Author : Maman Mama Category : Romantic Hausa Novels
bare ta
daga cikin ledar ta. We both dress light
sannan Esther ta cika mana basket da
abinci da sauran kayan ciye ciye, ta kuma
zubawa security suma dan Daddy ya
dage tare zamu tafi da su. Muna yin sallar
asuba muka dauki hanya. Wannan tafiyar
was one of the best memories of our lives
dan mun samu nishadi, nasara da
experience sosai a cikin ta.
Tun kafin mu tafi dama Muhammad ya
kira wanda Abba ya hada mu da shi ya
gaya masa zamu taho, sai kuma ya gaya
min cewa yana da surprise for me a can.
Hakan da naji sai ya saka ni cikin
anticipation and kept me moody a farkon
tafiyar ta mu, amma Muhammad knows
his ways around me dan haka bamu jima
on the road ba na manta da komai sai shi
sai kuma abinda nake ji a zuciya ta game
da shi din.
Munyi hira, munyi dariya, munyi fada mun
kuma mori soyayya, we had to park at one
time a cikin inuwar wata katuwar bishiya
muka danyi uzuri sannan muka muka
cigaba da tafiya muna dariya akan
audacity din mu to do that on the road.
"Baby da wani yazo yayi knocking fa ya
dauka motar ce ta lalace or something?"
"Ai kuwa da sai na cire masa idanu. And
the security won't let anyone come near
us" "idan kuma barayi ne fa?" "Tun muna
ciki ake yi mana addu'a Babe, none of
that will happen insha Allah",
Da muka sake gajiya kuma sai muka sake
tsayawa a wani guri mai kyau da muka
gani muka shimfida carpet din da Esther
ta sako mana a mota muka zauna muka
huta muka ci abinci muka yi sallar. A
wannan lokacin ne muka yi mani major
discovery a rayuwar mu, muka kuma
yanke wani major decision. Mun fahimci
cewa we both have a huge fashion for
travelling, sannan muka yanke shawarar
cewa no matter how long it will take us,
zamu kai ziyara each and every one of the
195 countries of this world. A take na fara
rubuta sunayen countries din da a taba
zuwa ni kadai da kuma wadanda ya taba
zuwa shi kadai sannan da wadanda muke
so mu fara zuwa a tare. A lokacin ne ya
gaya min wani abu da ban sani ba, "I
planned our honeymoon tun sanda na
fara tunanin za'a daura mana aure. I
booked and paid everything bayan an
daura auren an kuma saka ranar biki. Idan
zaki tuna first night din mu together akwai
wasu takardu da na fito da su tare da
rings din nan" na tuna ganin takardun
amma abinda ya faru ranar ya mantar da
ni bibiyar su,
na bude ido cikin mamaki "then why are
we still here?" Ya dan sosa kan sa sannan
yace "I saw jikin Daddy, and I know you
won't want to be away from him in that
condition. Sai na fasa. I cancelled
everything. Yanzu ba gashi muna
honeymoon din mu ba anan?" Ya fada
yana nuna gurin da muke, nayi dariya
amma kuma maganar sa ta taba min
zuciya ta sosai kuma ta kara masa kima
da daraja a cikin zuciya ta. Ina matukar jin
dadin yadda yake da damuwa akan duk
abinda ya dame ni.
Wadannan delays din da kuma
kasancewar ba gudu muke yi ba ya saka
ba mu je Kura ba sai la'asar. Sai da muka
je garin sannan jiki na yayi sanyi,
Muhammad ya kira Alhaji Abubakar ya
gaya masa mun shigo gari shi kuma yayi
guiding din mu zuwa gidan sa. Gida ne
mai kyau, shima kuma babban mutum ne
mai karamci, iyalansa ma haka. Anan
muka samu tarba mai kyau, ga abinci ga
nama da fura da nono. Bama jin yunwa
amma sai da na dan ci kadan duk kuwa da
girgiza min mai da Muhammad yake yi wai
ba'a cin abinci a bakon guri, ni kuma na ci
ne dan suji dadi.
Albishir din da suka yi min shine tun kafin
mu z0 Muhammad ya bawa Alhaji
information din da ya samu daga Daddy,
shi kuma already yayi bincike kuma ya
gane wanne Alhaji Haladu ake magana
akan sa.
