SAFIYYA BOOK COMPLETE MAMAN MAMA.txt

Author :  Maman Mama Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   105 / 113

312K to 315K   out of 336.6K words

da karfin da na kara
fahimtar yanzu yana da shi ya dake shi da
karfi da guiwar sa a tsakanin kafafuwan
sa.

Mukhtar ya sake shi sannan yayi baya
yana rike inda ya dake shi din, cikin zafin
nama Muhammad ya tashi ya kara masa
wani kyakyawan dukan a gurin again.
Mukhtar yayi kara ya fadi tare da hade
kafafuwan sa a waje daya cikin nuna
ciwon dukan da yaji, amma Muhammad
sai ya saka kafa ya sake bude kafafun ya
kuma take gurin da karfi da takalmin
kafarsa, Mukhtar ya saki karar azaba,
kamar an cire masa dukkan karfin jikin sa,
Muhammad ya sake duka, again and
again and again. Har tsalle yake yi sannan
ya taka gurin ya murje ya kuma takawa,
ban taba ganin ran Muhammad a bace irin
haka ba kuma bana fatan sake gani har
abada. Jinin da naga yana bin wandon
Mukhtar ne ya saka na fara kokarin rike
Muhammad amma yaki rikuwa, a dai dai
lokacin da aka fara kokarin bude kofar
dakin da muke ciki ne na ga ya bar shi, na
dauka da gaske barin na sa yayi, sai kawai
na ga yaje a kinkimo wata flower vase da
take kofar toilet dinsa, ya zo ya daga ta ya
sakar wa Mukhtar ita a tsakanin
kafafuwan sa,

Ta daki gurin sannan ta tarwatse. A dai-
dai lokacin da security din suka shigo
dakin da muke hannayen su rike da
bindigogi. Nayi sauri na rungume
Muhammad, ina jin yadda jikinsa yake
karkarwa, ina jin yadda zuciyar sa take
bugawa, ina jin yadda numfashin sa yake
fita sama sama. Chief security din ya kalli
Mukhtar da yake yashe a kasa yana fitar
da numfashi sama sama, ya saka kafa ya
shure shi dan ya tabbatar babu sauran
fada a tare da shi sannan Chief security
din ya tambaye ni "are you okay?" na
gyada masa kai kawai. Su biyu suka kama
hannayen Mukhtar suka ja shi a kasa suka
fita da shi. Na bishi da kallo, remembering
everything that happened, and I thought
"What a glorious God I have".

Ni na tabbatar ta Mukhtar ta kare, abin
nan dai ba zai kuma amfani da shi ba har
abada, ba a kaina ba, ba'a kan kowa ba.
Na kuma san Muhammad ya daki banza,
ko shari'a za'a yi Mukhtar ne a kasa,
sannan knowing irin gatan Muhammad,
bana jin ma za'a yi shari'ar.

Hukuncin da addinin musulunci ya tanada
for rape, shine Mukhtar ya kawo kansa
har gida Muhammad ya yanke masa.

Na kara rungume Muhammad, jiki na
gabaki daya yana karkarwa. A hankali ya
fara sauke ajjiyar zuciya sannan ya dago
fuskata daga kirjinsa yana kallo na yana
shafa fuskar yace "Hey. It is okay. It is
over. He will never touch you again. He
will never touch any woman again".

Maman Maama✍🏻
[07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: ❤️‍🩹Safiyya❤️‍🩹

Episode Sixty Eight: Detached

Not Edited

Him👳🏻‍♀️

Washegari ma bacci suka yi sosai da safe,
basu tashi ba sai around 12, ita ta fara
tashi ta gudu dakin ta ta barshi, rashin jin
duminta ya saka shi tashi shima. Yau ma
kamar jiya Mama ta aiko musu da abinci
sannan Esther ma da take gidan tayi, suna
vin breakfast suka sake dawowa sama. A
wanna ranar sunyi abubuwa da dama,
most of which includes exploring their
bodies, aside that sunyi arranging and
rearranging dakin sa. Daga cewa tazo ta
taya shi shirya kayan sa a closet dinsa sai
ta tsiri rearranging bedroom din nasa ma
gabaki daya bayan sun gama da closet
din, da kyar ya samu ta bar masa gadon
sa a inda yake shima dan ya ce mata ba
zai iya kunche shi bane ba, but kujerun
sai da ta saka shi chanja musu guri daga
inda yake so zuwa inda take so duk kuwa
da cewa dakin sane kuma kujerun sa
amma haka ya juya su da kansa zuwa
ra'ayin ta, bayan ta zama satisfied with
the arrangement kuma ta matsa masa
lallai shima sai ya amince cewa kujerun
sunfi dacewa a inda ta mayar da su, da
yaki fada sai tayi fushi, dole ya fadi abinda
take so din sannan kuma ya bata hakuri
for not saying it a sanda takeso.

