SAFIYYA BOOK COMPLETE MAMAN MAMA.txt

Author :  Maman Mama Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   90 / 113

267K to 270K   out of 336.6K words

ya fara typing kuma sai ya
daina, sai kuma ya koma offline. Naji wani
takaici ya kara mamaye zuciya ta hawaye
ya kawo a ido na. Nan da nan na fara
kukan kuwa. Ni da me zanji ne wai. Sai
kawai na danna masa recording kukan
nawa nayi tayi kamar karamar yarinya na
tura masa,

Ina kalion sanda message din ya je masa,
ma ga kuma sanda yayi playing, he
started typing again sai kuma ya daina.
Naji kamar in jefar da wayar a kasa dan
takaici. Sal na ajiye ta a kan gado na koma
toilet na wanke fuskata sannan na zo zan wuce in fita daga dakin naga wayar tana blinking, da sauri na dawo da sure ta na bude hoping to see his name sai kuwa naga message daga gare shi.

"Na samu sabon ring tune"

Sai da na dan dora wayar a saman kirjina
cikin nuna jin dadi na tare da lumshe ido
sannan na bude na tura mass reply,

"Ka wujjjiga zuciyata Muhammad. Gabaki
daya na fita daga hayyacina a cikin wuni
daya"

"Let me see"

"See what?"

"The face. Data fita daga hayyacin na ta"

Sai na gyara hijab din jikina tare da danna
masa video call. Bai dauka ba sai yayi
rejecting.

"Can't answer..... Let me call you"

Na rike wayar ina jujjuya ta a hannu na,
wata zuciyar tana gaya min suna tare da
Safina ne shi yasa yaki daukan kira na.

Mintina kadan sai gashi ya kira ni video call

Na jingina wayar tawa a jikin frame din
gado sannan na kwanta ruf da ciki ian
kallon wayar sai na answer. Yana dakin sa
na gidan su a kan kujera, Kallo daya nayi
masa na fahimci shima ya wujijiga kamar
ni. Fatar idonsa tayi ja sannan sides din
don sun tashi kadan. And his lips looked
a bit dry.

Direct nace masa "ba kayi bacci ba jiya
ko" na lura studying dina yake yi shima
sai yace "nayi. For like 3 hours I think.
How are you?" Ban amsa ba nace "3
hours yayi kadan" ya daga kafada "ba laifi
na bane ai. Me laifin ai ta san laifin ta" na
kwabe fuska makar zan cigaba da kukan
"na sani ai. Amma ai na baka hakuri. Dan
Allah ni dai kar ka sake yin fushi da ni kaji?
Gwara kayi min bulala Allah" na karasa ina
jin hawaye yana kawo wa ido na.

Yayi wanj gajeren murmushi da ban gane
ma"anar sa ba kuma naji bana son sani, a
hankali kuma yace "look at you. Kamar da
gaske zaki daina din" nayi sauri cewa
"Allah Yaya Muhammad da gaske nake, na
daina bata maka rai kaji?" Na karashe
cikin lallami, ya danyi shiru fuskarsa tana
nuna har lokacin yana cikin bacin ral yace
"but why do you do it?" Ya tambaya, sai nima na tambaye shi dan in tabbatar da cewa abinda nake tunanin ya bata masa rai din shine da gaske ya bata masa din "me yasa a karshen maganar mu ta jiya na
gaya maka zan rabu da kai?" Ya girgiza kansa idonsa a kasa sai kuma ya dago tace "me yasa tun kafin mu zauna baki gaya min cewa zaki yi recording maganganun mu ba? We promised each other that zamu ke yin everything together a yanzu. You
should have told me dan in san abinda ake ciki, I felt...........used". Ya karasa still da bacin rai a fuskarsa.