"Ban san mahaifiyar ki ba amma na san
yayan sa da yawa, na san shi marigayi
Malam Jamilu (yaya Malam), na san kanin
sa Dauda wanda yayi ajalinsa. Na kuma
san marigayi Alhaji Balarabe, na san da
yawa daga cikin yayansa maza. Da yawa
daga cikin su sun rasu, amma a yanzu dai
akwai mutum uku da na sani wadanda
suke raye a mazan ban sani ba ko bayan
su akwai wani. A matan kuma wadda na
sani ita ce Fatsima" na dago kai ina kallon
sa dan ban san Fatsiman da yake magana
a kanta ba, ban taba jin an ambace ta a
yan'uwan Ammie ba.
[07/01, 10:48 pm] +234 906 816 1960: "Ban san mahaifiyar ki ba amma na san
yayan sa da yawa, na san shi marigayi
Malam Jamilu (yaya Malam), na san kanin
sa Dauda wanda yayi ajalinsa. Na kuma
san marigayi Alhaji Balarabe, na san da
yawa daga cikin yayansa maza. Da yawa
daga cikin su sun rasu, amma a yanzu dai
akwai mutum uku da na sani wadanda
suke raye a mazan ban sani ba ko bayan
su akwai wani. A matan kuma wadda na
sani ita ce Fatsima" na dago kai ina kallon
sa dan ban san Fatsiman da yake magana
a kanta ba, ban taba jin an ambace ta a
yan'uwan Ammie ba.
Sai yace min "Fatima kawar yayar mai
daki na ce, Ita ce karama a cikin yayan
Alhaji Haladu kafin a haifi yayan amaryar
sa da suka rasu. Sanda na gane gidan da
Kuke nema sal na saka ita mai daki na ta
je har gida ta gaya mata labarin ki da
kuma labarin zuwan ki. Matar nan har
kuka tayi na murnar zata gan ki. Na
tabbatar kuma ke ma zaki ji dadin ganin ta
idan kuka je".
Mai dakin na sa ita ta yafa mayafin ta duk
kuwa da girman ta suka rakamu ita da yar
autar yar ta. A fadar ta cewa tayi inda
zamu je babu nisa ba sai mun shiga mota
ba, dan haka muka bar motocin mu a
kofar gidan muka bisu a baya Muhammad
yana rike da hannu na yara da sauran yan
gari suna kallon mu kamar wasu aliens
musamman saboda security din da suka
yi bake bake a bayan mu.
Dan wulakancin Muhammad wai har da
cewa idanun mutanen garin mu zai saka
mishi allergic reaction. Ai kuwa na ce sai
na rama duk sanda muka je yalleman.
Sai da na fahimci kokarin kwantar min da
hankali yake yi yana bani assurance cewa
yana tare da ni, ni kuma tunani na yana
kan wannan Fatsiman da aka ce yayar
Ammie ce, ban taba ganin wani dan uwan
Ammie ba tunda nake a duniya. Gurin da
dan nisa, dan ni kam har sal da na gaji da
taliya amma ban gaji da ganin gari ba, Na
bude ido sosal ina ta kallon titinan su da
layukan su in imagining Baba Hadiza
yadda take yawon tallan abinci, nayi
imagining Ammie da sisters din ta suna
tafiya makaranta, musamman da muka zo
muka wuce ta gaban wata primary sai
matar ta gaya mana wanna makarantar
Ammie na tayi. Jin hakan ya saka na bude
ido sosai ina kallon ta nace "kin san ta?"
Sai tayi murmushi tace "seat din mu daya
a primary one".
Daga nan sai ta fara bamu labarin abinda
zata iya tunawa na Ammie, "tana da wayo
sosai kamar ba yar fari ba. Tana da dogon
gashi. Ina tuna wa da yadda take tsananin
son kanwarta Sauda wadda suke zuwa
makaranta tare, da yadda saudan take
makale mata" sai naji hawaye yana taruwa
a ido na.
A hanya na kira Daddy na gaya masa
abinda muke ciki, dama tunda muka taho
muke waya da shi. Sai ace ya kira Alhaji
Jamil dan Hajiya Kyauta marigayiya
wanda har yanzu sun communicating da
Daddy musamman akan maintenance na
masallaci da boreholes din da aka yi wa
Baba Hadiza a garin, Ya turo mana
number din sa yace mu kira shi idan muna
bukatar wan abu.