Shi dama ya san ya debo wa kansa rigima
with auren Safiyya but he was so looking
forward to it and he knows yana da
hanyar controlling dinta a gurin da take
bukatar control din, but for other petty
things like this, zai barta to have it her
ways. Shima kuma sai ya taya ta gyaran
tata closet din, a nan ya sha iyayi har sai
da ya gode Allah, hatta folding kayan da
ba'a dinka ba sai da ta nuna masa yadda
zaivi, ballantana wadanda suke dinkakku,
daga baya sai ya ce zai yi hanging abayas
da English wears tunda su ba folding
dinsu za'ayi ba, amma nan ma sai da ta zo
ta nuna masa yadda ake saka veil din
kowacce abaya tare da abayar a jikin
hanger dinta, haka da suka zo kan
takalma da jakankuna suma, wai kowanne
takalmi sai an nemo jakarsa an ajiye su
adjacent to each other, a shirya kayan
kwalliya ne gayyar ta watse, suka bar aikin
kuma suka koma wasa wai shine makeup
artist ita kuma client dinsa, haka ta zauna
akan kujera yayi ta shafa mata abubuwa a
fuska, wani abin ma duk da ya karanta
description dinsa amma baya gane
amfaninsa dan haka ba'a gurin da ya
kamata a saka shi ya saka shi ba, a karshe
sai gata ta fito kamar mahaukaciya sabon
kamu, ya saka ta a gaba ya ringa
kyalkyala mata dariya, wannan dariyar da
yayi ce ta saka tace wallahi sai ta rama, ya
yi kokarin gudu ta kamo shi ta dawo da
shi ta zaunar da shi shima ta tsara masa
kyalliya tas a fuskarsa sannan ta rama
dariyar da yayi mata. Haka suka zauna
suna kallon junansu suna tuntsira dariya,
a karshe dai suka gaji dan kansu suka
zauna suka goge wa kansu kwalliyar.

Da rana ma Mama ta aiko musu da abinci.
Yau ma kamar jiya, sun fita sun je duba
Daddy bayan sallar magrib kamar yadda
yayi mata alkawari, bayan sun gaishe da
Daddyn sai ta shiga ta gaishe da Mommy
tunda ta lura yan kano sun koma. Da sauri
ta shiga ta fito saboda yana jiranta, suka
tafi.

Wasa wasa sai gashi wankin hula yana
neman ya kai Muhammad dare, love din
da yake ikrarin zaiyi fighting fear amma
sai ya kasa, sai dai kuma ya fahimci cewa
fadan was no longer between love and
fear but between love and love. Tana jin
toro sosai, shi kuma yana sonta sosai,
dan haka ya kasa takura mata dan yana jin
tausayin ta sosai. She would let him kiss
her, touch her, carry her and fly away with
her in to the sky, zasu yi souring har su
tarar da cloud eleven but she wouldn't let
him do the do, da zarar ta ga ya dauki
wannan hanyar zata rikice ta zare jikinta
daga nasa jiki yana karkarwa, idanu suna
fitar da hawaye, a haka dole zai hakura,
and then she would ask him to hug her
and sleep with her wai toro take ji.

"Baby I'm scared" haka ta kan fada cikin
shagwabar ta da take kara rikita masa
tunani.

A haka kwanaki uku na farkon auren su
suka zo masa, Duk da cewa abubuwa ba
su zo masa a yadda ya tsara su ba but he
wouldn't change a thing idan da ace za'a
bashi damar chanjawar, har zuwan
Mukhtar ma ba zai chanja ba, dan zuwan
na shi ya bashi damar hadiye wani abu da
ya tsaya masa a makogwaronsa tun sanda
Safiyya ta bashi labarin abinda Mukhtar
din yayi mata,