Na gyada kai cikin fahimtar sa, amma sai
nace "I promise I will explain everything to
you. Amma yanzu dan Allah kayi hakuri
kaji? Yanzu lokacin sallah yayi and zan
sauka wajen Daddy idan nayi sallah. I will
call you in na dawo daki and I will explain
everything to you" ya gyada kai shina
yana waigawa bayansa kamar wani ne ya
shigo dakin, sai kuna ya juyo yace min
"okay zamuyi magana in an jima" daga
haka ya katse kiran

Na ajiye wayar tare da kife goshi na akan
ta na some seconds sai kuma na mike da
sari yadida naji kiran sallah yana kara tashi a massilatai na shiga toilet. Bayan na 'idar na gabatar da adduoi na sai na sauka kasa kamar yadda na saba na tafi part din Daddy, babu kowa a parlour sai motsin
Esther tana shirya dinner dining. Na wuce
zuwa kofar shiga part din Daddy, tun safe
ban ganshi ba, tun safe bai bari kowa ya
ganshi ba dan haka bani da tabbas din
cewa yanzun ma zan ganshi din. Kowa a
gidan bai san dalilin hakan da Daddy yayi
ba amma ni na sani, duk kowa yana cikin
damuwa amma ni duk nafi kowa damuwa
duk kuwa da cewa ina jin relief a wani
bangare na zuciya ta cewa na gaya masa
gaskiyar komai ba zai mutu da haushi na a
ransa ba amma kuma bani da tabbas din
hukuncin da zai dauka, Sai dai kowanne
hukunci ya dauka na tabbatar ba zai yi
hukuncin da zai zama cutarwa a gare ni
ba.

Na shiga parlour sa na tarar da Hussain a
zaune daga alama daga masallaci va
dawo, ya mike tsaye yana kallona cikin
girmamawa sai nace "ya bude?" Ya dan
gyada kai kadan "ya budewa Mommy da
zu, amma ban sani ba ko ya kuma rufewa"
nace "ba ka gwada shiga ba bayan ta
fito?" Ya girgiza kai yana dan murmushi
"Ke dai je ki gwada, toro nake ji kar ya
sauke fada a kaina" na harare shi nayi
hanyar corridor din da zai sada ka da
bedroom dinsa. Na karasa bakin kofar na taba ta ina addu'ar Allah yasa ya bude, amma kuma ina tsoron facing dinsa after knowing what he heard and what he saw. Na danyi knocking kadan sai kuma na
murda handle din na tura ta, naji ta bude
sal nayi sallama tare da kasa kunnena,
banji ya amsa ba, kuma dama yanzu ba'a
fiya jin amsa sallamarsa ba tunda muryarsa tayi kasa sosai, dan haka kawai sai na shiga.

Yana zaune akan kujerar sa, da wayarsa a
hannun sa, naji gabana ya fadi amma sai
na maze na nuna kamar damuwata gabaki
daya akan halin da yake ciki ce. "Daddy"
na karasa gurin sa da sauri. "Daddy ka hana mu ganin ka tun safe, duk mun damu" na durkusa a gabansa trying so hard not to look at screen din wayarsa. Ya
saka hannu ya kashe hasken screen din
sannan yayi ajjiyar zuciya tare da miko
min hannu, na rike hannun nasa da hannayena duk biyun tare da dora guiwowina a kasa nace "Daddy are you okay? Wani abun yana damunka?" Sal ya danyi min gajeren murmushi, "I am fine Safiyya. Zuciyata tayi min dadi sosai. Ina fatan ke ma watarana zaki ji dadin taki zuciyar" na kara rikon hannun sa nace "a
yanxu ma ina jin dadin zuciya ta Daddy. Knowing that you are happy kadai ya ishe ni farin cikj" a hankali yace "I have made a lot of mistakes Safiyya in raising you, Nayi kurakurai da dama. Addu'a ta kadai a
yanzu ita ce Allah ya kara ara min lokacin
da zan gyara su" na zauna sosai tare da
zame hannu na daga cikin nasa, kai na a
kasa nace "Daddy you did well, kayi iya
kacin kokarin ka. Allah ya saka maka da
alkhairi",.