Bayan mun wuce primary din ne muka je
gidan, Gidan kasa ne wanda dakunan ne
kawal na kasa amma an zagaye shine da
kara, muna zuwa zamu shiga sal nace da
Muhammad ya tsaya a waje amma sai ya
rike hannuna ya tsare ni da ido kamar
wanda aka cewa in na shiga ba zan fito
ba, a dole muka shiga tare. Guards din ne
suka tsaya a waje da kyar. Matar tana
zaune akan yar baranda a kofar dakin ta
tana tankaden garin tuwo, gefe kuma ga
murhu nan an hada wuta an dora tukunya,
muka shiga da sallama. Ta amsa mana
sannan ta bi yar rakiyar tamu da kallo
"Hajiya Hajara?" Sai kuma ta kalle mu,
idonta ya tsaya a kaina, ina kallon sanda
idanuwan suka bude cikin mamaki sannan
ta mike da sauri kamar zata fadi. Na saki
hannun Muhammad na karasa gare ta ina
kokarin durkusawa in gaishe ta sai ta jawo
ni jikinta hawaye suna bin idonta "safiya!
Jama'a ga Safiya! Ashe ina da rabon
ganin ki kafin in bar duniya Safiya?" Ta
sake ni tana sake kallo na, nima fuskar
tata nake bi da kallo, ba zan ce suna kama
da Ammie ba amma suna yanayi, ina
ganin Ammie a fuskar ta, ta sake mayar
da ni jikin ta ta rungume ni ma sai na
samu kaina da rungume ta ina jin hawayen
da nake rikewa tun dazu suna gangaro
min,
Ta sake ni ta fara zagaye gidan "mai gida!
Mai gida! Harisu! Saminu! Ke Hannatu! Ku
fito ga yata nan tazo! Ku fito ga diyar
Safiya ta zo".
A take mutane suka fara shigowa gidan
nata, wannan ya sa guards dina suka
shigo suma idanunsu a kaina suna
observing duk wanda zai taba ni, ina
kallon Muhammad a tsaye a gefe hannun
sa a cikin aljihunsa yana kallona.
Wadanda ta kira suka firfito daga
dakunan su suna ta kallo na kawai. Sai da
ta nutsu sannan ta gaya min samarin
yayanta ne, magidancin kuma mijinta ne,
yar budurwar da ta kira da Hannatu kuma
ita ce autarta sauran duk ta aurar da su.
Sai da ta gama murnar ta, muka gama
kukan mu ni da ita, sannan ta dauki
tabarma ta shimfida wa Muhammad ya
zauna muma duk muka zauna.
A lokacin take bamu labari "sanda Baba
ya auri Baba Hadiza nice auta a gidan,
dan haka daga ni sai safiya. A shekaru da
kadan Baba Hadiza ta girme min dan ina
da shekaru sha biyu ita kuma tana da sha
hudu sanda Baba ya aure ta. Wannan
yasa a gidan nice zan ce mun saba da ita
dan nice kusan sa'ar ta, tare muka ringa
shiriritar kuruciyar mu, kuma ina nan
gidan ta haifi dukkan yayanta guda uku,
sai bayan haifuwar Khadijah ne aka yi min
aure kafin rasuwar Baba. Dan haka ni nati
kowa sabawa da Safiya. Amma kuma ni
karama ce a cikin yan'uwa na muryata
bata da karfin da zan saka ko kuma in
hana yin wani abu a gidan mu.
Duk abinda akayi musu bana jin dadi sai
dai bani da bakin magana, iyakaci in mun
ware da yan'uwa na inyi mita shima da
zarar sun yi kaina da fada dole in yi shiru.
Mutuwar sauda da batan Safiya suna
daga cikin tashin hankalin da ba zan taba
mantawa da shi a rayuwata ba. Tun daga
nan kuma na fara kukan yin shiru da nake
yi. Na fara neman yadda zanyi in samu
Safiya. Amma ni bani da hali. Mijina bashi
da karfi. Lokacin da labari yazo min cewa
safiya tazo garin nan har taje gidan mu
ranar ko takalmi babu haka naje har gida
amma na tarar ta tafi. Aka ce tayi kudi. A
kace dan yankan kai ta aura. A ka zo aka
ce ita ce mai yankan kan ma. Babu irin
sharrin da ba'a yi mata ba amma babu
yadda zanyi akai. Sanda aka nemo inda
take naso a tafi da ni amma aka ki aka ce
zan bata shiri ne. Daga nan ba na ma
sanin sanda suke zuwa. Sai labarin
mutuwar safiya naji. Nayi kuka sosai,
wannan ya sa aka tafi da ni a lokacin
amma abinda yan uwa na suka yi a gidan
gaisuwar ya sa nayi nadamar zuwa. Na
ganki a lokacin kina karama, kina ta kuka,
amma wadanda suke rike da ke ba zasu
bani ke in rike ba dan basu yarda da mu
ba kuma ban ga laifin su ba. Tun daga nan
duk zuwan da suke yi ban sake komawa
ba dan ina gudun abin kunyar da suke
zuwa yi a can. A karshe dai suka samo
kudin da yayi ajalin biyu daga cikin mu, da
babban yayan mu da kuma autan gidan a
maza, Dauda, wanda shi nake bi. Tun
daga nan sauran yan'uwa suka ce dukiyar
dama ta mutuwa ce, babu wanda ya kara
bi ta kan neman ki ni kuma ban san komai
a kan ki ba ba kuma zan iya mayar da
kaina zuwa gidan ku ba. Na sani a raina
kina raye, na kuma saka raina cewa
watarana zaki zo har nan gidan ki same ni.
