Daga marubuciyar:
Maimoon
A'isha Humaira
Diyam
Tagwaye
Jidda
And now..... Safiyya
*Episode Two: The Choices*
For sponsorship,
contact 0704 203 0419 on whatsap
or
send a dm to my Instagram page
https://www.instagram.com/maman.mamas.words?igsh=MW5yaXFqOHhubnIwaQ==
Save my business number
0704 203 0419
and say hi on whatsap dan inyi saving naku.
Please, dan Allah, abeg, ban da kira
*Her🧕🏻*
Har dare yayi na kwanta bacci babu wanda ya kara shigowa gurina babu kuma wanda ya neme ni sai Mommy da ta shigo ta matsa min naci abinci sannan nasha prenatal vitamins dina. Tun da na tashi da assuba kuwa nayi wankana na shirya na saka jilbab ɗin da nake fatan zai rage nuna wa mutane cikin da yake jikina. Dama kayana a hade suke ban fito da su daga jaka ba, duk abinda na fito da shi kuma nayi deciding cewa ba zan tafi dashi ba dan bani da karfi na jiki dana zuciya da zan iya yin wani abu akai.
Na koma na kwanta a kan gado na nannade jikina da jilbab ɗin, na rufe idona da fatan bacci zai dauke ni ko na samu na ɗan rage ciwon da kaina yake yi min, amma sai dai a maimakon bacci, memories ne suka yi ta overlapping a cikin kaina, memories of yarintata, memories of relationships dina da family dina a da da kuma a yanzu, memories din Gidado and all the hopes we had for a future together, and the memories of daren da ya lalata komai a rayuwa ta, daren last birthday din Gidado.
Na tashi zaune tare da dafe kaina da hannayena ina jin yana barazanar tarwatsewa. Sai kuma na daga kaina sama ina kallon hoton da yake facing ɗin gadona, hoton mahaifiyata a kwance akan gadon asibiti rike da yar jaririya a hannunta, fuskarta cike da tsantsar farin ciki. Nayi ajjiyar zuciya, ina ma dai rayuwa tana da control button, ina ma dai zan iya rewinding komai na koma yar jaririya na cigaba da jin dumin mahaifiyata, inama.......
Sai nace a fili kamar mai magana da ta cikin hoton. "you set me up to be devoured by the blood thirsty vultures, yanzu gashi sun kassara rayuwata" nayi tsaki na juyawa hoton baya, sai kuma na sake juyawa nace "I miss you though".
Knocking din da naji a bakin kofa ya saka na dawo da dubana kan kofar sannan na kalli agogo, 7:35. "Yes?" Nace ina gyara hijab dina tare da sake haɗe fuska. Sai dai kuma ana bude kofar yanayin fuska ta ya juya zuwa murmushi. At last, someone I can talk to, someone who truly loves me.
Suka shigo a tare suma fuskokin su dauke da murmushi, na bude musu hannayena amma maimakon su fada jikina kamar kullum sai suka zauna a sides dina sannan suka rungume ni a tare. Nayi ajjiyar zuciya ina kara rungumar su jikina, ina jin yadda suka kara girma duk su biyun, a tsaho yanzu duk sun kere ni.
"Yan biyun yaya Fiyya, I am glad you made it. Ina ta jin babu dadi na dauka ba zan ganku ba har mu tafi".
Hassan ya dago kansa daga kafada ta yace "kinga gudun da muka yi a mota kuwa? Mommy tace mu hakura mu zauna tunda jiya ma evening paper mukayi amma muka dage sai da muka zo dan mu ganki kafin ki tafi"
Hussain yace "Mommy tace zaki jima baki dawo kasar nan ba, haka ne? Amma zamu iya zuwa mu kai miki ziyara in mun gama waec ko?".
Na gyada kai nace "duk sanda kuke son ganin mu kuyi min magana ko kuyi wa Daddy magana, za'a siya muku ticket ku tafi. And anything you need, ko menene, ku kira ni ku gaya min".