Muka danyi shiru kadan amma ina jin a
jikina kallo na yake, sai kuma yace "kina
da wani abu da kike so inyi miki? To put a
smile on your gloomy face today? Tunda
bani da tabbas din gobe" na danyi murmushi sai kuma na dago kai nace "Daddy ka dawo da Mustapha gida, he should be with you too, Bashi da wani
gidan sai nan. Bashi da wani uban sai kai.
Ban san laifin da yayi maka ba amma kayi
hakuri". Ya sauke ajiyar zuciya yana kallon gefe
amma bai ce min komai ba, a hankali na
sake cewa "kaji Daddy na?" Ya dan kalle
ni kadan ya sake dauke kai yace "ina
twins? Suna ta nema na ko?" Na danyi
murmushi "Hassan yana parlour, wai
toro yake ji kar kayi masa fada idan ya
shigo* ya danyi murmushi mai sauti yace
Wit a min sh)" na tashi ina jin dadi a raina duk kuwa da naga Daddy bai amsa bukatar da na gabatar masa ba na leka nace "baban Daddy, Daddy yana
magana" ya bude ido sal kuma ya mike da
sauri yana magana a hankali yadda Daddy
ba zal jI ba "shi yasa nace ki shiga, yana
ganin ki zai sauko" nay dariya tare da
talle masa keya, ya shiga yana sosa keyar
na bishi a baya ina jin yana gayawa Daddy
*Daddy ka ga ta dake ni ko?", Daddy ya
mika masa hannu "zo nan babana" na
karasa nima ina dariya. Daga baya sai ga
Hussain ya shigo shima, sai kuma ga
Mommy ta shigo ganin babu wanda yaje
cin abinci, a karshe sai abincin aka hado
aka kawo mana nan muka zauna muka ci
a plate daya mu uku, Daddy yana kalion
mu yana murmushi amma kana ganinsa in
dai ka san shi kasan akwai abinda yake
ransa. Mommy ma haka, tana tayamu
hirar kadan kadan amma ita ma ranta duk
a dagule yake kuma nasan Mustapha take
missing. A lokacin ne kuma naji tana waya
da Safina, Safinan tana gaya mata cewa
a koma gidan mijinta, Ta ajiye wayar tare
da jan tsaki tana kara bata fuska tace da
Daddy "Safina ce. Wai an mayar da ita
gida dazu, an kuma bata wata yar aikin. Ina in maganar komawar tata baban yaron yazo da zu kuy" Daddy ya juya ya kalle ta kadan sal kuma ya dauke kansa al ce komal ba ya cigaba da sauraron musun da ake tafkawa tsakanin Hassan da Hussain akan yan wasan ball.

Duk hirar nan da akeyi Muhammad yana
raina, na sam ya kira waya ta yaji ban
dauka ba amma kuma bana son tashi
saboda ina jin dadin zama da Daddy
musamman idan naga yana wasa da
twins. A haka har mukayi sallar isha muka
cigaba da hirar mu, Mommy kam sai naga
ta kwanta akan kujerar da take dakin ta
rufe idon ta, naji babu dadi a raina, na san
Safina da Mustapha ne a ranta and I felt
bad for her amma sam ban ji regret akan
abinda nayi ba.

Sai da Dr Ma'aruf ya shigo sannan ya
sallame mu yace mu bar Daddy ya huta,
muka tashi muka fita muka bar su sai
Mommy da ta zauna ita ma. Direct dakina
na koma ina addu'ar Allah ya sa
Muhammad bai sake yin wani fushin ba.
Na je na dauki waya ta na kuwa ga missed
calls din sa kusan two hours ago. Har na
zauna na danna kiran sa sai kuma na tuna
da maganar Mommy cewa Safina ta koma
sai na kashe a raina ina gayawa kaina
yana can yana angoncewa. Yes, na
fahimci yaudarar sa tayi ta aure shi amma har yanzu ban manta da zancen cikin da tayi a gidan sa ba. Nayi kwafa na tashi na fara cire kayan jiki na. Sai gashi ya kira ashe wancan kiran nawa ya shiga. Na harari wayar ina gaya wa kaina cewa taimaka masa zanyi by not answering his call dan kar yashiga hakkin matar sa. Amma ni na san kishi ne.

Sai da na shiga nayi wanka na fito sannan
na sake ganin wani missed call din da
kuma message.

"Sarkin kishi"

Na murguda baki kamar yana kallo na
amma kuma ina jin kewar sa a raina ina so
muyi magana dan akwai a lot of unsaid
words a tsakanin mu.

Sai da na gama dukkan shirin kwanciya
bacci na sannan na hau gado nayi addu'a
na rufe ido, so nake inyi bacci da wuri dan
ina da abubuwan yi da yawa washegari
wadanda suka shafi aiki na kuma ina
bukatar clear head. Amma bacci yayi
kaura daga idanuwa, kawai lissafe lissafe
nake tayi,

Nasan Daddy yaga video din can, wanne hukunci zai yanke akai? Me Abba yazo yi gidan nan? Da gaske maganar Safina ce ta kawo shi ko kuma wata maganar daban? Me Muhammad da Safina suke yi yanzu? Nayi tsaki tare da juyi, "Ya Rabbi" na fada a hankali kamar zanyi kuka, Sai kuma na jawo wayata na kunna data ina lura da yadda lokaci ya tura, Messages
suka yi ta shigowa duk ban damu da su
ba sal da naga nasa sannan na bude.