Gashi kuma yau Allah ya cika min burina"
Sai da ta gama jawabin sannan tace "ya
sunan kip?" "Safiyya" na amsa murya ta
can kasa "suna na Safiyya".
And that was how I found an Aunt.
Muna gurin ta akayi sallar magrib, ta tuka
mana tuwo ta zubo mana, ina kallon
Muhammad ya dauki cokali yayi loma
daya daga ita kuma bai kara ba. Sai daga
baya na samu yin magana da Muhammad
*kwana ya kama mu, Allah ya sa na taho
mana da kaya" ya gyada kai yana kallon
surrounding din "anan zaki kwana?" Na
daga kai "yes" yayl ajjiyar zuciya, nace
*kai kuma better ka koma gidan Alhaji
Abubakar, na ga masaukin da yayi mana
is decent, zaka iya kwana a can" ya sake
kallon gidan fatsima yace "zaki iya kwana
anan?" Nayi murmushi "zata ji dadi" ya
dan kalli cikin gidan, "just be careful. Your
security will be here with you. Kina da
charge a wayarki?" Nace "eh" na rike
hannunsa "I will miss you, Baby" ina jin
kewarsa a raina tun kafin ya bar kusa da
ni, yayi murmushi "ba yanzu zan bar ki ba
ai. Let's go explore the town muga yadda
yake da daddare".
And it was a good idea, da farko we tried
to mingle with the town people amma
securityn mu suka hana mu sakewa, daga
baya sai muka yi musu wayo muka dawo
ta gidan fatsima muka tambayi Hannatu
ko akwai inda zamu iya fita banda inda
muka shigo? ta nuna mana wata kofa ta
baya da aka rufe da kara muka bi muka
gudu muka barsu suna gadin bakin kofa.
Yawo muka yi sosai hand in hand, muka
zauna a dandali muka sayi awara muka ci,
ko ince naci, dan Muhammad daga guda
daya sai yaki karawa nima da na cinye
guda biyar sai ya hanani karawa ya bayar
da sauran sannan muka sayi rake da
gyada, Muhammad ya zuba mana gyadar
a aljihunsa, muna tafiya a titi muna shan
raken mu muna hira har muka shanve
sannan muka fara in gyadar.
Munyi yawo har sai da kafafuwan mu suka
gaji, babu haske sosai dan haka babu
wanda yake gane mu baki ne. A lokacin
ne muka zo masallacin Baba Hadiza, ina
ganin sa na gane shi dan ina ganin
hotunan shi a wajen Daddy. Sai naga yafi
min girma a ido akan a hotunan. Na tsaya
ina kallon sa, Muhammad ma sai ya gane
shine dan haka ya tsaya. "it is big and
beautiful" ya fada, nima na gyada kai cikin
amincewa "yes it is", sai na cigaba da
kallon masallacin ina mamakin wai da
gaske nan shine asalin gidan kakanni na,
anan aka haifi Ammie, Muhammad kalle ni
'"muyi sallah anan. Dama bamuyi isha ba".
Muka je muka yi alwala a pumps din da
suke a jere a gefe, na lura ana kula da
masallacin sosai dan komai a gyare yake,
na shiga bangaren mata shi kuma ya
shiga na maza mukayi sallah. Na samu
kaina da yin dogayen adduoin ga kakanni
na da iyalin su har da su inna gaje da inna
saade.
Sai da na gama sannan na fito na tarar
Muhammad yana jirana a waje, na lura
mai gadin masallacin jajirtacce ne dan
babu wanda yake bari ya shigo in dai har
ba ibada zaka yi ba dan Muhammad ma
da zai jira ni hana shi tsayawa yayi a
harabar sai da ya fita waje sannan ya jira,
naji kuma voices din yara suna ta karatun
Alkur'ani, sai naji dadi sosai, a raina nayi
niyyar inganta makarantar tare da yiwa
mai gain abun alkhairi.