Suka gyada kai a tare, Hassan yace "but this is not fair, Daddy is not being fair to you. Me yasa zai miki aure yanzu? Mommy tace aure zai yi miki da yaya Mustapha. Yaya Mustapha fa for God's sake. It shouldn't be. Kamata yayi a barki kiyi healing, ki kuma samu wanda kike so ku fahimci juna sannan sai kiyi aure" na kalle shi ina murmushi nace "all that sounds so good. Amma kuma ba haka Daddy ya zaba ba, and I am sure Daddy ba zai zaba min abinda zai cutar da ni ba, da abinda ka fada ɗin shine zai fi min dai dai I am sure Daddy shi zai zaba min, you should be kinder to him".
Hussain yace "but what about you. You are obviously not happy" nace "it doesn't matter. Maybe I will be nan gaba. Hussain, a yanzu haka happiness dina kadan ne a cikin irin abinda zan iya sacrificing dan in gyara relationship dina da Daddy, zan iya bayar da komai, ko da kuwa rayuwata ce to have Daddy hug me and say 'I love you Safiyya'" na karasa maganar ina share hawaye da bayan hannuna".
Suka yi shiru gabaki daya sannan Hussain yace "he loves you, you know. Yafi son ki akan kowa" na yi yar karamar dariya mai kama da kuka nace "my dear brother, am not sure about that. To him, I am just a big fat disappointment".
Hassan yace "no you are not. He loves you. We all love you". Nayi kokarin chanja topic ta hanyar cewa "sooo, waye yayi driving a cikin ku, naji kunce kun sharara gudu" Hussain yana dariya yace "Hassan ne" Hassan yace "i passed my driving test last week, shine yanzu na gwada skill dina" nace "yayi kyau. Amma a daina gudu da yawa. An kawo muku motocin kenan?" Hassan yace "no... Ta wani friend din mu ne" na bata rai "why? Me yasa ba'a kawo muku ba? Kun sake yiwa Uncle Ahmad maganar?" Hussain yace "munyi masa fa, sai kawai ya rufe mu da fada wai me zamuyi da personal cars bayan akwai motoci a gida"
Na fara girgiza kaina ina cewa "nasan akwai motoci a gidan ai, ni nayi niyyar zan siya muku motoci a matsayin gift na jamb da kuka ci. Zanyi masa magana. Allah yasa zai zo yau yayi wa Daddy sallama, zanyi masa magana".
Hassan yace "uhm uhm, kar ki sa yayi miki faɗa kema. Yanzu kula da lafiyar ki yafi komai muhimmanci. Ki rabu da shi kawai". Na sake girgiza kai stubbornly "zan yi masa magana".
A haka muka cigaba da hirar mu har sai da Esther ta shigo da tray din breakfast ɗina ta kuma sanarwa su Hussain da cewa nasu abincin yana kasa sannan suka mike suka yi min sallama. Na tashi tsaye nima na rike hannayen su a cikin nawa nace "idan kunje gurin Daddy, be nice to him please, ku fada mishi maganganu masu daɗi and tell him you love him, hug him" suka tsaya kawai suna kallona amma kuma fuskokin su sun nuna cewa sun fahimci abinda nake cewa, a tare suka gyada kai, nayi musu murmushi sannan ta saki hannayen suka fita jiki a sanyaye.
Suna fita Mommy ta shigo ta kuma saka ni a gaba sai da na ci abinci, ina ci tana yi min hira. "Gwara ki ci abinci ki koshi dan ba lallai bane ki iya cin abincin jirgi. Kuma gwara ki ci abinci a daki dan ban san waye zai shigo gidan nan yau ba, ko ma'aikatan gidan ma ban yarda su san halin da kike ciki ba, dan hausawa sunce munafukin ka tabarmar ka".
Muna nan zaune Safina ta shigo ta zauna tana kallona ina shan tea din da Mommy ta hada min, tace "I will miss you little sister. Though na san ba dadewa zakiyi sosai ba. Kina dawowa kuma sai mu sha biki" ta karasa tana murmushi. Ban ce komai ba har sai da Safina ta mike zata fita sannan na daga kai nace mata "I will miss you too. Allah ya bada sa'ar karatu" tace "Ameen. Nagode" sannan ta fita.
Ban fita ba har sai da aka gama saka duk kayan mu a cikin mota, sannan Mommy tazo da kanta tace inje in shiga mota, shima sai data tabbatar jilbab din jikina ya boye cikin sannan ta kama hannuna muka fita tare.