*I called, ba kya kusa. Call me in kin
gama"

Ina gama karantawa na ganshi online.

"Me kike yi baki yi bacci ba?"

*Kar ka dame ni. Go back to your wife"

"Hmmmm"

*Fadi dai abinda yake ranka, kar maganar
ta kumbura maka ciki"

*Ban san me yasa kike nuna kishin ki akan
ta ba, even after I told you yadda abin ya
kasance"

"She is still your wife, And you got her
pregnant"

“Hmmmm"

“Kai ma hmmm”

"Me kike nufi da hmmm din ta ki?"

"Abinda kake nufi da taka hmmmm din shi
nake nufi da tawa hmmm din"

"To ai baki san me tawa hmmm din take
nufi ba"

"Me take nufi kuwa? In banda cewa maza
rigar kaya ne ku?"

"Lo!"

'"Dariya ma kake yi ko?"

"Okay to me kike so nayi? Can I call you
please?"

"Ni ba zanyi waya da mijin aure ba da
daddare. Saurayi na zan kira wanda bashi
da mata"

"Hmmmm"

"Kai ma hmmm"

"Please in kira ki?"

"This user is busy"

“Please minti biyu kawai, So nake kawal
inji muryar ki kince min goodnight baby"

Kaje ta gaya maka baby din, ta goya ka
da zani ma babu ruwa na”

Na tura masa ina jin raina yana kara baci,
ni yadda ya dauk maganar ba koma ba
shi yafi komai bata min rai. Ina ganin sa
yana typing na kashe data ta tare da jetar
da wayar gefe na a kan gadon na ja bargo
na lulube har kaina.

A wannan daren shima da kyar bacci ya
dauice ni. Washegari ina kan system tun
safe ina all dan ko breakfast ban saulia
kasa rayi ba sai dal Esther ta kano min,
ina sane da Muhammad kuma na san ya
kamata muyi magana in warware masa
abubuna amma na cigaba da share shi.
Har sal wajen azahar na kammala na tashi
tsaye nayi mika duk jiina yana ciNio, wai
dan mana samu tunda uncle Ahmad ya
kora bakin aikin sa yana dan dauke min
wasu nauye nauyen.

Sai da na shiga toilet nayi wanka na shirya
sannan na zauna na kunna wayata ina
murmushi, ko babu komai na san jilin sa
-ya gaya masa zuNa yanzu, ba dai shi mai
mata ba? Himmm

Ina kunnawa sai ma hau yan danne danne
na, a haka na shiga Instagram na fara
scrolling through feeds, a lokacin ne naga
wani post a wani blog da naga yaja
hankali na saboda tarin comments din da
akavi akan sa. Sai na samu kaina da
karantawa. Irin yan hide my ID din nan ne,
na karanta labarin tun daga farko har
karshe sannan na sake karantawa sai
kawai na samu kaina da dariya. Mamakin
Safina yana kara kamani.

Tun a karantawar farko na gane ita ce.
Wai tana neman shawara ne agun
malamar blog din da yan comment
section, wai step sister din ta tana neman
raba ta da mijinta. A labarin nata yadda ta
nuna shine a gurin dinner dinta ne muka
hadu da Muhammad, wai tun daga nan na
makale masa shi kuma ya juya mata baya,
babu irin wulakancin da baya yi mata
akaina. Tace a wayarta ma ya dauki
number ta kuma ya gaya mata baki da
baki cewa number ta ya dauka. Sannan
bayan ta samu ciki yace baya so saboda
yana ganin in suka haihu za'a hana shi
aure na, yace sai ta zubar taki shine ya
mare ta ya kuma ture ta da mota ta fadi
cikin ya zube kuma taji ciwuka.
Maganganu dal iri iri,

Ko comment section din ban shiga ba na
wuce na cigaba da abinda yake gaba na.
Mani da lokacin ta ballantana na bloggers Sal na fita ma na koma na Kira mijin nata sai bayan da ya dauka sannan a tuna ashe fushi nake yi dashi, duk kuwa da
cewa ban san abinda yayi wanda yasa
nake yin fushin ba. Da ya dauka kuma si
nayi shiru. Shima daga bangaren sa sai
yay shiru din muk cigaba da sauraron
numfashin juna. A raina nace zanga wanda zai fara sauko wa tsakanin ni da kai,