Abinda ya fahimta da ita shine ba wai bata
son abin bane ba, ya fahimci tana so, just
that wancan memory yana sakata tana jin
toro sosai, maybe tana gain kamar
abinda ta ji a wancan karon shi zata sake
ji a wannan karon, duk kuwa da cewa a
zuciyarta ta san ba haka bane ba amma
kwakwalwarta taki karbar gaskiya, the
trauma is still with her and she panics at
the slightest thought of it. Wannan ya
kara masa jin tausayinta da kuma
lallabata. Washegari, maana ranar da suka kwana
na uku together, bayan sun yi sallar asuba
sai suka koma bacci kamar yadda suka
saba yi kullum, ya rungume ta a jikinsa ya
lullube su nan take bacci mai nauyi ya
dauke su, sun jima suna yin baccin
sannan karar wayarsa ta tashe shi, cikin
bacci ya jawo wayar and sunan da ya gani
a jikin screen din ya bata masa mood
dinsa, ya katse kiran sannan ya saka
wayar a silent, ya koma da niyyar cigaba
da baccin sa amma sai yaji baccin yaki
zuwa, reality din situation dinsa yana
lullube shi, kafin ya gama analyzing
situation din nasa yaji wayar Safiyya ta
dauki kara itama, kasancewar tana
bangaren ta sai ta riga shi dauka and cikin
bacci ba tare da ta duba sunan wanda ya
kira ta ba ta amsa ta saka a kunnen ta
tare da cewa "hello" cikin muryar bacci,
kusancin da suke da juna ya saka yaji
muryar da kuma abinda ya fito daga cikin
wayar ta ta, muryar Safina "na kira wayar
sa bai dauka ba, na san kuna tare, ki gaya
masa ko ince ki tuna masa cewa yau
kwanan ku uku tare, hakan yana nufin yau
kwana na ne tun da dai ke bazawara ce
ba budurwa ba......" ya saka hannu ya zare
wayar da ga kunnen ta sannan ya katse
kiran ya ajiye tare da rintse idonsa yana jin
zafin maganar kamar shi aka gayawa, sai
kuma ya sake juyawa wajen Safiyya,
kasancewar ta juya masa baya ne sai
hakan ya hana shi ganin fuskarta. "Piya"
ya kira sunan ta yana kokarin juyo da ita
ta fuskance shi amma sai taki, "safiyya ta"
ya fada with that deep voice of his wanda
ya kara zama deeper saboda baccin da
yayi, tare da zura hannunsa a kasan
cikinta yana kara jawo ta zuwa gare shi.
Ta raba hannunsa da jikinta sannan ta
mike da sauri, har tana vi kamar zata fadi
ta shige toilet dinsa, ya dafe kansa da
hannunsa daya tare da rufe idonsa for
some seconds sai kuma ya tashi ya sauka
daga gadon, ya duba agogo yaga some
minutes to 12, dama jiya ma sai kusan
hakan suka tashi, ya juya ya kalli toilet din,
yana jin karar ruwa amma kuma sai jikinsa
yake bashi cewa ba wanka take yi ba kuka
take yi, ya mike ya bita toilet din, duk
sanda ta shiga toilet takan rufe ne saboda
ya san takura mata yace sai sun shiga
tare, amma sai ya tarar yau a bude, ya
tura ya shiga sai ya ji shower ce a kunne a
dakin shower, ya karasa gurin ya tura
kofar, kamar yadda yayi tunani kuwa a
zaune take dirshen a kasa ta kunna
shower din tana zubowa a kanta duk
kuwa da cewa kayan baccin ta still suna
jikinta, fuskarta a boye a tsakanin
kafafuwanta, duk da baya ganin fuskar
amma ya san kuka take yi.

Yaji wani abu ya tsaya masa a kirjinsa, just
3 days ago ya zauna ya gama tsara mata
alkawarin cewa ba zai barta ta sake yin
kuka ba and she is already doing it. Ya
shiga cikin shower din shima da kayan sa
a jikinsa ya zauna a kusa da ita sannan ya
jawo ta jikinsa. "Babe" Sai dai kuma sai ya
rasa kalaman da zai yi amfani da su wajen
rarrashin, "Babe please ki daina kuka
mana" ya fada yana dago fuskarta tare da
kissing idanunta da ya lura cewa hawaye
ne yake fita daga ciki duk kuwa da cewa
ruwan da yake zubowa a kan su yana
wanke hawayen.