Sai dai muna fita compound din gidan motar Uncle Ahmad tana shigowa, driver yana tukawa, Mukhtar a gaba, Uncle Ahmad a baya. Mommy ta tura ni gaba "sauri ki je ki shiga mota gani nan zuwa" amma sai na makale, ina so nayi magana da Uncle Ahmad akan maganar motocin twins. Mommy ta sake turani amma maimakon nayi hanyar motar da zamu tafi airport a cikin ta sai nayi hanyar inda su Uncle Ahmad sukayi packing.
Kafin na karasa suka fito, kallo daya Uncle Ahmad yayi min ya dauke kai, yayin da Mukhtar kuma ya taho direct gurinna yana washe baki. Sai a lokacin nayi nadamar kin jin maganar Mommy. Ya tare min hanya yayin da ni kuma nake kokarin wuce shi na tafi gurin Uncle Ahmad. Yace "Fiyya ko gaisuwa babu? Ko nayi wani laifin ne wai? Ni ina ta jin dadin zan samu na ganki ke kuma ko kallo ban ishe ki ba ko?"
Na tsaya tare da juyowa ina kallon sa. "Yaya Mukhtar, barka da zuwa, ya hanya. Nice to see you. Bye". Na juya zan tafi ya sake tarar gabana. "Dan Allah Safiyya ki tsaya. You don't have to be cold. Ki bani dama muyi magana ta fahimtar juna please. Minti biyu ya ishe ni" nayi ajjiyar zuciya ina lura da Mommy da ta bata rai a gefe tana kallon mu. Nace "ina jinka" ya gyara tsayuwa sa, na lura da yadda yake kokarin kar ya kalli cikina, yace "ina jin yau kusan shekaru biyu kenan da na fara gaya miki abinda yake zuciya ta. So kin riga kin sani. Ina so ne in gaya miki cewa babu abinda ya chanja a zuciyata a game dake duk da rejecting dina da kikayi the first time. Babu abinda ya chanja a zuciyata duk da wannan abin da kika yi" ya fada yana waving hannunsa around cikinta ba tare da ya kalli cikin ba, naji zuciyata ta tattare ta dawo wuyana, na nade hannuna a kirjina nace "what do you want, Mukhtar?" Ya dago kai yana kallon cikin idona, nima ban dauke nawa ba, yace "you know exactly what I want" nace "no, I don't. Just skip the whole preamble ka gaya min direct. Menene kake bukata daga gare ni".
Ya sauke idonsa kasa yana hadiye yawu yace "idan kin amince ..... A matsayi na na dan'uwanki na jini, ina so in kin haihu, zan taimaka miki in aure ki, har abada babu wanda zai san me ya faru. Har abada babu wanda zai san me kika yi" na kankance idona a kansa nace "Mukhtar, a tsakanin ni da kai tabbas akwai wanda yake bukatar taimako, kuma daga ni har kai mun san waye".
Na juya da sauri na bar inda yake, raina a matukar bace, blindly nake tafiya ina magana da kaina kasa kasa, ban ankara ba sai gani na nayi a gaban Uncle Ahmad, na dan ja baya sannan na gaishe shi a diririce "uhmm. Uncle. Ina kwana" yana danna wayarsa ya amsa. "Lafiya" har na wuce shi sai kuma na tuna da alkawarin da nayi wa twins dan haka na dawo da baya. "Uncle.....dama ina so zanyi maka magana ne ... Dazu munyi magana da twins akan cars din da nace a siya musu. Shine nace bara in tuna maka maybe ka manta ne".
Wani mugun kallo daya watso min ne ya saka a lokaci daya naji ina ma dai jiya da na kwanta bacci yau ban tashi da rai ba. Na ja da baya taku biyu cikin sauri dan a tunani na rufe ni zaiyi da duka amma instead sai yace cikin daga murya "Safiyya? Yanzu rashin kunyar taki har ta kai haka dama? Zamani har ya kai haka lalacewa? Ke sam baki ma damu da wannan abun kunyar da yake jikin ki kike yawo da shi ba har kina da karfin halin tsayawa a gaba na da abun kunya a jikin ki kina bani umarni?" Na juya da sauri na yi gurin motar mu ina jin kafafuwa na suna harhadewa a cikin juna, ina kuma jin idanuwan duk mutanen da suke gurin a kaina.
Kafin in kai mota hawaye sun jika fuskata, ta gefen idona na