Shi din ne kuwa ya fara magana "wai ni ya
akayi wanna lamarin ya juye ne? The last
time I checked ni akayi wa laifi nake yin
fushi ana bani hakuri har da yi min kuka.
Yanzu kuma lokaci daya na samu kaina a
mai bada hakuri bayan ban san laifin da
nayi ba kuma ban gama hucewa daga
laifin da aka yi min ba" na murguda baki
*oho. Nima ban sani ba" na kuma yin
shiru, yayi ajjiyar zuciya "to shikenan. Kiyi
hakuri. Whatever it is. I am sorry,
shikenan?*

Nace "shikenan. Kai ma kayi hakuri. Na
san nayi ba dai dai ba amma ina saka ran
dan nayi maka bayani zaka gane insha
Allah* ya danyi shiru sannan yace *why
do jou do it? Why were you recording our conversation kuma meyasa baki gaya min zaki yi hakan ba before you do it”

Na danyi ajiyar zuciya nace "I wasn't
recording.... Yace "then someone was
listening. Maganganun ki na karshe sun
nuna min cewa ba dani kike magana ba,
da wani kike magana. Waye?" Nace
"Daddy" duk muka yi shiru, sai ya
maimaita "Daddy? How?" Sai na bashi
labarin cctvn da Daddy ya saka a ko'ina a
gidan sa da niyyar kamani tunda ya lura
kamar bani da gaskiya ina boye wani abu,
and how I used that to my advantage
wajen warwarewa Daddy duk abinda
nake ganin ya karata ya sani a game da
alakar mu.

Yayi shiru har na kai karshen bayanin
nawa sannan yace "and why didn't you
tell me before? Yadda zamu zauna mu
shirya komai tare?" Na ce "I wanted to do
that. Amma kuma idan na gaya maka your
reactions won't be real, I wanted to show
Daddy the truth and the depth of your
love for me, and I did. Kayi hakuri Baby. I
believe wanna maganganun da Daddy
yaji tsakanin mu su zasu kawo mana
karshen issue din mu with him. Insha
Allah ina ran zai fahimta"

Na danyi ajiyar zuciya nace "I wasn't
recording.... Yace "then someone was
listening. Maganganun ki na karshe sun
nuna min cewa ba dani kike magana ba,
da wani kike magana. Waye?" Nace
"Daddy" duk muka yi shiru, sai ya
maimaita "Daddy? How?" Sai na bashi
labarin cctvn da Daddy ya saka a ko'ina a
gidan sa da niyyar kamani tunda ya lura
kamar bani da gaskiya ina boye wani abu,
and how I used that to my advantage
wajen warwarewa Daddy duk abinda
nake ganin ya karata ya sani a game da
alakar mu.

Yayi shiru har na kai karshen bayanin
nawa sannan yace "and why didn't you
tell me before? Yadda zamu zauna mu
shirya komai tare?" Na ce "I wanted to do
that. Amma kuma idan na gaya maka your
reactions won't be real, I wanted to show
Daddy the truth and the depth of your
love for me, and I did. Kayi hakuri Baby. I
believe wanna maganganun da Daddy
yaji tsakanin mu su zasu kawo mana
karshen issue din mu with him. Insha
Allah ina ran zai fahimta"

Ya danyi shiru kadan kamar yana tunani akan maganar sannan yace "na fahimce ki, na kuma karbi uzurin ki, but please Piya let this be the last time da zaki boye
min magana. Please" a hankali nace
"insha Allah. Kayi hakuri. Wannan shine
bacin ranka akan wanna maganar na
karshe. Kaji?" "Hmmm" kawai yace, nace
"ka hakura?" Yayi ajiyar zuciya "ya zanyi?
Ya zanyi da ke Piya? Ba na iya fushi da ke
duk yadda naso inyi hakan kuwa. Yanzu
wannan fushin da nayi me ya faru da ni?
Ba gashi nan kuma ni nazo ina bada hakuri ba?" Nace "ai issue din da ka bada hakuri a kansa daban ne ba wannan bane ba. Wannan ai ni na bada hakuri akan sa
tunda

90 / 113