Ta kwace fuskarta ta mike tsaye,
forgetting cewa a jike jikinta yake, "ni ka
rabu dani, bana son jin komai, a tashi ka
tafi gurinta". Ruwan da ya jika ta ya saka
kayan baccin ta marasa nauyi suka
mammanne a jikinta suna bayyanar masa
da dukkan surar ta, abinda ya gani ya
rikirkita tunanin sa gabakidaya. Ya mike
tsaye shima tare da jawo ta ya manna ta a
jikinsa ruwan yana cigaba da sauka a
kansu, a kunnen ta ya rada mata "am
sorry Babe, I promise you, ba zaki kara
kuka akan wannan issue din ba kinji?
Please ki daina" ta fara kokarin kwatar
kanta daga gare shi da niyyar cigaba da
fushin ta, ya ki sakin ta da niyyar cigaba
da lallashi, sai dai kuma a hankali sai
lallashin ya chanja salo daga na kalamai
ya koma na gangar jiki, jin ya fara daukan
wata hanyar ta da ban ya saka ta cigaba
da ture shi "ni ka rabu da ni, ka tafi gurin
ta, kar ka kara zuwa guri na, kar ka kara yi
min magana ma, kar ka ....... " Ya jawo
fuskarta gare shi tare da hade bakin su
cikin kiss mai cike da bayyana mata halin
da zuciyar shi da gangar jikinsa suke ciki
a kanta, tun tana kokarin kwatar kanta har
ya samu nasarar zare dukkan wata laka
da take jikinta, tun tana kokarin resisting
kisses and touches din sa har ta fara
mayar masa da martani ba tare da ta sani
ba. A haka rarrashin yayi leading to
something else wanda a karshe har sai da
ya wajabtar da wanka akan su duk su
biyun duk kuwa da cewa Gidado bai kai
ga destination din sa ba yet. Amma a
ransa ya san cewa ya kusa, kadan ya rage
masa ya je din, ko a yanzu ma da ya
takura da zata barshi ya je amma baya
son ya takura din, baya son ta kuma
alakanta wannan abin da feeling of being
forced, ya fi son duk ranar da zai samu ya
kasance da kanta ta bude masa kofa
kuma ta gayyace shi.

Ya kara karfin shower din tare da fara
gabatar da wankan da ya wajaba a gare
shi, ya juya yana kallon ta, ta dunkule a
can karshe ta rufe fuskarta da hannayenta
biyu da suka sha lalle, shi ya san ko ya ce
ta taso suyi wankan tare ba zata taso ba
dan kunyar sa take ji sosai, kunyar ce ma
ta saka ta dunkulewa a guri daya kamar
ball, sai dai, through all the kunya and all
the rufe fuska yana iya hango murmushin
da yake kwance akan fuskar ta, wannan
murmushin kuma kadai ya ishe shi
payment na hard work dinsa.

Kunyar da yasan tana ji bata hana shi
tsokanar ta ba, yayi directing ruwan
shower din towards har ya fesa mata. Ta
danyi kara tare da tare ruwan da
hannayenta ta bude idonta kadan, sai
kuma ta mayar ta rufe da sauri saboda
abinda ta gani "na shiga uku. Menene
haka ne? Wai kai ba ka jin kunya? Dan
Allah ka saka kayanka ko kuma ka fita"
yayi dariya "toilet dina ne, in kin isa ki
tashi ki fita ke" amma kuma ya san ba
zata iya tashi ba. Ko me zai yi mata ba
zata iya tashi tsaye a gabansa a yadda
take ba. "Dan Allah ka bari.... Dan Allah
ka fita" ta cigaba da rokon sa a lokacin da
ya cigaba da fesa mata ruwan avoiding
her face dan kar ya hana ta numfashi,
yace "ki taso muyi wanka to" ta girgiza
kanta tana kara rintse idonta "I can't. Dan
Allah kayi hakurj" yayi dariya, wai ita ce
mai bashi hakuri, "ki kara bani hakuri to"
"Allah ya baka hakuri, Allah ya huci
zuciyar ka" "kice min Baby" "Baby na dan
Allah kayi hakuri ka fita, ba zan kara
tsokanar ka ba" yayi kwafa sannan ya
mayar da ruwan kansa ya sake wankan da
ya fara daga farko trying not to look at her
dan kar ya koma ruwa, ya san yana
bukatar concentration for abunda yake da
niyyar yi yau.