Ina fitowa Muhammad ya kama hannuna
muka cigaba da tafiya, sai kuma muka
fahimci mun bata dan bamu san hanyar
da zamu bi mu koma gidan fatsima ko
gidan Alhaji Abubakar ba, a lokacin ne
kuma muka lura da security mu suna bin
mu a baya amma sun dan bada distance a
tsakanin mu, Muhammad ne ya gansu ya
nuna min su, na juya na kalle su sai chief
securityn ya daga min hannu, dariya muka
yi, bamu san ya akayi suka nemo mu ba
kuma bamu san tun yaushe suke bin mu
ba.
Wani mutum muka samu muka tambaya,
da kyar ya gane Alhaji Abubakar din da
muke magana akai tunda mu bamu san
wata inkiya ta shi ba ko kuma sunan wani
dan sa, sai yace "ko kune bakin da kuka
2o gidan da zu?" Sai muka yi mamaki
amma Muhammad ya amsa masa da eh
sal yayi mana kwatance. Gidan muka
koma muka dauki motar mu sannan
Muhammad ya mayar da ni gidan fatsima
da already hankalin ta ya fara tashi tana
neman mu. A mota muka yi sallama,
kamar ba zai barni in shiga ba. Yace "take
care" yafi a kirga.
Ina shiga cikin gidan kuwa waya ta tayi
kara naga sunansa sai na saka bluetooth
a kunne na dan na san wayar ba me
karewa ba ce ba.
Ranar mun kusa kwana hira da fatsima da
iyalinta, ni sai naji ina jin nauyin ce mata
fatsima duk kuwa da cewa yayanta ma
haka suke ce mata, sai na fara ce mata
Aunty, suka yi ta min dariya amma naki
dainawa har dai ta fara amsawa. Tayi min
hirarrakin Ammie sosai. Ta kuma bani
labarikan family din mu da abubuwan da
suka faru, tace su uku suka rage a mata,
maza ma su uku ne. Sai jikoki wadanda
suma duk sun girma sun manyanta tunda
dama wadansu jikokin sun girmi Ammie
ma ballantana ni. Itama da take karama
yayanta gabaki daya Hannatu kadai na
girma, Nima na basu Labarin abubuwan
da nake ganin ya kamata su sani kamar
matsayin Muhammad a gurina, amma ban
bude cikina nayi magana sosai ba kamar
yadda Daddy ya gargade ni, duk da dai
banga alamar cutarwa a tare da su ba but
time will tell.
Ta saka aka dauki katifar ta ta kan gado
aka yi min shimfida anan tsakar gida
saboda basu da wuta a gidan, ala daura
min net, na shiga na kwanta ina jin dadin
iskar da take kada ni. Amma kuma dai
baccin banyi wani mai nisa ba saboda
kukan kwari da kuma yanayin chanjin
bakon guri ga kuma sararin samaniya
tarwai a kaina, Duk da haka da safe na
tashi fresh saboda fresh air din da na sha.
A niyyar mu da wuri zamu wuce
kwatarkwashi amma taki yarda, sai da tayi
ta yawo dani gidajen yan'uwa, duk sauran
yan'uwan su sai da ta kaini wajen su, naga
murna a idon wadansu, na ga mamaki a
na wasu, sannan naga mixed feelings a
gurin wadansu, sai dai ban damu ba, bana
nufin kowa da sharri kuma ina addu'ar
kariya daga sharrin kowa. Muhammad ya
bude bakin aljihu da kudin da ban san ma
ya taho da su ba ya ringa raba musu. Ai
kam da yawa ya saye su da wanna kudin.
Da kyar muka samu muka kwace bayan
azahar muka bar garin bayan ta saka nayi
mata alkawari tare da rantsuwa cewa zan
dawo. Ni dariya ma na ringa yi. Tace ta
zata sati daya zanyi. Na tabbatar mata
zuwa nayi kawai gain guri amma tunda
na gansu har sai sun gaji da ni.
Daga nan Alhaji Abubakar ya hada mu da
wani yaron sa muka tafi kwatarkwashi.....
Bani da hope din ganin kowa nawa a can
duk kuwa da cewa Alhaji Abubakar ya
gaya min yana da another surprise for me,
amma abinda na tarar yafi