Ya gama wankansa sannan ya fita ya bar
mata toilet din, ya shirya cikin sauri dan
ya kusa makara masallacin sallar azahar,
har ya fita daga dakin bata fito daga toilet
din ba kuma ya san ta gama kunyar fitowa
kawai take ji, da ya dawo daga masallaci
ma bai same ta a dining ba kamar jiya da
shekaran jiya, wannan ya sa ya debi
abincin ya hau mata da shi har zuwa dakin
ta, ya tarar da ita tana ta kokarin daura
dankwali sai kamshi take, tana ganin sa ta
warware dankwalin ta rufe fuskarta da shi,
ya ajiye abincin tare da karasawa ya jawo
ta jikinsa, ta fara ture shi yace "ko ki bude
fuskar nan ko kuma ni kadai na san me
zanyi miki" ya rada mata a kunne.
Ta yi masa chakulkulin da ya saka ya sake
ta da sauri, ta dauki abincin da ya ajiye ta
ruga da gudu ta shige closet ta rufe kofa.
Ya jima yana kallon kofar yana murmushi
sannan ya fita.

Shi kadai ya ci abincin sa a kasa yana jin
kewarta, amma kuma bai matsa mata da
sai ta fito sunci tare ba dan yana bukatar
concentrating, ita kuma indai tana guri to
dukkan tunanin sa a kanta yake tsayawa.
And now he needs to think about
something else. Wayarsa da take haske
ya kalla, Safina ce dai, kira na kusan biyar
kenan tayi masa a yau. Wannan ma barin
sa yayi har ya katse da kansa bai dauka
ba. Ya samu ya gama cuccusa abincin da
kyar sannan ya shanye tea dinsa ya mike
ya fita. Sai da ya zauna a sabuwar
motarsa sannan ya dauko wayarsa ya tura
wa Safiyya message "hey Babe, a fita.
We will talk about it later".
Yana tura mata ya tashi motar ya fita daga
gidan zuciyar sa cike da tunane tunane.
Hanyar daya gidan nasa ya dauka inda
Safina take. Rabonsa da gidan tun ranar
da za'a kawo Safiyya, ranar asabar. Dama
tun ranar juma'a Mama ta kira shi tayi
masa fada tas akan kin gaya mata da yayi
cewa Safina bata gida tun ranar da aka
daura auren sa da Safiyya. Shi dama tun
ranar da aka daura auren bayan ya bar
gidan su very late ya koma gida mai gadi
yake gaya masa cewa ta fita daga gidan
cikin tashin hankali, mai gadin was
concerned cewa ko mutuwa aka Vi ko
wani mugun abun da ban, sai ya fahimci
cewa ta san abinda ya faru shine ta tafi
gida.

Tun daga nan kawai ya cigaba da harkokin
sa bai neme ta ba bai kuma gayawa
iyayensa ba ballantana su neme ta, amma
a ransa yana ta jira yaji an kira shi ance
Safina ko iyayen Satina sun ce ya sake ta,
amma shiru babu wannan sakon, sal
fadan Mama ne ya biyo baya tare da
sanar masa da tayi cewa ta saka an dawo
da Safina gidan ta. "ya kamata ka san
halin da kake ciki akan yarinyar nan tun
kafin ka daukar wa kanka nauyin da ba
zaka iya saukewa ba" Mama ta fada a
karshen fadan nata.
Ya san abubuwa da yawa maganar
maman take nufi, a ciki har da approval
dinta na abinda ta san cewa yana ransa
tun farkon auren na sa da Safina.
Tabbas, tun ranar dinner din bikin su,
ranar da ya fahimci dangantakar Safina da
Safiyya, a ranar ya san cewa auren sa da
Safina ba mai dore wa bane ba, ya san
cewa zaman su tare wani abu ne da duk
su biyun ba zasu ji dadin sa ba. Amma
kuma ya kasa datse igiyar auren na su ne
saboda iyayensa, saboda gudun bacin
ransu, sai ya fara neman hujjar da zai
basu dan su fahimce shi, aside her being
related to Safiyya dan a lokacin yana
ganin ba zasu dauki hakan a matsayin
huja ba. Amma bai samu ba har abinda va
faru tsakaninsa da Safina ya faru, sai
kuma ga issue din cikinta, wannan duk ya
kara hana shi rabuwa da ita.
Yanzu kuma tun sanda cikinta ya zube
tausayinta yake ji, duk da yasan ita din ba
abar tausayi ba ce ba, gani yake ta rasa
komai saboda soyayyar sa. Gani yake
kuma idan bata yafe masa akan yanayin
zaman da suke yi ba sai Allah ya kama shi
da hakkin ta. Amma kuma ya sani, the
more da ya cigaba da zama da ita the
more alhakin ta da zai dauka ya dora wa
kansa, wannan kuma shine maganar da
Mama take yi masa. Sai dai kuma yana
son rabuwar tasu ta zo da dadi yadda
maybe zata iya yafe masa ko da ba yanzu
ba, yana kuma

105 / 113